< Jeremiah 36 >

1 And in the fourth yeere of Iehoiakim the sonne of Iosiah King of Iudah, came this word vnto Ieremiah from the Lord, saying,
A shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
2 Take thee a roule or booke, and write therein all the wordes that I haue spoken to thee against Israel, and against Iudah, and against all the nations, from the day that I spake vnto thee, euen from the dayes of Iosiah vnto this day.
“Ka ɗauki littafi ka rubuta dukan maganganun da na yi maka game da Isra’ila, Yahuda da kuma dukan sauran al’ummai daga lokacin da na fara maka magana a mulkin Yosiya har zuwa yanzu.
3 It may bee that the House of Iudah will heare of all the euill, which I determined to doe vnto them that they may returne euery man from his euil way, that I may forgiue their iniquitie and their sinnes.
Wataƙila sa’ad da mutanen Yahuda suka ji game da kowace masifar da na shirya in auka musu, kowa ya juya daga muguwar hanyarsa; sa’an nan in gafarta musu muguntarsu da kuma zunubinsu.”
4 Then Ieremiah called Baruch the sonne of Neriah, and Baruch wrote at the mouth of Ieremiah all the wordes of the Lord, which hee had spoken vnto him, vpon a roule or booke.
Saboda haka Irmiya ya kira Baruk ɗan Neriya, yayinda Irmiya yake fadar dukan waɗannan maganganun da Ubangiji ya faɗa masa, Baruk ya rubuta su a littafin.
5 And Ieremiah commanded Baruch, saying, I am shut vp, and can not go into the House of the Lord.
Sai Irmiya ya ce wa Baruk, “An hana ni, ba zan tafi haikalin Ubangiji ba.
6 Therefore goe thou, and reade the roule wherein thou hast written at my mouth the words of the Lord in the audience of the people in the Lordes House vpon the fasting day: also thou shalt reade them in the hearing of all Iudah, that come out of their cities.
Saboda haka ka tafi gidan Ubangiji a ranar azumi ka karanta wa mutane daga littafin maganar Ubangiji da na shibta maka ka rubuta. Ka karanta su ga dukan mutanen Yahuda waɗanda suka zo daga garuruwansu.
7 It may be that they will pray before the Lord, and euery one returne from his euill way, for great is the anger and the wrath, that the Lord hath declared against this people.
Wataƙila za su kawo kukansu a gaban Ubangiji, kowanne kuma ya juya daga muguwar hanyarsa, gama fushi da hasalar da Ubangiji ya furta a kan mutanen nan yana da girma.”
8 So Baruch the sonne of Neriah did according vnto all, that Ieremiah the Prophet commanded him, reading in the booke the wordes of the Lord in the Lords House.
Sai Baruk ɗan Neriya ya yi dukan abin da annabi Irmiya ya ce ya yi; a haikalin Ubangiji kuwa ya karanta maganar Ubangiji daga littafin
9 And in the fift yeere of Iehoiakim the sonne of Iosiah King of Iudah, in the ninth moneth, they proclaimed a fast before the Lord to all the people in Ierusalem, and to all the people that came from the cities of Iudah vnto Ierusalem.
A watan tara na shekara ta biyar ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, an yi shela a yi azumi a gaban Ubangiji ga dukan mutanen Urushalima da waɗanda suka zo daga garuruwan Yahuda.
10 Then read Baruch in the booke the wordes of Ieremiah in the house of the Lord, in the chamber of Gemariah the sonne of Shaphan the secretarie, in the hier court at the entrie of the new gate of the Lordes house, in the hearing of all the people.
Daga ɗakin Gemariya ɗan Shafan magatakarda, wanda yake a fili na bisa a mashigin Sabuwar Ƙofar haikali, Baruk ya karanta wa dukan mutane a haikalin Ubangiji maganar Irmiya daga littafin.
11 When Michaiah the sonne of Gemariah, the sonne of Shaphan had heard out of the booke all the wordes of the Lord,
Sa’ad da Mikahiya ɗan Gemariya, ɗan Shafan, ya ji dukan maganar Ubangiji daga littafin,
12 Then hee went downe to the Kings house into the Chancellours chamber, and loe, all the princes sate there, euen Elishama the Chancellour, and Delaiah the sonne of Shemaiah, and Elnathan the sonne of Achbor, and Gemariah the sonne of Shaphan, and Zedekiah the sonne of Hananiah, and all the princes.
sai ya sauka zuwa ɗakin magatakarda a fada, inda dukan fadawa suke zaune, Elishama magatakarda, Delahiya ɗan Shemahiya, Elnatan ɗan Akbor, Gemariya ɗan Shafan, Zedekiya ɗan Hananiya, da dukan sauran fadawa.
13 Then Michaiah declared vnto them all the wordes that he had heard when Baruch read in the booke in the audience of the people.
Bayan Mikahiya ya faɗa musu kome da ya ji Baruk ya karanta wa mutane daga littafin,
14 Therefore all the princes sent Iehudi the sonne of Nethaniah, the sonne of Shelemiah, the sonne of Chushi, vnto Baruch, saying, Take in thine hande the roule, wherein thou hast read in the audience of the people, and come. So Baruch the sonne of Neriah, tooke the roule in his hand, and came vnto them.
sai dukan fadawan suka aiki Yehudi ɗan Netaniya, ɗan Shelemiya, ɗan Kushi, ya ce wa Baruk, “Ka zo tare da littafin da ka karanta wa mutane.” Saboda haka Baruk ɗan Neriya ya tafi wurinsu tare da littafin a hannunsa.
15 And they saide vnto him, Sit downe now, and reade it, that we may heare. So Baruch read it in their audience.
Suka ce masa, “Zauna, ka karanta mana littafin.” Sai Baruk ya karanta musu littafin.
16 Now when they had heard all the wordes, they were afraid both one and other, and said vnto Baruch, We will certifie the King of all these wordes.
Da suka ji dukan maganar, sai suka dubi juna a firgice suka ce wa Baruk, “Dole mu sanar da dukan maganan nan ga sarki.”
17 And they examined Baruch, saying, Tell vs nowe, howe diddest thou write all these wordes at his mouth?
Sa’an nan suka ce wa Baruk, “Faɗa mana yadda ka yi ka rubuta dukan wannan. Irmiya ne ya yi maka shibtar ta?”
18 Then Baruch answered them, He pronounced all these wordes vnto me with his mouth, and I wrote them with ynke in the booke.
Baruk ya amsa ya ce, “I, shi ne ya faɗa mini dukan wannan magana, na kuwa rubuta su a takarda.”
19 Then saide the princes vnto Baruch, Goe, hide thee, thou and Ieremiah, and let no man knowe where ye be.
Sa’an nan fadawan suka ce wa Baruk, “Kai da Irmiya ku je ku ɓuya. Kada ku bari wani ya san inda kuke.”
20 And they went in to the King to the court, but they layde vp the roule in the chamber of Elishama the Chancellour and tolde the King all the wordes, that he might heare.
Bayan da suka ajiye littafin a ɗakin Elishama magatakarda, sai suka tafi wurin sarki a fili suka sanar da shi kome.
21 So the King sent Iehudi to fet the roule, and he tooke it out of Elishama the Chancellours chamber, and Iehudi read it in the audience of the King, and in the audience of all the princes, which stoode beside the King.
Sai sarki ya aiki Yehudi ya kawo littafin daga ɗakin Elishama magatakarda ya kuma karanta wa sarki da kuma dukan fadawan da suke tsaye kusa da shi.
22 Nowe the King sate in the winter House, in the ninth moneth, and there was a fire burning before him.
A watan tara ne sarki kuwa yana zaune a gidansa na rani, wuta kuwa tana ci a kasko a gabansa.
23 And when Iehudi had read three, or foure sides, hee cut it with the penknife and cast it into the fire, that was on the hearth vntil all the roule was consumed in the fire, that was on the hearth.
Duk sa’ad da Yehudi ya karanta sashi uku ko huɗu na littafin, sai sarkin ya sa wuƙa ya yanke su, ya zuba a wutar da take ci a kasko, da haka ya ƙone dukan littafin.
24 Yet they were not afraide, nor rent their garmets, neither the King, nor any of his seruants, that heard all these wordes.
Sai sarki da dukan masu yin masa hidima waɗanda suke jin maganan nan ba su firgita ba, balle su keta rigunansu.
25 Neuerthelesse, Elnathan, and Delaiah, and Gemariah had besought the King, that he would not burne ye roule: but he would not heare them.
Ko da yake Elnatan, Delahiya da Gemariya sun roƙi sarki kada yă ƙone littafin, bai saurare su ba.
26 But the King commanded Ierahmeel the sonne of Hammelech, and Seraiah the sonne of Azriel, and Shelemiah the sonne of Abdiel, to take Baruch the scribe, and Ieremiah the Prophet, but the Lord hid them.
A maimakon haka, sai sarki ya umarci Yerameyel ɗan sarki, Serahiya ɗan Azriyel da Shelemiya ɗan Abdeyel su kama Baruk marubuci da Irmiya annabi. Amma Ubangiji ya ɓoye su.
27 Then the word of the Lord came to Ieremiah (after that the King had burnt the roule and the words which Baruch wrote at the mouth of Ieremiah) saying,
Bayan sarki ya ƙone littafin da ya ƙunshi maganar da Baruk ya rubuta daga shibtar Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
28 Take thee againe another roule and write in it all ye former words that were in the first roule which Iehoiakim the King of Iudah hath burnt,
“Ka ɗauki wani littafi ka rubuta a kansa dukan maganar da littafi na farin ya ƙunsa, wanda Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone.
29 And thou shalt say to Iehoiakim King of Iudah, Thus saith the Lord, Thou hast burnt this roule, saying, Why hast thou written therein, saying, that the King of Babel shall certainly come and destroye this land, and shall take thence both man and beast?
Ka kuma faɗa wa Yehohiyakim sarkin Yahuda cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka ƙone wancan littafin ka kuma ce, “Don me ka rubuta a cikinsa, cewa lalle sarkin Babilon zai zo ya hallaka wannan ƙasa, zai kashe mutum duk da dabba?”
30 Therefore thus saith the Lord of Iehoiakim King of Iudah, Hee shall haue none to sit vpon the throne of Dauid, and his dead body shall be cast out in the day to the heate, and in the night to the frost.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim sarkin Yahuda. Ba zai kasance da wani wanda zai zauna a kan gadon sarautar Dawuda ba; za a jefar da gawarsa ta sha zafi da rana da dare kuma ta sha matsanancin sanyi.
31 And I will visite him and his seede, and his seruants for their iniquitie, and I will bring vpon them, and vpon the inhabitants of Ierusalem, and vpon the men of Iudah all the euil that I haue pronounced against them: but they would not heare.
Zan hukunta shi da kuma’ya’yansa da masu hidimarsa saboda muguntarsu; zan kawo kowace masifar da na furta a kansu da kuma waɗanda suke zama a Urushalima da na Yahuda, domin sun ƙi su saurara.’”
32 Then tooke Ieremiah another roule, and gaue it Baruch the scribe the sonne of Neriah, which wrote therein at the mouth of Ieremiah all the wordes of the booke which Iehoiakim King of Iudah had burnt in the fire, and there were added besides them many like wordes.
Sai Irmiya ta ɗauko wani littafi ya ba wa Baruk ɗan Neriya marubuci, kuma yayinda Irmiya yake shibtawa, Baruk ya rubuta a littafin dukan maganar da take a littafin da Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone. Ya kuma ƙara ire-iren maganganun nan a kansu.

< Jeremiah 36 >