< Job 40 >

1 Moreouer ye Lord spake vnto Iob, and said,
Ubangiji ya ce wa Ayuba,
2 Is this to learne to striue with the Almightie? he that reprooueth God, let him answere to it.
“Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
3 Then Iob answered the Lord, saying,
Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
4 Beholde, I am vile: what shall I answere thee? I will lay mine hand vpon my mouth.
“Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
5 Once haue I spoken, but I will answere no more, yea twise, but I will proceede no further.
Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
6 Againe the Lord answered Iob out of the whirle winde, and said,
Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
7 Girde vp now thy loynes like a man: I will demaunde of thee, and declare thou vnto me.
“Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
8 Wilt thou disanul my iudgement? or wilt thou condemne me, that thou mayst be iustified?
“Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
9 Or hast thou an arme like God? or doest thou thunder with a voyce like him?
Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
10 Decke thy selfe now with maiestie and excellencie, and aray thy selfe with beautie and glory.
Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
11 Cast abroad the indignation of thy wrath, and beholde euery one that is proude, and abase him.
Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
12 Looke on euery one that is arrogant, and bring him lowe: and destroy the wicked in their place.
Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
13 Hide them in the dust together, and binde their faces in a secret place.
Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
14 Then will I confesse vnto thee also, that thy right hand can saue thee.
Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
15 Behold now Behemoth (whom I made with thee) which eateth grasse as an oxe.
“Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
16 Behold now, his strength is in his loynes, and his force is in the nauil of his belly.
Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
17 When hee taketh pleasure, his taile is like a cedar: the sinews of his stones are wrapt together.
Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
18 His bones are like staues of brasse, and his small bones like staues of yron.
Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
19 He is the chiefe of the wayes of God: he that made him, will make his sworde to approch vnto him.
Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
20 Surely the mountaines bring him foorth grasse, where all the beastes of the fielde play.
Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
21 Lyeth hee vnder the trees in the couert of the reede and fennes?
Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
22 Can the trees couer him with their shadow? or can the willowes of the riuer compasse him about?
Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
23 Behold, he spoyleth the riuer, and hasteth not: he trusteth that he can draw vp Iorden into his mouth.
Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
24 Hee taketh it with his eyes, and thrusteth his nose through whatsoeuer meeteth him.
Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?

< Job 40 >