< Joel 2 >

1 Blowe the trumpet in Zion, and shoute in mine holy mountaine: let all the inhabitants of the lande tremble: for the day of the Lord is come: for it is at hand.
Ku busa ƙaho a cikin Sihiyona; ku yi karar amo a tsaunina mai tsarki. Bari dukan mazaunan ƙasar su yi rawan jiki, gama ranar Ubangiji tana zuwa. Tana gab da faruwa
2 A day of darkenesse, and of blacknesse, a day of cloudes, and obscuritie, as the morning spred vpon the mountaines, so is there a great people, and a mighty: there was none like it from the beginning, neither shalbe any more after it, vnto the yeeres of many generations.
rana ce ta baƙin duhu ƙirin, ranar gizagizai ce baƙi ƙirin. Babbar rundunar mayaƙa mai ƙarfi tana zuwa kamar ketowar alfijir a kan duwatsu yadda ba a taɓa ganin irinta ba, ba kuwa za a ƙara ganin irinta ba har tsararraki masu zuwa.
3 A fire deuoureth before him, and behinde him a flame burneth vp: the land is as the garden of Eden before him, and behinde him a desolate wildernesse, so that nothing shall escape him.
A gabansu wuta tana ci, a bayansu ga harshen wuta yana ci, A gabansu ƙasa ta yi kamar gonar Eden, a bayansu kuma jeji ne wofi, babu abin da ya kuɓuce musu.
4 The beholding of him is like the sight of horses, and like the horsemen, so shall they runne.
Suna da kamannin dawakai; suna gudu kamar dokin yaƙi.
5 Like the noyse of charrets in the toppes of the mountaines shall they leape, like the noyse of a flame of fire that deuoureth the stubble, and as a mightie people prepared to the battel.
Da motsi kamar na kekunan yaƙi sun tsallake ƙwanƙolin duwatsu, kamar ƙarar harshen wuta mai cin tattaka, kamar runduna mai ƙarfi wadda ta ja dāgār yaƙi.
6 Before his face shall the people tremble: all faces shall gather blackenesse.
Da ganinsu, al’ummai sun kamu da azaba; kowace fuska ta yanƙwane.
7 They shall runne like strong men, and goe vp to the wall like men of warre, and euery man shall goe forward in his wayes, and they shall not stay in their paths.
Sukan auka kamar jarumawa; sukan hau katanga kamar sojoji. Kowa yana takawa bisa ga tsari, ba mai kaucewa.
8 Neither shall one thrust another, but euery one shall walke in his path: and when they fall vpon the sword, they shall not be wounded.
Ba sa turin juna, kowane yakan miƙe gaba. Sukan kutsa cikin abokan gāba ba mai tsai da su.
9 They shall runne to and from in the citie: they shall runne vpon the wall: they shall clime vp vpon the houses, and enter in at ye windowes like ye thiefe.
Sukan ruga cikin birni, suna gudu a kan katanga. Sukan hau gidaje, sukan shiga ta tagogi kamar ɓarayi.
10 The earth shall tremble before him, ye heauens shall shake, the sunne and the moone shalbe darke, and the starres shall withdraw their shining,
A gabansu duniya takan girgiza, sararin sama kuma yakan jijjigu, rana da wata su yi duhu, taurari kuma ba sa ba da haske.
11 And the Lord shall vtter his voyce before his hoste: for his hoste is very great: for he is strog that doeth his word: for the day of the Lord is great and very terrible, and who can abide it?
Ubangiji ya yi tsawa wa shugaban mayaƙansa; sojojinsa sun fi a ƙirge masu ƙarfi ne kuma su waɗanda suke biyayya da umarninsa. Ranar Ubangiji da girma take; mai banrazana. Wa zai iya jure mata?
12 Therefore also now the Lord sayth, Turne you vnto me with all your heart, and with fasting, and with weeping, and with mourning,
“Ko yanzu”, in ji Ubangiji, “Ku juyo gare ni da dukan zuciyarku, da azumi da kuka da makoki.”
13 And rent your heart, and not your clothes: and turne vnto the Lord your God, for he is gratious, and mercifull, slowe to anger, and of great kindnes, and repenteth him of the euill.
Ku kyakkece zuciyarku ba rigunanku ba. Ku juyo ga Ubangiji Allahnku, gama shi mai alheri ne mai tausayi kuma mai jinkirin fushi da yawan ƙauna, yakan kuma janye daga aika da bala’i.
14 Who knoweth, is he wil returne and repent and leaue a blessing behinde him, euen a meate offring, and a drinke offring vnto ye Lord your God?
Wa ya sani? Ko zai juya yă kuma ji tausayi yă sa mana albarka ta wurin hadaya ta gari da hadaya ta sha wa Ubangiji Allahnku.
15 Blowe the trumpet in Zion, sanctifie a fast, call a solemne assembly.
A busa ƙaho a Sihiyona, a yi shelar azumi mai tsarki, a kira tsarkakan taro.
16 Gather the people: sanctifie the congregation, gather the elders: assemble the children, and those that sucke the breastes: let the bridegrome go forth of his chamber, and the bride out of her bride chamber.
A tattara mutane; ku tsarkake taron; ku kawo dattawa wuri ɗaya; ku kuma tara yara, da waɗanda suke shan mama. Bari ango yă bar ɗakinsa amarya kuma lolokinta.
17 Let the Priestes, the ministers of the Lord weepe betweene the porch and the altar, and let them say, Spare thy people, O Lord, and giue not thine heritage into reproche that the heathen should rule ouer them. Wherefore should they say among the people, Where is their God?
Bari firistocin da suke yin hidima a gaban Ubangiji, su yi kuka tsakanin filin haikali da bagade. Bari su ce, “Ka cece mutanenka, ya Ubangiji. Kada ka bar gādonka yă zama abin dariya, da abin ba’a a cikin al’ummai. Me zai sa a ce a cikin mutane, ‘Ina Allahnsu yake?’”
18 Then will the Lord be ielous ouer his land, and spare his people.
Ta haka Ubangiji zai yi kishin ƙasarsa yă kuma ji tausayin mutanensa.
19 Yea, the Lord wil answere and say vnto his people, Beholde, I will send you corne, and wine, and oyle, and you shalbe satisfied therewith: and I will no more make you a reproche among the heathen,
Ubangiji zai amsa musu ya ce, “Ina aika da hatsi, sabon ruwan inabi, da mai, isashe da zai ƙosar da ku sosai; ba kuma zan ƙara maishe ku abin dariya ga al’ummai ba.
20 But I will remooue farre off from you the Northren armie, and I will driue him into a land, barren and desolate with his face toward the East sea, and his end to the vtmost sea, and his stinke shall come vp, and his corruption shall ascend, because he hath exalted himselfe to do this.
“Zan kori sojojin arewa nesa da ku, in tura su cikin busasshiyar ƙasa marar amfani kuma, kuma da sawunsu na gaba zan tura su zuwa gabashin teku da kuma sawunsu na baya tura su zuwa yammanci a Bahar Rum. Warinsu kuma zai bazu; ɗoyinsu zai tashi.” Tabbatacce ya yi al’amura masu girma.
21 Feare not, O land, but be glad, and reioyce: for the Lord wil do great things.
Kada ki ji tsoro, ya ƙasa; ki yi murna ki kuma yi farin ciki. Tabbatacce Ubangiji ya yi abubuwa masu girma.
22 Be not afrayde, ye beastes of the fielde: for the pastures of the wildernesse are greene: for the tree beareth her fruite: the figge tree and the vine do giue their force.
Kada ku ji tsoro, ya ku namun jeji, gama wuraren kiwo sun yi kore shar. Itatuwa suna ba da’ya’yansu; itacen ɓaure da na inabi suna ba da amfaninsu.
23 Be glad then, ye children of Zion, and reioyce in the Lord your God: for he hath giuen you the rayne of righteousnes, he wil cause to come downe for you the rayne, euen the first raine, and the latter raine in the first moneth.
Ku yi murna, ya ku mutanen Sihiyona, ku yi farin ciki cikin Ubangiji Allahnku, gama ya ba ku ruwan bazara cikin adalci. Yakan aika muku yayyafi a yalwace, na bazara da na kaka, kamar dā.
24 And the barnes shalbe full of wheate, and the presses shall abound with wine and oyle.
Masussukai za su cika da hatsi; randuna za su cika da sabon ruwan inabi da mai suna zuba.
25 And I will render you the yeeres that the grashopper hath eaten, the canker worme and the caterpiller and the palmer worme, my great hoste which I sent among you.
“Zan mayar muku da abin da fāra suka ci a waɗannan shekaru waɗanda ɗango da fāra masu gaigayewa, da kuma sauran fāra da tarin fāra babban mayaƙan da na aika don su fāɗa muku.
26 So you shall eate and be satisfied and praise the Name of the Lord your God, that hath dealt marueilously with you: and my people shall neuer be ashamed.
Za ku sami a wadace ku ci, har sai kun ƙoshi, za ku kuma yabi sunan Ubangiji Allahnku, wanda ya yi muku ayyukan banmamaki; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
27 Ye shall also know, that I am in the middes of Israel, and that I am the Lord your God and none other, and my people shall neuer be ashamed.
Sa’an nan za ku sani ina cikin Isra’ila, cewa ni ne Ubangiji Allahnku, babu wani kuma; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
28 And afterward will I powre out my Spirit vpon all flesh: and your sonnes and your daughters shall prophecie: your olde men shall dreame dreames, and your yong men shall see visions,
“Daga baya kuma, zan zuba Ruhuna a bisan dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, tsofaffinku za su yi mafarkai, matasanku za su ga wahayoyi.
29 And also vpon the seruants, and vpon the maydes in those dayes wil I powre my Spirit.
Har ma a bisan bayina, maza da mata, zan zuba Ruhuna a kwanakin nan.
30 And I will shewe wonders in the heauens and in the earth: blood and fire, and pillars of smoke.
Zan nuna abubuwan banmamaki a cikin sammai da kuma a kan duniya, za a ga jini da wuta da murtukewar hayaƙi.
31 The sunne shalbe turned into darkenesse, and the moone into blood, before the great and terrible day of the Lord come.
Rana za tă duhunta wata kuma yă zama jini kafin isowar babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji.
32 But whosoeuer shall call on the Name of the Lord, shalbe saued: for in mount Zion, and in Ierusale shalbe deliuerance, as the Lord hath said, and in the remnant, whom the Lord shall call.
Amma dukan waɗanda suka nemi Ubangiji za su tsira. Kamar yadda Ubangiji ya ce, gama a Dutsen Sihiyona da Urushalima akwai ceto, a cikin waɗannan da Ubangiji ya kira.

< Joel 2 >