< Jeremiah 51 >

1 Thus sayth the Lord, Beholde, I wil raise vp against Babel, and against the inhabitants that lift vp their heart against me, a destroying wind,
Ubangiji ya ce, “Ga shi, zan zuga ruhun mai hallakarwa a kan Babilon da mutanen Leb Kamai.
2 And wil send vnto Babel fanners that shall fanne her, and shall empty her land: for in the day of trouble they shalbe against her on euery side.
Zan aika da baƙi zuwa Babilon su casa ta su kuma yi kaca-kaca da ƙasarta; za su yi hamayya da ita a kowane gefe a ranar masifarta.
3 Also to the bender that bendeth his bowe, and to him that lifteth himselfe vp in his brigandine, will I say, Spare not her yong men, but destroy all her hoste.
Kada ku bar maharbi yă ja bakansa, kada kuma ku bari yă sa kayan yaƙinsa. Kada ku rage samarinta, ku hallaka sojojinta ƙaf.
4 Thus the slaine shall fall in the lande of the Caldeans, and they that are thrust through in her streetes.
Za su fāɗi matattu a ƙasar Babilon, da munanan raunuka a titunanta.
5 For Israel hath bene no widowe, nor Iudah from his God, from the Lord of hostes, though their lande was filled with sinne against the holy one of Israel.
Gama Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila da Yahuda bai yashe su ba, ko da yake ƙasarsu cike da take da laifi a gaban Mai Tsarki na Isra’ila.
6 Flee out of the middes of Babel, and deliuer euery man his soule: be not destroyed in her iniquitie: for this is the time of the Lordes vengeance he will render vnto her a recompence.
“Ku gudu daga cikin Babilon! Bari kowa yă ceci ransa! Kada a hallaka saboda zunubanta. Gama lokaci ne don ramuwar Ubangiji, zai sāka mata bisa ga alhakinta.
7 Babel hath bene as a golden cuppe in the Lordes hand, that made all the earth drunken: the nations haue drunken of her wine, therefore do the nations rage.
Babilon ta zama ƙoƙon zinariya a hannun Ubangiji, ta sa dukan duniya ta yi maye. Ƙasashe sun sha ruwan inabinta, saboda haka yanzu sun haukace.
8 Babel is suddenly fallen, and destroyed: howle for her, bring balme for her sore, if she may be healed.
Farat ɗaya Babilon za tă fāɗi ta farfashe. Ku yi kuka dominta! Ku samo mata magani saboda azabarta; wataƙila za a iya warkar da ita.
9 We would haue cured Babel, but she could not be healed: forsake her, and let vs go euery one into his owne countrey: for her iudgement is come vp vnto heauen, and is lifted vp to ye cloudes.
“‘Da mun warkar da Babilon, amma ba za tă warke ba; mu ƙyale ta kowane yă koma garinsu, gama hukuncinta ya kai sammai, ya yi tsawo kamar gizagizai.’
10 The Lord hath brought forth our righteousnesse: come and let vs declare in Zion the worke of the Lord our God.
“‘Ubangiji ya baratar da mu; zo mu tafi mu yi shelarsa a Sihiyona mu faɗa abin da Ubangiji Allahnmu ya yi.’
11 Make bright the arrowes: gather the shieldes: the Lord hath raised vp the spirit of the King of the Medes: for his purpose is against Babel to destroy it, because it is the vengeance of the Lord, and the vengeance of his Temple.
“Ku wasa kibiyoyi, ku ɗauko garkuwoyi! Ubangiji ya zuga sarakunan Medes, domin niyyarsa ce yă hallaka Babilon. Ubangiji zai yi ramuwa, zai yi ramuwa saboda haikalinsa.
12 Set vp the standart vpon the walles of Babel, make the watch strong: set vp the watchmen: prepare the skoutes: for the Lord hath both deuised, and done that which he spake against the inhabitantes of Babel.
Ku tā da tuta gāba da katangan Babilon! Ku ƙara matsara, ku kafa masu tsaro, ku shirya kwanto! Ga shi, Ubangiji zai aikata abin da ya faɗa umarninsa a kan mutanen Babilon.
13 O thou that dwellest vpon many waters, abundant in treasures, thine ende is come, euen the ende of thy couetousnes.
Ke da kike zama kusa da ruwaye da kike kuma wadatar dukiya, ƙarshenki ya zo, lokaci ya yi da za a kau da ke.
14 The Lord of hostes hath sworne by him selfe, saying, Surely I will fill thee with men, as with caterpillers, and they shall cry and shoute against thee.
Ubangiji Maɗaukaki ya rantse da zatinsa, ya ce Tabbatacce zan cika ka da mutane kamar fāra, za su kuwa yi sowa don nasara a kanka.
15 He hath made the earth by his power, and established the world by his wisedome, and hath stretched out the heauen by his discretion.
“Ya halicci ƙasa ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa, ya kuma shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
16 Hee giueth by his voyce the multitude of waters in the heauen, and he causeth the cloudes to ascend from the endes of the earth: he turneth lightnings to raine, and bringeth forth the winde out of his treasures.
Sa’ad da ya yi tsawa ruwan da suke sammai sukan yi ruri; yakan sa gizagizai su tashi daga ƙarshen duniya. Yakan tura walƙiya tare da ruwan sama yakan kuma saki iska daga cikin taskokinsa.
17 Euery man is a beast by his owne knowledge: euery founder is confounded by the grauen image: for his melting is but falsehood, and there is no breath therein.
“Kowane mutum marar azanci ne kuma ba shi da sani; kowane maƙerin zinariya yakan sha kunya daga wurin gumakansa. Siffofinsa na ƙarya ne; babu numfashi a cikinsu.
18 They are vanitie, and the worke of errours: in the time of their visitation they shall perish.
Su marasa amfani ne, abubuwan ba’a ne kawai; sa’ad da lokacin hukuncinsu ya kai, za su hallaka.
19 The portion of Iaakob is not like them: for he is the maker of all things, and Israel is the rodde of his inheritance: the Lord of hostes is his Name.
Wanda yake na wajen Yaƙub ba kamar waɗannan ba ne, gama shi ne Mahalicci dukan abu, har da kabilar abin gādonsa, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
20 Thou art mine hammer, and weapons of warre: for with thee will I breake the nations, and with thee wil I destroy kingdomes,
“Kai ne kulkin yaƙina, kayan yaƙina, da kai ne na ragargaza ƙasashe, da kai ne na hallaka mulkoki,
21 And by thee wil I breake horse and horseman, and by thee will I breake the charet and him that rideth therein.
da kai ne na ragargaza doki da mahayi, da kai ne na ragargaza keken yaƙin da matuƙi,
22 By thee also will I breake man and woman, and by thee wil I breake olde and yong, and by thee wil I breake the yong man and the mayde.
da kai ne na ragargaza miji da mata, da kai ne na ragargaza tsoho da saurayi, da kai ne na ragargaza saurayi da budurwa,
23 I wil also breake by thee the shepheard and his flocke, and by thee will I breake the husband man and his yoke of oxen, and by thee will I breake the dukes and princes.
da kai ne na ragargaza makiyayi da garke, da kai ne na ragargaza manoma da dawakan noma, da kai ne na ragargaza masu mulki da shugabanni.
24 And I will render vnto Babel, and to all the inhabitants of the Caldeans all their euil, that they haue done in Zion, euen in your sight, sayth the Lord.
“Zan sāka wa Babilon da dukan mazaunan Babilon a idanunku saboda dukan muguntar da suka aikata a Sihiyona,” in ji Ubangiji.
25 Beholde, I come vnto thee, O destroying mountaine, sayth the Lord, which destroyest all the earth: and I will stretch out mine hand vpon thee, and rolle thee downe from the rockes, and wil make thee a burnt mountaine.
“Ga shi, ina gāba da kai, ya ke dutse mai hallakarwa, wadda ta hallaka duniya duka,” in ji Ubangiji. “Zan miƙa hannuna gāba da ke, zan mirgina ƙasa daga ƙwanƙolin dutse, zan maishe ki ƙonannen dutse.
26 They shall not take of thee a stone for a corner, nor a stone for foundations, but thou shalt be destroyed for euer, sayth the Lord.
Ba za a ɗauki dutsen yin kusurwa daga gare ki ba ko na kafa harsashen gini, gama za ki zama marar amfani har abada,” in ji Ubangiji.
27 Set vp a standard in the lande: blowe the trumpets among the nations: prepare the nations against her: call vp the kingdomes of Ararat, Minni, and Ashchenaz against her: appoynt the prince against her: cause horses to come vp as the rough caterpillers.
“Ku tā da tuta a ƙasa! Ku busa ƙahoni a cikin ƙasashe! Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, ku kira waɗannan mulkokin gāba da ita. Ararat, Minni, da Ashkenaz. A naɗa shugaba gāba da ita; ku shirya dawakai kamar fāra.
28 Prepare against her the nations with the Kings of the Medes, the dukes thereof, and the princes thereof, and all the land of his dominion.
Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, sarakunan Medes, gwamnoninsu da dukan masu shugabancinsu da kowace ƙasar da take ƙarƙashin mulkinsu.
29 And the land shall tremble and sorow: for the deuise of the Lord shalbe performed against Babel, to make the lande of Babel waste without an inhabitant.
Ƙasa ta girgiza tana makyarkyata saboda nufin Ubangiji na gāba da Babilon ya tabbata, nufinsa na mai da ƙasar Babilon kufai don kada kowa yă zauna a can.
30 The strong men of Babel haue ceased to fight: they haue remayned in their holdes: their strength hath fayled, and they were like women: they haue burnt her dwelling places, and her barres are broken.
Sojojin Babilon sun daina yaƙi, suna zaune a cikin kagaransu. Ƙarfinsu ya ƙare, sun zama mata. An sa wa wuraren zamanta wuta, an karya ƙyamaren ƙofofin garinta.
31 A post shall runne to meete the post, and a messenger to meete the messenger, to shew the King of Babel, that his citie is taken on a side thereof,
Maguji yana biye da maguji a guje, jakada yana biye da jakada, don su faɗa wa sarkin Babilon, cewa an ci birninsa a kowane gefe.
32 And that the passages are stopped, and the reedes burnt with fire, and the me of war troubled.
An ƙwace mashigai aka ƙone fadamu da wuta, sojoji kuma suka giggice.”
33 For thus sayth the Lord of hosts the God of Israel, the daughter of Babel is like a threshing floore: the time of her threshing is come: yet a litle while, and the time of her haruest shall come.
Ni Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila na ce, “’Yar Babilon kamar daɓen masussuka a lokacin da ake sussuka, ba da daɗewa ba lokacin girbe ta zai zo.”
34 Nebuchad-nezzar the King of Babel hath deuoured me, and destroyed me: he hath made me an emptie vessel: he swallowed mee vp like a dragon, and filled his belly with my delicates, and hath cast me out.
“Nebukadnezzar sarkin Babilon ya cinye mu, ya sa muka rikice, ya maishe mu kamar tulun da babu kome a cikinsa. Ya cinye mu kamar yadda dodon ruwa yakan yi ya kuma cika cikinsa da kayan marmarinmu, sa’an nan kuma ya yi amanmu.
35 The spoyle of me, and that which was left of me, is brought vnto Babel, shall the inhabitant of Zion say: and my blood vnto the inhabitantes of Caldea, shall Ierusalem say.
Bari abin da aka yi wa jikinmu yă kasance a bisa Babilon,” in ji mazaunan Sihiyona. “Bari jininmu yă kasance a kan waɗanda suke zama a Babilon,” in ji Urushalima.
36 Therefore thus sayth the Lord, Beholde, I will maintayne thy cause, and take vengeance for thee, and I will drie vp the sea, and drie vp her springes.
Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “Duba, zan tsaya muku, zan ɗaukar muku fansa, zan sa tekunta kafe in kuma sa maɓulɓulanta su ƙafe.
37 And Babel shall be as heapes, a dwelling place for dragons, an astonishment, and an hissing, without an inhabitant.
Babilon za tă zama tarin juji, wurin zaman diloli, abin ƙyama da abar ba’a, inda ba kowa.
38 They shall rore together like lions, and yell as the lyons whelpes.
Mutanenta duk suna ruri kamar zakoki, suna gurnani kamar’ya’yan zaki.
39 In their heate I will make them feastes, and I wil make them drunken, that they may reioyce, and sleepe a perpetual sleepe, and not wake, sayth the Lord.
Amma sa’ad da aka farkar da su, zan yi musu biki in sa su sha su bugu, domin yi sowa da dariya, sa’an nan su shiga barcin da ba za su farka ba,” in ji Ubangiji.
40 I wil bring them downe like lambes to the slaughter, and like rams and goates.
“Zan sauko da su kamar tumaki zuwa mayanka, kamar raguna da bunsurai.
41 How is Sheshach taken! and howe is the glory of the whole earth taken! how is Babel become an astonishment among the nations!
“Yadda za a ci Sheshak, taƙamar duniya duka za tă daina! Babilon za tă zama abar ƙyama a cikin al’ummai!
42 The sea is come vp vpon Babel: he is couered with the multitude of the waues thereof.
Teku zai malalo a kan Babilon, raƙumansa masu hauka za su rufe ta.
43 Her cities are desolate: the land is dry and a wildernes, a land wherein no man dwelleth, neither doth the sonne of man passe thereby.
Garuruwanta sun zama abin kufai, za tă zama hamada inda ba ruwa, ƙasar da ba mazauna, ba kuma mutumin da zai ratsa ta cikinta.
44 I wil also visite Bel in Babel, and I wil bring out of his mouth, that which he hath swallowed vp, and the nations shall runne no more vnto him, and the wall of Babel shall fall.
Zan hukunta Bel a Babilon, in sa ya yi aman abin da ya haɗiye. Ƙasashe ba za su ƙara bumbuntowa wurinsa ba. Katangan Babilon kuwa za tă rushe!
45 My people, go out of the middes of her, and deliuer yee euery man his soule from the fierce wrath of the Lord,
“Ku fito daga cikinta, jama’ata! Ku tsere da ranku! Ku tsere daga zafin fushin Ubangiji.
46 Least your heart euen faynt, and ye feare the rumour, that shalbe heard in the land: the rumour shall come this yeere, and after that in the other yeere shall come a rumour, and crueltie in the land, and ruler against ruler.
Kada zuciyarku tă yi suwu ko ku ji tsoro sa’ad da aka ji labarin a ƙasar, labari guda a wannan shekara, wani kuma a ta biye, labarin hargitsi a ƙasar mai mulki ya tasar wa mai mulki.
47 Therefore beholde, the dayes come, that I will visite the images of Babel, and the whole land shalbe confounded, and all her slayne shall fall in the middes of her.
Gama kwanaki tabbatacce suna zuwa, sa’ad da zan hukunta gumakan Babilon, zan kunyatar da dukan ƙasar kuma matattunta duk za su kwanta a cikinta.
48 Then the heauen and the earth, and all that is therein, shall reioyce for Babel: for the destroyers shall come vnto her from the North, saith the Lord.
Sa’an nan sama da ƙasa da dukan abin da yake cikinsu, za su yi sowa ta murna a kan Babilon, gama daga arewa masu hallakarwa su auko mata,” in ji Ubangiji.
49 As Babel caused the slaine of Israel to fal, so by Babel the slaine of all the earth did fall.
“Babilon za tă fāɗi saboda kisassun mutanen Isra’ila, kamar dai yadda kisassu dukan duniya suka fāɗi saboda Babilon.
50 Ye that haue escaped the sworde, goe away, stand not still: remember the Lord a farre of, and let Ierusalem come into your minde.
Ku waɗanda kuka tsere wa takobi, ku gudu kada ku tsaya! Ku tuna da Ubangiji a ƙasa mai nesa, ku kuma yi ta tunani a kan Urushalima.”
51 Wee are confounded because wee haue heard reproch: shame hath couered our faces, for straungers are come into the Sanctuaries of the Lordes House.
“Mun sha kunya saboda zargin da ake yi mana kunya ta rufe mu, domin baƙi sun shiga tsarkakan wurare na gidan Ubangiji.”
52 Wherefore behold, the dayes come, sayth the Lord, that I will visite her grauen images, and through all her land the wounded shall grone.
“Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta gumakanta, da kuma a dukan ƙasarta waɗanda aka yi wa rauni, za su yi nishi.
53 Though Babel should mount vp to heauen, and though shee should defend her strength on hye, yet from mee shall her destroyers come, sayth the Lord.
Ko da Babilon za tă kai sararin sama ne, ta gina kagaranta mai ƙarfi, duk da haka zan aiki masu hallakarwa a kanta,” in ji Ubangiji.
54 A sound of a cry commeth from Babel, and great destruction from the land of the Caldeans,
“Ku ji muryar kuka daga Babilon, Da hargowar babbar hallakarwa daga ƙasar Babiloniyawa!
55 Because the Lord hath layde Babel waste and destroyed from her the great voyce, and her waues shall roare like great waters, and a sounde was made by their noyse:
Gama Ubangiji zai rushe Babilon, zai sa ta ƙame bakinta na alfarma. Sojoji za su yi ta kutsawa kamar raƙuman ruwa; suna tā da muryoyinsu.
56 Because the destroyer is come vpon her, euen vpon Babel, and her strong men are taken, their bowes are broken: for the Lord God that recompenceth, shall surely recompence.
Gama mai hallakarwa ya auka wa Babilon, a kama sojojinta, a kuma kakkarya bakkunansu. Gama Ubangiji shi Allah ne mai sakayya; zai yi sakayya sosai.
57 And I will make drunke her princes, and her wise men, her dukes, and her nobles, and her strong men: and they shall sleepe a perpetuall sleepe, and not wake, sayth the King, whose Name is the Lord of hostes.
Zan sa mahukuntanta da masu hikimarta, gwamnoninta, shugabanninta da sojojinta su sha su bugu; za su dinga yin barcin da ba za su farka ba,” in ji Sarkin, mai suna Ubangiji Maɗaukaki.
58 Thus saith the Lord of hostes, The thicke wall of Babel shalbe broken, and her hie gates shall be burnt with fire, and the people shall labour in vaine, and the folke in ye fire, for they shalbe weary.
Ni Ubangiji Maɗaukaki, na ce, “Za a baje katangan nan na Babilon mai kauri za a kuma ƙone dogayen ƙyamarenta da wuta; mutane sun wahalar da kansu a banza, al’umma sun yi wahala kawai domin wutar lalata.”
59 The worde which Ieremiah the Prophet commanded Sheraiah the sonne of Neriiah, the sonne of Maaseiah, when he went with Zedekiah the King of Iudah into Babel, in the fourth yeere of his reigne: and this Sheraiah was a peaceable prince.
Jawabin da annabi Irmiya ya ba Serahiya, ɗan Neriya, wato, jikan Ma’asehiya, lokacin da ya tafi tare da Zedekiya, Sarkin Yahuda, zuwa Babilon a shekara ta huɗu ta mulkinsa. Serahiya shi ne shugaba mai lura da gidajen saukar baƙi.
60 So Ieremiah wrote in a booke all the euill that should come vpon Babel: euen al these things, that are written against Babel.
Irmiya ya rubuta a littafi dukan masifun da za su auko wa Babilon, wato, dukan wannan magana da aka rubuta a kan Babilon.
61 And Ieremiah sayd to Sheraiah, Whe thou commest vnto Babel, and shalt see, and shalt reade all these wordes,
Irmiya kuwa ya ce wa Serahiya, “Lokacin da ka kai Babilon, sai ka karanta dukan maganan nan.
62 Then shalt thou say, O Lord, thou hast spoken against this place, to destroy it, that none should remaine in it, neither man nor beast, but that it should be desolate for euer.
Ka kuma ce, ‘Ya Ubangiji, kai ne ka yi magana a kan wannan wuri, cewa za ka lalatar da shi, har ba abin da zai zauna a ciki, mutum ko dabba. Wurin zai zama kufai har abada.’
63 And when thou hast made an ende of reading this booke, thou shalt binde a stone to it, and cast it in the middes of Euphrates,
Sa’ad da ka gama karanta wannan littafi, sai ka ɗaura wa littafin dutse, sa’an nan ka jefar da shi tsakiyar Kogin Yuferites.
64 And shalt say, Thus shall Babel be drowned, and shall not rise from the euil, that I will bring vpon her: and they shall be weary. Thus farre are the wordes of Ieremiah.
Sa’an nan ka ce, ‘Haka Babilon za tă nutse, ba za tă ƙara tashi ba saboda masifar da zan kawo mata. Mutanenta kuwa za su fāɗi.’” Wannan shi ne ƙarshen kalmomin Irmiya.

< Jeremiah 51 >