< John 20 >

1 Nowe the first day of the weeke came Marie Magdalene, early when it was yet darke, vnto the sepulchre, and sawe the stone taken away from the tombe.
To da sassafe ranar farko ta mako, da sauran duhu, Maryamu Magadaliya ta zo kabarin, ta tarar an kawar da dutsen daga kabarin.
2 Then she ranne, and came to Simon Peter, and to the other disciple whom Iesus loued, and saide vnto them, They haue taken away the Lord out of the sepulchre, and we knowe not where they haue laid him.
Sai ta ruga da gudu zuwa wurin Saminu Bitrus tare da almajirin nan da Yesu ke kauna, tace masu, “Sun dauke Ubangiji daga kabarin, bamu kuwa san inda aka sa shi ba.”
3 Peter therefore went forth, and the other disciple, and they came vnto the sepulchre.
Sai Bitrus tare da almajirin nan suka fita, kuma suka tafi kabarin,
4 So they ranne both together, but the other disciple did outrunne Peter, and came first to the sepulchre.
dukansu suka ruga da gudu tare, amma daya almajirin ya riga Bitrus isowa kabarin,
5 And he stouped downe, and sawe the linnen clothes lying: yet went he not in.
Sai ya sunkuya ya leka ciki, ya ga likkafanin lillin a wurin, amma fa bai shiga ciki ba.
6 Then came Simon Peter following him, and went into the sepulchre, and sawe the linnen clothes lye,
Sai Saminu Bitrus ya iso daga bayansa sai ya shiga kabarin, ya tarar da likkafanin lillin a ajiye.
7 And the kerchiefe that was vpon his head, not lying with the linnen clothes, but wrapped together in a place by it selfe.
sai fallen kuma da yake kansa. Ba'a ajiye tare da likkafanin ba amma aka linkeshi aka ajiye shi daban.
8 Then went in also the other disciple, which came first to the sepulchre, and he sawe it, and beleeued.
Sai almajirin nan da ya riga isa kabarin shi ma ya shiga ya gani, sai ya ba da gaskiya.
9 For as yet they knewe not the Scripture, That he must rise againe from the dead.
Har ya zuwa wannan lokacin basu san nassin daya ce zai tashi daga matattu ba.
10 And the disciples went away againe vnto their owne home.
Sai almajiran suka sake komawa gida kuma.
11 But Marie stoode without at the sepulchre weeping: and as she wept, she bowed her selfe into the sepulchre,
Amma Maryamu tana tsaye a bakin kabarin tana kuka. Yayin da take kuka, sai ta sunkuya ta leka cikin kabarin.
12 And sawe two Angels in white, sitting, the one at the head, and the other at the feete, where the body of Iesus had laien.
Sai ta ga mala'iku guda biyu cikin fararen kaya zaune, daya ta wurin kai daya kuma ta wurin kafafu inda aka kwantar da Yesu.
13 And they said vnto her, Woman, why weepest thou? She said vnto them, They haue taken away my Lord, and I know not where they haue laide him.
Sukace mata, “Uwargida don me kike kuka? Sai tace masu, “Domin sun dauke Ubangijina, ban kuwa san inda suka ajiye shi ba.
14 When she had thus said, she turned her selfe backe, and sawe Iesus standing, and knewe not that it was Iesus.
Bayan ta fadi haka, ta juya sai ta ga Yesu tsaye a wurin. Amma bata san cewa Yesu bane,
15 Iesus saith vnto her, Woman, why weepest thou? whom seekest thou? She supposing that he had bene the gardener, said vnto him, Sir, if thou hast borne him hence, tell me where thou hast laid him, and I will take him away.
Yesu yace mata, “Uwargida, me yasa kike kuka? Wa kuma kike nema? Domin tana zaton shine mai kula da lambun, sai tace masa, “Maigida in kaine ka dauke shi, gaya mani inda ka sa shi, ni kuwa in dauke shi.”
16 Iesus saith vnto her, Marie. She turned her selfe, and said vnto him, Rabboni, which is to say, Master.
Yesu yace mata, “Maryamu”. Sai ta juya, tace masa da Armaniyanci “Rabboni!” wato mallam.
17 Iesus saith vnto her, Touch me not: for I am not yet ascended to my Father: but goe to my brethren, and say vnto them, I ascend vnto my Father, and to your Father, and to my God, and your God.
Yesu yace mata, kada ki taba ni, domin har yanzu ban hau wurin Uba ba tukuna, amma kije wurin 'yan'uwana kice masu, zan je wurin Ubana da Ubanku, Allahna da kuma Allahnku”.
18 Marie Magdalene came and told the disciples that she had seene the Lord, and that he had spoken these things vnto her.
Maryamu Magadaliya ta je tace wa almajiran, “Na ga Ubangiji” Ta kuma ce ya fada mata wadannan abubuwa.
19 The same day then at night, which was the first day of the weeke, and when the doores were shut where the disciples were assembled for feare of the Iewes, came Iesus and stoode in the middes, and saide to them, Peace be vnto you.
Da yamma a wannan rana, a rana ta farko ta mako, almajiran suna kulle a daki saboda tsoron Yahudawa, Yesu yazo ya tsaya a tsakaninsu, yace “Salama Agareku”.
20 And when he had so saide, he shewed vnto them his handes, and his side. Then were the disciples glad when they had seene the Lord.
Bayan ya fadi haka, sai ya nuna masu hannuwansa da kuibinsa. Da almajiran suka ga Ubangiji, sai suka yi farin ciki.
21 Then saide Iesus to them againe, Peace be vnto you: as my Father sent me, so sende I you.
Yesu ya sake ce masu, “salama agareku. “Kamar yadda Uba ya aiko ni, haka Ni ma na aike ku”.
22 And when he had saide that, he breathed on them, and saide vnto them, Receiue the holy Ghost.
Da Yesu ya fadi haka, sai ya hura masu lumfashinsa, yace masu, “Ku karbi Ruhu Mai Tsarki.
23 Whosoeuers sinnes ye remit, they are remitted vnto them: and whosoeuers sinnes ye reteine, they are reteined.
Duk wanda kuka gafarta wa zunubai, an gafarta masa; kowa kuka rike zunubansa, an rikesu.”
24 But Thomas one of the twelue, called Didymus, was not with them when Iesus came.
Toma, daya daga cikin sha biyun, wanda ake kira Dan Tagwai, baya tare dasu lokacin da Yesu ya bayyana.
25 The other disciples therefore saide vnto him, We haue seene the Lord: but he said vnto them, Except I see in his handes the print of the nailes, and put my finger into the print of the nailes, and put mine hand into his side, I will not beleeue it.
Sauran almajiran sukace masa “Mun ga Ubangiji”. Sai yace masu, “In ban ga gurbin kusoshi a hannuwansa ba, in sa yatsana a gurbin kusoshin ba, in kuma sa hannuna cikin kuibinsa ba, ba zan bada gaskiya ba.
26 And eight dayes after, againe his disciples were within, and Thomas with them. Then came Iesus, when the doores were shut, and stood in the middes, and said, Peace be vnto you.
Bayan kwana takwas har wa yau almajiran na cikin gida, Toma ma na tare dasu, kofofin suna kulle, sai ga Yesu a tsakaninsu yace, “Salama agareku”.
27 After saide he to Thomas, Put thy finger here, and see mine hands, and put forth thine hand, and put it into my side, and be not faithlesse, but faithfull.
Sa'an nan yace wa Toma, “Iso nan da yatsanka, dubi hannuwana. Miko hannunka kuma kasa a kuibina, kada ka zama marar bada gaskiya, sai dai, mai bada gaskiya”.
28 Then Thomas answered, and said vnto him, Thou art my Lord, and my God.
Toma ya amsa yace “Ya Ubangijina da Allahna!”
29 Iesus said vnto him, Thomas, because thou hast seene me, thou beleeuest: blessed are they that haue not seene, and haue beleeued.
Yesu yace masa, “Wato saboda ka gan ni, ka bada gaskiya? Albarka ta tabbata ga wadanda basu gani ba, amma kuwa sun bada gaskiya.
30 And many other signes also did Iesus in the presence of his disciples, which are not written in this booke.
Yesu yayi wadansu alamu da yawa dabam dabam a gaban almajiransa, wadanda ba'a rubuta a littafin nan ba.
31 But these things are written, that ye might beleeue, that Iesus is that Christ that Sonne of God, and that in beleeuing ye might haue life through his Name.
Amma an rubuta wadannan ne, domin ku bada gaskiya Yesu shine Almasihu, Dan Allah, ta wurin gaskatawa kuma ku sami rai cikin sunansa.

< John 20 >