< Jeremiah 52 >

1 Zedekiah was one and twentie yeere olde when he began to reigne, and he reigned eleuen yeeres in Ierusalem, and his mothers name was Hamutal, the daughter of Ieremiah of Libnah.
Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Sunan uwarsa Hamutal,’yar Irmiya, wanda yake zaune a Libna.
2 And he did euil in the eyes of the Lord, according to all that Iehoiakim had done.
Sarki Zedekiya ya aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda Sarki Yehohiyakim ya yi.
3 Doubtlesse because the wrath of the Lord was against Ierusalem and Iudah, till he had cast them out from his presence, therefore Zedekiah rebelled against the King of Babel.
Al’amarin ya zama da muni ƙwarai a cikin Isra’ila da Yahuda, don haka Ubangiji ya husata har ya sa aka kai mutanen bautar talala. Zedekiya kuwa ya tayar wa Sarkin Babilon.
4 But in the ninth yeere of his reigne, in the tenth moneth the tenth day of the moneth came Nebuchad-nezzar King of Babel, he and all his hoste against Ierusalem, and pitched against it, and buylt fortes against it round about.
A kan rana ta goma ga watan goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya, Sarkin Yahuda, sai Nebukadnezzar, Sarkin Babilon, ya zo yaƙi da Urushalima tare da dukan sojojinsa. Suka kewaye ta da yaƙi, suka gina katanga kewaye da ita.
5 So the citie was besieged vnto the eleuenth yeere of the King Zedekiah.
An kewaye birnin da yaƙi har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
6 Now in the fourth moneth, the ninth day of the moneth, the famine was sore in ye citie, so that there was no more bread for ye people of the land.
A kan rana ta tara a watan huɗu na wannan shekara, yunwa ta tsananta ƙwarai a birnin. Mutane suka rasa abin da za su ci.
7 Then the citie was broken vp and all the men of warre fled, and went out of the citie by night, by the way of the gate betweene the two walles, which was by the kings garden: (now the Caldeans were by the citie round about) and they went by the way of the wildernes.
Sai aka huda katangan birnin, sojojin kuwa suka gudu, suka fita daga cikin birnin da dare ta hanyar ƙofar da take tsakanin bango biyu, kusa da gonar sarki, sa’ad da Babiloniyawa suke kewaye da birnin. Sojojin suka nufi wajen Araba.
8 But the army of the Caldeans pursued after the king, and tooke Zedekiah in the desert of Iericho, and all his host was scattered from him.
Amma sojojin Babiloniyawa suka runtumi sarki Zedekiya, suka ci masa a filayen Yeriko. Dukan sojoji suka yashe shi.
9 Then they tooke the king and caryed him vp vnto the king of Babel to Riblah in the lande of Hamath, where he gaue iudgement vpon him.
Da aka kama Zedekiya, sai aka kai shi wurin Sarkin Babilon a Ribla a ƙasar Hamat, a nan ne Sarkin Babilon ya yanke masa shari’a.
10 And the king of Babel slewe the sonnes of Zedekiah, before his eyes he slew also al ye princes of Iudah in Riblah.
Sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idonsa. Ya kuma kashe dukan shugabannin Yahuda a Ribla.
11 Then he put out the eyes of Zedekiah, and the king of Babel bound him in chaines, and caried him to Babel, and put him in pryson till the day of his death.
Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya, ya kuma sa masa ƙuƙumi, aka kai shi Babilon inda aka sa shi a kurkuku har ran da ya mutu.
12 Now in the fift moneth in the tenth day of the moneth (which was the nineteenth yere of ye King Nebuchad-nezzar King of Babel) came Nebuzar-adan chiefe steward which stoode before the king of Babel in Ierusalem,
A kan rana ta goma ga watan biyar a shekara ta goma sha tara ta sarautar Nebukadnezzar, Sarkin Babilon, sai Nebuzaradan shugaban matsara da kuma ɗan majalisar sarki, ya zo Urushalima.
13 And burnt the House of the Lord, and the Kings house, and all the houses of Ierusalem, and all the great houses burnt he with fire.
Sai ya ƙone haikalin Ubangiji, da gidan sarki, da dukan gine-gine masu alfarman da suke Urushalima.
14 And al the armie of the Caldeans that were with the chiefe steward, brake downe all ye walles of Ierusalem round about.
Sojojin Babiloniyawa da suke tare da shugaban matsara, suka rushe dukan katangan Urushalima.
15 Then Nebuzar-adan the chiefe steward caried away captiue certaine of the poore of the people, and the residue of the people that remayned in the citie, and those that were fled, and fallen to the king of Babel, with the rest of the multitude.
Sa’an nan Nebuzaradan shugaban matsara ya kwashe waɗansu matalauta, da sauran mutane da aka bari a birnin, da waɗanda suka gudu zuwa wurin Sarkin Babilon, da sauran masu sana’a, ya kai su bautar talala a Babilon.
16 But Nebuzar-adan the chiefe steward left certaine of the poore of the lande, to dresse the vines, and to till the land.
Amma ya bar waɗansu matalauta na gaske a ƙasar don su yi aiki a gonakin inabi, da sauran gonaki.
17 Also the pillars of brasse that were in the House of the Lord, and the bases, and the brasen Sea, that was in the house of ye Lord, the Caldeans brake, and caried all the brasse of them to Babel.
Babiloniyawa kuwa suka farfasa ginshiƙan tagulla, da dakalai, da babbar kwatarniya, waɗanda suke a haikalin Ubangiji. Suka kwashe tagulla duka suka kai Babilon.
18 The pots also and the besomes, and the instruments of musicke, and the basins, and the incense dishes, and all the vessels of brasse wherewith they ministred, tooke they away.
Suka kwashe tukwanen ƙarfe, da manyan cokula, da hantsuka, da daruna, da tasoshin ƙona turare, da kayayyakin tagulla waɗanda ake amfani da su domin hidimar haikali.
19 And the bowles, and the ashpannes, and the basins, and the pots, and the candlestickes, and the incense dishes, and the cuppes, and all that was of golde, and that was of siluer, tooke the chiefe steward away,
Suka kuma kwashe ƙananan kwanonin sha, da farantan wuta, da daruna, da tukwane, da alkukai, da tasoshin ƙona turare, da kwanonin miƙa hadayar sha. Duk abin da yake na zinariya da azurfa, shugaban matsara ya kwashe.
20 With the two pillars, one Sea, and twelue brasen bulles, that were vnder the bases, which King Salomon had made in ye house of ye Lord: the brasse of all these vessels was without weight.
Tagullar da sarki Solomon ya yi wa haikalin Ubangiji da ita, wato, ginshiƙai biyu, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla, da bijimai goma sha biyu, waɗanda suke ɗauke da kwatarniya, da dakalai, ta fi ƙarfin a auna.
21 And concerning the pillars, the height of one pillar was eighteene cubites, and a threede of twelue cubites did compasse it, and the thicknesse thereof was foure fingers: it was holowe.
Tsawon kowane ginshiƙi kamu goma sha takwas ne, kewayensa kuwa kamu goma sha biyu ne, kaurinsa kuma huɗu ne. Kowannensu yana da rami a ciki.
22 And a chapiter of brasse was vpon it, and the height of one chapiter was fiue cubites with networke, and pomegranates vpon the chapiters round about, all of brasse: the seconde pillar also, and the pomegranates were like vnto these.
A kan kowane ginshiƙi, an yi masa dajiyar tagulla, tsayinta kamu biyar. A bisa kan kowace dajiya akwai raga da siffofin rumman na tagulla kewaye da dajiyar. Ginshiƙi na biyu ma haka yake da siffofin rumman.
23 And there were ninetie and sixe pomegranates on a side: and all the pomegranates vpon the net worke were an hundreth round about.
Akwai siffofin rumman tasa’in da shida da ake gani a gefen. Dukan siffofin rumman da suke a kan ragar kewaye, guda ɗari ne.
24 And the chiefe steward tooke Sheraiah the chiefe Priest, and Zephaniah the seconde Priest, and the three keepers of the doore.
Shugaban matsara kuma ya ɗauki Serahiya babban firist, da Zefaniya wanda yake biye da babban firist, da mutum uku masu tsaron ƙofar, ya tafi da su.
25 Hee tooke also out of the citie an Eunuch, which had the ouersight of the men of warre, and seuen men that were in the Kings presence, which were founde in the citie, and Sopher captayne of the hoste who mustered the people of the lande, and threescore men of the people of the land, that were found in the middes of the citie.
Daga cikin birnin kuma ya ɗauki shugaban sojojin, da mutum bakwai’yan majalisar sarki, da magatakardan shugaban sojojin wanda yakan tara sojojin ƙasar, da mutane sittin na ƙasar, waɗanda aka same su a birnin, ya tafi da su.
26 Nebuzar-adan the chiefe stewarde tooke them, and brought them to the king of Babel to Riblah.
Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da waɗannan mutane wurin Sarkin Babilon a Ribla,
27 And the king of Babel smote them, and slewe them in Riblah, in the lande of Hamath: thus Iudah was caried away captiue out of his owne land.
Sarkin Babilon kuwa ya kashe su a Ribla a ƙasar Hamat. Haka aka tafi da mutanen Yahuda bautar talala, daga ƙasarta.
28 This is the people, whome Nebuchad-nezzar caried away captiue, in the seuenth yeere, euen three thousande Iewes, and three and twentie.
Wannan shi ne yawan mutanen da Nebukadnezzar ya kai su bauta. A shekara ta bakwai ta sarautarsa, ya tafi da Yahudawa 3,023;
29 In the eightenth yere of Nebuchad-nezzar he caried away captiue from Ierusalem eight hundreth thirtie and two persons.
a shekara ta goma sha takwas ta sarautar Nebukadnezzar, ya tafi da Yahudawa daga Urushalima 832;
30 In the three and twentieth yeere of Nebuchad-nezzar, Nebuzar-adan the chiefe stewarde caried away captiue of the Iewes seuen hundreth fourtie and fiue persons: all the persons were foure thousand and sixe hundreth.
a shekara ta ashirin da uku ta sarautarsa, Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da Yahudawa 745. Jimillarsu duka 4,600 ne.
31 And in the seuen and thirtieth yeere of the captiuitie of Iehoiachin King of Iudah, in the twelfth moneth, in the fiue and twentieth day of the moneth, Euil-merodach King of Babel, in the first yeere of his reigne, lifted vp the head of Iehoiachin King of Iudah, and brought him out of pryson,
A shekarar da Ewil-Merodak ya zama Sarkin Babilon, sai ya nuna wa Yehohiyacin Sarkin Yahuda alheri. Ya fisshe shi daga kurkuku. Wannan ya faru ran ashirin da biyar ga watan goma sha biyu a shekara ta talatin da bakwai bayan da aka kai Yehohiyacin bauta.
32 And spake kindly vnto him, and set his throne aboue the throne of the Kings, that were with him in Babel,
Ewil-Merodak ya nuna wa Yehohiyacin alheri, ya ba shi matsayi na daraja fiye da waɗansu sarakunan da aka kai su bautar talala a Babilon tare da shi.
33 And changed his pryson garmentes, and he did continually eate bread before him all the dayes of his life.
Yehohiyacin ya tuɓe tufafin kurkuku, ya riƙa cin abinci kullum a teburin sarki, har dukan sauran kwanakin ransa.
34 His porcion was a continuall portion giuen him of ye king of Babel, euery day a certaine, all the dayes of his life vntill he died.
Kowace rana akan ba shi kyauta bisa ga umarnin sarkin Babilon, saboda bukatarsa. Haka aka yi masa har rasuwarsa.

< Jeremiah 52 >