< Job 24 >

1 Howe should not the times be hid from the Almightie, seeing that they which knowe him, see not his dayes?
“Domin me Maɗaukaki ba zai sa ranar shari’a ba? Don me waɗanda suka san shi suke faman samun irin ranakun nan?
2 Some remoue the land marks, that rob the flockes and feede thereof.
Mugaye suna satar fili ta wurin matsar da duwatsun da aka yi iyaka da su; suna satar dabbobi su kuma yi kiwon su.
3 They leade away the asse of the fatherles: and take the widowes oxe to pledge.
Suna ƙwace wa marayu jakunansu suna kuma ƙwace wa gwauruwa sa don suna binta bashi.
4 They make the poore to turne out of the way, so that the poore of the earth hide themselues together.
Suna ture matalauta daga hanya suna kuma sa dole matalautan ƙasar su ɓoye.
5 Behold, others as wilde asses in the wildernesse, goe forth to their businesse, and rise early for a praye: the wildernesse giueth him and his children foode.
Kamar jakunan jeji a hamada, matalauta suna aikin neman abinci gonaki marasa amfani suna tanada abinci wa’ya’yansu.
6 They reape his prouision in the fielde, but they gather the late vintage of the wicked.
Suna girbi a gonakin da ba nasu ba, suna yin kala a gonar inabi ta mugaye.
7 They cause the naked to lodge without garment, and without couering in the colde.
Don ba su da tufafi, sukan kwana tsirara; ba su da wani abin da zai rufe su cikin sanyi.
8 They are wet with the showres of the moutaines, and they imbrace the rocke for want of a couering.
Sun jiƙe sharkaf da ruwan da yake kwararowa daga duwatsu, sun rungume duwatsu don rashin wurin fakewa.
9 They plucke the fatherles from the breast, and take the pledge of the poore.
Ana ƙwace jinjiri mai shan mama; ana ƙwace ɗan yaron matalauci don biyan bashi.
10 They cause him to go naked without clothing, and take the glening from the hungrie.
Don ba su da tufafi suna yawo tsirara; suna dakon dammunan hatsi amma duk da haka suna cikin shan yunwa.
11 They that make oyle betweene their walles, and treade their wine presses, suffer thirst.
Suna matse zaitun a cikin kunyoyi suna kuma matse ruwan inabi daga’ya’yan inabi, duk da haka suna fama da ƙishi.
12 Men cry out of the citie, and the soules of the slayne cry out: yet God doth not charge them with follie.
Ana jin nishin masu mutuwa daga birni, kuma rayukan waɗanda aka ji musu rauni suna kuka suna kira don taimako. Amma bai ba wani laifi ba.
13 These are they, that abhorre the light: they know not the wayes thereof, nor continue in the paths thereof.
“Akwai waɗanda suke yi wa haske tawaye, waɗanda ba su san hanyoyinsa ba ko kuma ba su taɓa bin hanyoyinsa ba.
14 The murtherer riseth earely and killeth the poore and the needie: and in the night he is as a theefe.
Sa’ad da hasken yini ya tafi, mai kisankai yakan tashi; yă je yă kashe matalauta da masu bukata; a cikin dare yake shigowa kamar ɓarawo.
15 The eye also of the adulterer waiteth for the twilight, and sayth, None eye shall see me, and disguiseth his face.
Idanun mazinaci suna jiran yamma ta yi sosai; yana tunani cewa, ‘Ba wanda zai gan ni,’ sai kuma yă ɓoye fuskarsa.
16 They digge through houses in the darke, which they marked for themselues in the daye: they knowe not the light.
Cikin duhu mutane suna fasa gidaje, amma da rana sukan kulle kansu; ba sa so wani abu yă haɗa su da haske.
17 But the morning is euen to them as the shadow of death: if one knowe them, they are in the terrours of the shadowe of death.
Gama dukansu, duhu mai yawa shi ne safiyarsu; suna abokantaka da razanar duhu.
18 He is swift vpon the waters: their portion shalbe cursed in the earth: he will not behold the way of the vineyardes.
“Duk da haka kamar abu marar nauyi suke a kan ruwa; gefen ƙasar da suke, an la’anta ta, yadda ba wanda yake zuwa gonar inabinsu.
19 As the dry ground and heate consume the snowe waters, so shall the graue the sinners. (Sheol h7585)
Kamar yadda zafi da fări suke shanye ƙanƙarar da ta narke, haka kabari zai ƙwace waɗanda suka yi zunubi. (Sheol h7585)
20 The pitifull man shall forget him: the worme shall feele his sweetenes: he shalbe no more remembered, and the wicked shalbe broke like a tree.
Waɗanda suka haife su za su manta da su, tsutsotsi za su cinye su; ba za a sāke tunawa da mugaye ba amma an sare su kamar itace.
21 He doth euil intreat ye barren, that doeth not beare, neither doeth he good to the widowe.
Suna cutar macen da ba ta da ɗa, suna nuna wa gwauruwa rashin alheri.
22 He draweth also the mighty by his power, and when he riseth vp, none is sure of life.
Amma Allah cikin ikonsa yakan kawar da masu ƙarfi, ko da yake sun yi ƙarfi, ba su da tabbacin rayuwa.
23 Though men giue him assurance to be in safetie, yet his eyes are vpon their wayes.
Mai yiwuwa zai bar su su zauna cikin kwanciyar hankali, amma idanunsa suna kansu.
24 They are exalted for a litle, but they are gone, and are brought lowe as all others: they are destroyed, and cut off as the toppe of an eare of corne.
Sukan samu cin nasara na ɗan lokaci, amma kuma za su ɓace; za su fāɗi a tattara su kamar sauran; za a datse su kamar kan hatsi.
25 But if it be not so, where is he? or who wil proue me a lyer, and make my words of no value?
“In wannan ba haka ba ne, wane ne zai shaida ƙarya nake yi har yă ƙi yarda da maganata?”

< Job 24 >