< Joshua 11 >

1 And whe Iabin King of Hazor had heard this, then he sent to Iobab King of Madon, and to the king of Shimron, and to the king of Achshaph,
Sa’ad da Yabin sarkin Hazor ya ji wannan, sai ya aika saƙo zuwa wurin Yobab sarkin Madon, da sarkin Shimron, da Akshaf,
2 And vnto the Kings that were by ye North in the mountaines and plaines toward the Southside of Cinneroth, and in the valleys, and in the borders of Dor Westward,
ya kuma aika zuwa ga sarakunan arewa waɗanda suke kan tuddai da kuma waɗanda suke cikin Araba a kudancin Kinneret da cikin filayen kwari, da cikin Nafot Dor a yamma;
3 And vnto the Canaanites, both by East, and by West, and vnto the Amorites, and Hittites, and Perizzites, and Iebusites in the mountaines, and vnto the Hiuites vnder Hermon in the land of Mizpeh.
ya kuma aika zuwa ga Kan’aniyawa a gabas da yamma; da kuma zuwa ga Amoriyawa, Hittiyawa da Ferizziyawa, da Yebusiyawa da suke kan tuddai; da kuma Hiwiyawa masu zama a gindin dutsen Hermon a yankin Mizfa.
4 And they came out and all their hostes with them, many people as the sande that is on the sea shore for multitude, with horses and charets exceeding many.
Suka fito da dukan rundunansu da keken yaƙi masu yawan gaske, babbar runduna, yawansu ya yi kamar yashin bakin teku.
5 So all these Kings met together, and came and pitched together at the waters of Merom, for to fight against Israel.
Duk sarakunan nan suka haɗa mayaƙansu tare, suka kafa sansani a bakin Ruwayen Meron don su yi yaƙi da Isra’ilawa.
6 Then the Lord sayd vnto Ioshua, Be not afrayd for them: for to morowe about this time will I deliuer them all slaine before Israel: thou shalt hough their horses, and burne their charets with fire.
Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoronsu, domin war haka gobe zan ba da dukansu a hannun Isra’ilawa, za su kuwa karkashe su. Za ku gurgunta dawakansu, ku kuma ƙone keken yaƙinsu.”
7 Then came Ioshua and al the men of warre with him against them by the waters of Merom suddenly, and fell vpon them.
Sai Yoshuwa da dukan mayaƙan suka auka musu a bakin Ruwayen Meron.
8 And the Lord gaue them into the hand of Israel: and they smote them, and chased them vnto great Zidon, and vnto Misrephothmaim, and vnto the valley of Mizpeh Eastward, and smote them vntill they had none remaining of them.
Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa nasara a kan su, suka ci su da yaƙi, suka fafare su har zuwa Sidon Babba, zuwa Misrefot Mayim, har zuwa Kwarin Mizfa a gabas, ba wanda suka bari da rai.
9 And Ioshua did vnto them as the Lord bade him: he houghed their horses, and burnt their charets with fire.
Yoshuwa ya yi musu yadda Ubangiji ya umarta, ya gurgunta dawakansu, ya kuma ƙone keken yaƙinsu.
10 At that time also Ioshua turned backe, and tooke Hazor, and smote the King thereof with the sword: for Hazor before time was the head of all those kingdomes.
A lokacin nan Yoshuwa ya koma da baya ya ci Hazor da yaƙi, ya kuma kashe sarkinta da takobi. (Hazor ce babbar masarautan ƙasashen nan.)
11 Moreouer, they smote all the persons that were therein with the edge of the sworde, vtterly destroying all, leauing none aliue, and hee burnt Hazor with fire.
Suka karkashe duk mazaunan ƙasar da takobi, ba su bar wani mai numfashi ba, suka kuma ƙona Hazor.
12 So all ye cities of those Kings, and all the kings of them did Ioshua take, and smote them with the edge of the sword, and vtterly destroyed them, as Moses the seruant of the Lord had commanded.
Yoshuwa ya ƙwace masarautun nan duka ya kuma kashe sarakunansu da takobi, ya hallakar da su ƙaƙaf kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarta.
13 But Israel burnt none of the cities that stoode still in their strength, saue Hazor onely, that Ioshua burnt.
Duk da haka Isra’ilawa ba su ƙone biranen da suke kan tuddai ba, sai Hazor kaɗai Yoshuwa ya ƙone.
14 And all the spoyle of these cities and the cattel the children of Israel tooke for their praye, but they smote euery man with the edge of the sword vntill they had destroyed them, not leauing one aliue.
Isra’ilawa suka kwashi ganima da dabbobi na waɗannan birane, amma suka karkashe mutanen duka da takobi, ba su bar wani mai numfashi ba.
15 As the Lord had commanded Moses his seruant, so did Moses commande Ioshua, and so did Ioshua: he left nothing vndone of all that the Lord had commanded Moses.
Yadda Ubangiji ya umarci bawansa Musa, haka Musa ya umarci Yoshuwa, shi kuwa ya yi duk abin da Ubangiji ya umarci Musa.
16 So Ioshua tooke all this land of the mountaines, and all the South, and all the lande of Goshen, and the lowe countrey, and the plaine, and the mountaine of Israel, and the lowe countrey of the same,
Saboda haka Yoshuwa ya cinye ƙasar duka da yaƙi, dukan Negeb, duka yankin Goshen, filayen kwari na yamma, Araba da tuddai na Isra’ila da kwarinta.
17 From the mount Halak, that goeth vp to Seir, euen vnto Baal-gad in the valley of Lebanon, vnder mount Hermon: and all their Kings he tooke, and smote them, and slewe them.
Daga Dutsen Halak wanda ya miƙe zuwa wajajen Seyir, zuwa Ba’al-Gad a Kwarin Lebanon ƙasa da Dutsen Hermon. Ya kama sarakunansu ya karkashe su.
18 Ioshua made warre long time with all those Kings,
Yoshuwa ya daɗe yana yaƙi da dukan waɗannan sarakuna.
19 Neither was there any citie that made peace with the children of Israel, saue those Hiuites that inhabited Gibeon: all other they tooke by battell.
Sai Hiwiyawa kaɗai waɗanda suke zama a Gibeyon, sauran ba ko birni ɗaya da ta yi yarjejjeniya ta salama da Isra’ilawa, Isra’ilawa kuwa suka ci dukansu da yaƙi.
20 For it came of the Lord, to harden their heartes that they shoulde come against Israel in battell to the intent that they shoulde destroye them vtterly, and shewe them no mercie, but that they shoulde bring them to nought: as the Lord had commanded Moses.
Gama Ubangiji ne ya taurare zukatansu waɗannan sarakuna suka yi yaƙi da Isra’ilawa don yă hallaka su gaba ɗaya, yă gamar da su ba jinƙai, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
21 And that same season came Ioshua, and destroyed the Anakims out of the mountaines: as out of Hebron, out of Debir, out of Anab, and out of all the mountaines of Iudah, and out of all the mountaines of Israel: Ioshua destroyed them vtterly with their cities.
A lokacin nan Yoshuwa ya je ya hallaka Anakawa daga ƙasar tudu. Daga Hebron, Debir da Anab. Daga dukan ƙasar tuddai na Yahuda, da kuma dukan ƙasar tudu ta Isra’ila, Yoshuwa ya hallaka su duka da garuruwansu.
22 There was no Anakim left in the lande of the children of Israel: onely in Azzah, in Gath, and in Ashdod were they left.
Ba a bar waɗansu Anakawa a harabar Isra’ila ba; sai dai a Gaza, Gat da Ashdod ne aka samu waɗanda suka ragu da rai.
23 So Ioshua tooke the whole land, according to all that the Lord had saide vnto Moses: and Ioshua gaue it for an inheritance vnto Israel according to their portion through their tribes: then the land was at rest without warre.
Yoshuwa kuwa ya ƙwace dukan ƙasar yadda Ubangiji ya umarci Musa, ya ba da ita ta zama ƙasar gādo ga Isra’ilawa, kabila-kabila. Ta haka ƙasar ta huta daga yaƙi.

< Joshua 11 >