< Jeremiah 6 >

1 O ye children of Beniamin, prepare to flee out of the middes of Ierusalem, and blowe the trumpet in Tekoa: set vp a standart vpon Beth-haccerem: for a plague appeareth out of the North and great destruction.
“Ku gudu neman mafaka, mutanen Benyamin! Ku gudu daga Urushalima! Ku busa ƙaho a Tekowa! Ku ba da alama a Bet-Hakkerem! Gama masifa tana zuwa daga arewa, mummunar hallaka ce kuwa.
2 I haue compared the daughter of Zion to a beautifull and daintie woman.
Zan hallaka Diyar Sihiyona, kyakkyawa da kuma mai laulayi.
3 The pastors with their flockes shall come vnto her: they shall pitche their tentes rounde about by her, and euery one shall feede in his place.
Makiyaya da garkunansu za su taso mata; za su kafa tentunansu kewaye da ita, kowanne yana lura da sashensa.”
4 Prepare warre against her: arise, and let vs goe vp toward the South: wo vnto vs: for the day declineth, and the shadowes of the euening are stretched out.
“Mu shirya don yaƙi da ita! Ku tashi, bari mu fāɗa mata da tsakar rana! Amma, kaito, rana tana fāɗuwa, inuwar yamma kuwa sai ƙaran tsawo take.
5 Arise, and let vs goe vp by night, and destroy her palaces.
Saboda haka ku tashi, bari mu fāɗa mata da dare mu rurrushe kagaranta!”
6 For thus hath the Lord of hostes said, Hewe downe wood, and cast a mounte against Ierusalem: this citie must be visited: all oppression is in the middes of it.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku sassare itatuwan ku tula ƙasa kewaye da Urushalima. Dole a hukunta wannan birni; saboda ya cika da zalunci.
7 As the fountaine casteth out her waters, so she casteth out her malice: crueltie and spoyle is continually heard in her before me with sorowe and strokes.
Kamar yadda rijiya takan ba da ruwarta, haka birnin yake da muguntarsa. Ana jin labarin rikici da hallaka a cikinsa; ciwonsa da mikinsa kullum suna a gabana.
8 Be thou instructed, O Ierusalem, lest my soule depart from thee, lest I make thee desolate as a land, that none inhabiteth.
Ki ji gargaɗi, ya Urushalima, ko kuwa in juya daga gare ki in mai da ƙasarki kufai don kada wani ya zauna a cikinta.”
9 Thus sayeth the Lord of hostes, They shall gather as a vine, the residue of Israel: turne backe thine hande as the grape gatherer into the baskets.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Bari su yi kalan raguwar Isra’ila a yi kalan sarai yadda ake yi wa inabi; ka sāke miƙa hannunka a kan rassan, kamar mai tattara inabi.”
10 Vnto whome shall I speake, and admonish that they may heare? beholde, their eares are vncircumcised, and they cannot hearken: beholde, the worde of the Lord is vnto them as a reproche: they haue no delite in it.
Ga wa zan yi magana in kuma gargaɗar? Wa zai saurare ni? Kunnuwansu sun toshe don kada su ji. Maganar Ubangiji ta zama abin zargi a gare su; ba sa jin daɗinta.
11 Therefore I am full of the wrath of the Lord: I am weary with holding it: I will powre it out vpon the children in the streete, and likewise vpon the assembly of the yong men: for the husband shall euen be taken with the wife, and the aged with him that is full of daies.
Amma ina cike da fushin Ubangiji, kuma ba na iya kannewa. “Ka kwararo shi a kan yara a titi da kuma a kan samarin da suka tattaru; za a kama miji da mata a cikinsa, tsofaffi da suka tsufa tukub.
12 And their houses with their landes, and wiues also shalbe turned vnto strangers: for I will stretch out mine hande vpon the inhabitants of the land, sayeth the Lord.
Za a ba da gidajensu ga waɗansu, tare da gonakinsu da matansu, sa’ad da na miƙa hannuna gāba da waɗanda suke zama a ƙasar,” in ji Ubangiji.
13 For from the least of them, euen vnto the greatest of them, euery one is giuen vnto couetousnesse, and from the Prophet euen vnto the Priest, they all deale falsely.
“Daga ƙarami zuwa babba, dukansu masu haɗama ne don riba; har da annabawa da firistoci, dukansu suna aikata rashin gaskiya.
14 They haue healed also ye hurt of the daughter of my people with sweete woordes, saying, Peace, peace, when there is no peace.
Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, ‘Lafiya, Lafiya,’ alhali kuwa ba lafiya.
15 Were they ashamed when they had committed abomination? nay, they were not ashamed, no neither coulde they haue any shame: therefore they shall fall among the slaine: when I shall visite them, they shall be cast downe, sayth the Lord.
Suna jin kunyar halinsu na banƙyama? A’a, ba sa jin kunya sam; ba su ma san yadda za su soke kai ba. Saboda haka za su fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za a hamɓarar da su sa’ad da na hukunta su,” in ji Ubangiji.
16 Thus sayeth the Lord, Stande in the waies and beholde, and aske for the olde way, which is the good way and walke therein, and yee shall finde rest for your soules: but they saide, We will not walke therein.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba; ku nemi hanyoyin dā, ku tambaya inda hanyar mai kyau take, ku yi tafiya a kanta, za ku kuwa sami hutu wa rayukanku. Amma kun ce, ‘Ba za mu bi ta ba.’
17 Also I set watchmen ouer you, which said, Take heede to the sound of the trumpet: but they said, We will not take heede.
Na naɗa muku masu tsaro a kanku na kuma ce, ‘Ku saurari karan ƙaho!’ Amma kuka ce, ‘Ba za mu saurara ba.’
18 Heare therefore, yee Gentiles, and thou Congregation knowe, what is among them.
Saboda haka ku, ya al’ummai; ku lura Ya shaidu, abin da zai faru da su.
19 Heare, O earth, beholde, I will cause a plague to come vpon this people, euen the fruite of their owne imaginations: because they haue not taken heede vnto my woordes, nor to my Lawe, but cast it off.
Ki ji, ya duniya. Zan kawo masifa a kan waɗannan mutane, sakayyar ƙulle-ƙullensu, domin ba su saurari maganata ba suka kuma ƙi dokata.
20 To what purpose bringest thou mee incense from Sheba, and sweete calamus from a farre countrey? Your burnt offerings are not pleasant, nor your sacrifices sweete vnto me.
Babu riba a kawo mini turare daga Sheba ko rake mai zaƙi daga ƙasa mai nisa? Ba zan karɓi hadayunku na ƙonawa ba; ba na jin daɗin sadakokinku.”
21 Therefore thus sayeth the Lord, Beholde, I will laie stumbling blockes before this people, and the fathers and the sonnes together shall fall vpon them: the neighbour and his friende shall perish.
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Zan sa abin tuntuɓe gaban mutanena. Mahaifi da’ya’yansa maza za su yi tuntuɓe a kan juna; maƙwabci da abokansa za su hallaka.”
22 Thus sayeth the Lord, Beholde, a people commeth from the North countrey, and a great nation shall arise from the sides of the earth.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Duba, sojoji suna zuwa daga ƙasar arewa; babbar al’umma ce ta yunƙuro daga iyakokin duniya.
23 With bowe and shield shall they be weaponed: they are cruell and will haue no compassion: their voyce roareth like the sea, and they ride vpon horses, well appointed, like men of warre against thee, O daughter Zion.
Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne kuma marasa tausayi. Motsinsu kamar ƙugin teku ne yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa a jere kamar wanda ya yi shirin yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Sihiyona.”
24 We haue heard their fame, and our handes waxe feeble sorrowe is come vpon vs, as the sorrowe of a woman in trauaile.
Mun ji labari a kansu, hannuwanmu kuwa suka yi laƙwas. Azaba ta kama mu, zafi kamar na mace mai naƙuda.
25 Goe not foorth into the fielde, nor walke by the way: for the sword of the enemie and feare is on euery side.
Kada ku fita zuwa gonaki ko ku yi tafiya a hanyoyi, gama abokin gāba yana da takobi, kuma akwai razana ko’ina.
26 O daughter of my people, girde thee with sackecloth, and wallowe thy selfe in the ashes: make lamentation, and bitter mourning as for thine onely sonne: for the destroier shall suddenly come vpon vs.
Ya mutanena, ku sanya tufafin makoki ku yi birgima a toka; ku yi kuka mai zafi irin wanda akan yi wa ɗa tilo, gama nan da nan mai hallakarwa zai auko mana.
27 I haue set thee for a defence and fortresse among my people, that thou maiest knowe and trie their waies.
“Na maishe ka mai jarrabawar ƙarfe mutanena ne kuwa ƙarfen, don ka lura ka kuma gwada hanyoyinsu.
28 They are all rebellious traitours, walking craftily: they are brasse, and yron, they all are destroyers.
Su duka masu taurinkai ne,’yan tawaye, suna yawo suna baza jita-jita. Su tagulla ne da ƙarfe; dukansu lalatattu ne.
29 The bellowes are burnt: the lead is consumed in the fire: the founder melteth in vaine: for the wicked are not taken away.
Mazuga yana zuga da ƙarfi don yă ƙone dalma da wuta, amma tacewa yana tafiya a banza; ba a fitar da mugaye.
30 They shall call them reprobate siluer, because the Lord hath reiected them.
Ana ce da su azurfar da aka ƙi, gama Ubangiji ya ƙi su.”

< Jeremiah 6 >