< Jeremiah 23 >

1 Woe be vnto the pastors that destroy and scatter the sheepe of my pasture, saith the Lord.
“Kaiton makiyayan da suka hallakar suka kuma warwatsar da tumakin makiyayanta!” In ji Ubangiji.
2 Therefore thus saith the Lord God of Israel vnto the pastors that feede my people, Yee haue scattered my flock and thrust them out, and haue not visited them: beholde, I will visite you for the wickednesse of your works, saith the Lord.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana ce wa makiyayan da suke lura da mutanena, “Domin kun watsar da garkena kuka kuma kore su ba ku kuma lura da su ba, zan kawo hukunci a kanku saboda muguntar da kuka yi,” in ji Ubangiji.
3 And I will gather the remnant of my sheepe out of all countreyes, whither I had driuen them, and will bring them againe to their foldes, and they shall growe and encrease.
“Ni kaina zan tattara raguwar garkena daga ƙasashen da na kore su zuwa zan kuma dawo da su ga makiyayansu, inda za su yi ta haihuwa su riɓaɓɓanya.
4 And I will set vp shepheardes ouer them, which shall feede them: and they shall dread no more nor be afraide, neither shall any of them be lacking, saith the Lord.
Zan sa makiyaya a kansu waɗanda za su lura da su, ba za su ƙara jin tsoro ko razana ba, ba kuwa waninsu da zai ɓace,” in ji Ubangiji.
5 Behold, The dayes come, saith the Lord, that I will raise vnto Dauid a righteous branche, and a King shall reigne, and prosper, and shall execute iudgement, and iustice in the earth.
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan tā da wa Dawuda Reshen adalci, Sarki wanda zai yi mulki da hikima ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai a ƙasar.
6 In his dayes Iudah shalbe saued, and Israel shall dwell safely, and this is the Name wherby they shall call him, The Lord our righteousnesse.
A cikin zamaninsa za a ceci Yahuda Isra’ila kuma zai zauna lafiya. Sunan da za a kira shi ke nan, Ubangiji Adalcinmu.
7 Therefore behold, the dayes come, sayth the Lord, that they shall no more say, The Lord liueth, which brought vp the children of Israel out of the lande of Egypt,
“Saboda haka fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da mutanen ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da Isra’ila daga Masar ba,’
8 But the Lord liueth, which brought vp and led the seede of the house of Israel out of the North countrey and from all countryes where I had scattered them, and they shall dwell in their owne lande.
amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da zuriyar Isra’ila daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashen da ya yashe su.’ Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu.”
9 Mine heart breaketh within mee, because of the prophets, all my bones shake: I am like a drunken man (and like a man whome wine hath ouercome) for the presence of the Lord and for his holie wordes.
Game da annabawa kuwa, Zuciyata ta karai; dukan ƙasusuwana suna kaɗuwa. Na zama kamar wanda ya bugu, kamar mutumin da ruwan inabi ya sha kansa, saboda Ubangiji da kuma maganarsa mai tsarki.
10 For the lande is full of adulterers, and because of othes the lande mourneth, the pleasant places of the wildernesse are dried vp, and their course is euill, and their force is not right.
Ƙasar ta cika da mazinata; saboda la’ana ƙasar ta zama kango makiyaya a hamada ta bushe. Annabawa suna bin mugayen muradu suna kuma amfani da ƙarfinsu a hanyar marar kyau.
11 For both the prophet and the Priest doe wickedly: and their wickednesse haue I found in mine House, saith the Lord.
“Annabi da firist dukansu biyu marasa sanin Allah ne; har ma a cikin haikalina na tarar da muguntarsu,” in ji Ubangiji.
12 Wherefore their way shalbe vnto them as slipperie wayes in the darknesse: they shalbe driuen foorth and fall therein: for I will bring a plague vpon them, euen the yeere of their visitation, saith the Lord.
“Saboda haka hanyarsu za tă yi santsi; za a jefar da su cikin duhu a can kuwa za su fāɗi. Zan kawo musu masifa a shekarar da za a hukunta su,” in ji Ubangiji.
13 And I haue seene foolishnesse in the prophets of Samaria, that prophecied in Baal, and caused my people Israel to erre.
“A cikin annabawan Samariya na ga wannan abin banƙyama. Suna annabci ta wurin Ba’al suna ɓad da mutanena Isra’ila.
14 I haue seene also in the prophets of Ierusalem filthines: they commit adulterie and walke in lies: they strengthen also the hands of the wicked that none can returne from his wickednesse: they are all vnto me as Sodom, and the inhabitants thereof as Gomorah.
A cikin annabawan Urushalima kuma na ga wani abin bantsoro. Suna zina suna kuma rayuwar ƙarya. Sun ƙarfafa hannuwa masu aikata mugunta, domin kada wani ya juya daga muguntarsa. Dukansu sun yi kama da Sodom a gare ni; mutanen Urushalima sun yi kama da Gomorra.”
15 Therefore thus saith the Lord of hostes concerning the prophets, Beholde, I will feede them with wormewood, and make them drinke the water of gall: for from the prophets of Ierusalem is wickednesse gone forth into all the lande.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da annabawa, “Zan sa su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwa mai dafi, domin daga annabawan Urushalima rashin sani Allah ya bazu ko’ina a ƙasar.”
16 Thus sayth ye Lord of hosts, Heare not the wordes of the prophets that prophecie vnto you, and teach you vanitie: they speake the vision of their owne heart, and not out of the mouth of the Lord.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Kada ku saurari abin da annabawan suke muku annabci; suna cika ku da sa zuciyar ƙarya. Suna maganar wahayi daga tunaninsu, ba daga bakin Ubangiji ba.
17 They say still vnto them that despise mee, The Lord hath sayde, Ye shall haue peace: and they say vnto euery one that walketh after the stubbernesse of his owne heart, No euill shall come vpon you.
Suna cin gaba da ce wa waɗanda suka rena ni, ‘Ubangiji ya ce za ku zauna lafiya.’ Ga duka waɗanda suke bin taurin zukatansu kuwa sukan ce, ‘Babu lahanin da zai same ku.’
18 For who hath stand in the counsel of the Lord that he hath perceiued and heard his word? Who hath marked his worde and heard it?
Amma wane ne a cikinsu ya taɓa tsaya a majalisar Ubangiji yă ga ko ya ji maganarsa? Wa ya saurari ya kuma ji maganarsa?
19 Beholde, the tempest of the Lord goeth forth in his wrath, and a violent whirlewinde shall fall downe vpon the head of the wicked.
Ga shi, hadarin Ubangiji zai taso cikin hasala guguwa tana kaɗawa a kan kawunan mugaye.
20 The anger of the Lord shall not returne vntill he haue executed, and till he haue perfourmed the thoughts of his heart: in the latter dayes ye shall vnderstande it plainely.
Fushin Ubangiji ba zai kau ba sai ya aikata nufin zuciyarsa. A kwanakin masu zuwa za ku gane sarai.
21 I haue not sent these prophets, sayth the Lord, yet they ranne; I haue not spoken to them, and yet they prophecied.
Ban aiki waɗannan annabawa ba, duk da haka sun tafi da saƙonsu; ban yi musu magana ba, duk da haka sun yi annabci.
22 But if they had stande in my counsell, and had declared my words to my people, then they should haue turned them from their euill way, and from the wickednesse of their inuentions.
Amma da a ce sun tsaya a majalisata, da sun yi shelar maganata ga mutanena sun kuma juyar da su daga mugayen hanyoyinsu da kuma daga mugayen ayyukansu.
23 Am I a God at hande, saith the Lord, and not a God farre off?
“Ni ɗin Allah na kusa ne kawai,” in ji Ubangiji, “ba Allah na nesa ba?
24 Can any hide him selfe in secrete places, that I shall not see him, sayth the Lord? Do not I fill heauen and earth, saieth the Lord?
Akwai wanda zai iya ɓuya a lungu har da ba zan iya ganinsa ba?” In ji Ubangiji “Ban cika sama da ƙasa ba?” In ji Ubangiji.
25 I haue heard what the prophets said, that prophecie lies in my Name, saying, I haue dreamed, I haue dreamed.
“Na ji abin da annabawa suna cewa su da suke annabcin ƙarya a sunana. Suna cewa, ‘Na yi mafarki! Na yi mafarki!’
26 Howe long? Doe the prophets delite to prophecie lies, euen prophecying the deceit of their owne heart?
Har yaushe wannan zai ci gaba a cikin zukata annabawa masu ƙarya, waɗanda suke annabcin ruɗun tunaninsu?
27 Thinke they to cause my people to forget my Name by their dreames, which they tell euery man to his neyghbour, as their forefathers haue forgotten my Name for Baal?
Suna tsammanin mafarkan da suke faɗa wa juna za su sa mutane su manta da sunana, kamar yadda kakanninsu suka manta da sunana ta wurin yin wa Ba’al sujada.
28 The prophet that hath a dreame, let him tell a dreame, and hee that hath my worde, let him speake my worde faithfully: what is the chaffe to the wheate, sayth the Lord?
Bari annabin da ya yi mafarki ya faɗa mafarkinsa, amma bari wanda yake da maganata ya yi ta da aminci. Gama me ya haɗa ciyawa da alkama?” In ji Ubangiji.
29 Is not my word euen like a fire, sayeth the Lord? and like an hammer, that breaketh the stone?
“Maganata ba wuta ba ce,” in ji Ubangiji, “kuma kamar gudumar da kan ragargaza dutse?
30 Therefore beholde, I will come against the prophets, saieth the Lord, that steale my word euerie one from his neighbour.
“Saboda haka,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke satar maganganuna daga juna.
31 Beholde, I will come against the prophets, saith the Lord, which haue sweete tongues, and say, He saith.
I,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke kaɗa harsunansu sa’an nan su ce, ‘Ubangiji ne ya furta.’
32 Beholde, I will come against them that prophecie false dreames, saith the Lord, and doe tell them, and cause my people to erre by their lies, and by their flatteries, and I sent them not, nor commanded them: therefore they bring no profite vnto this people, saith the Lord.
Tabbatacce, ina gāba da waɗannan da suke annabci mafarkan karya,” in ji Ubangiji. “Suna faɗarsu suna ɓad da mutanena da ƙarairayinsu na rashin hankali, duk da haka ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba. Ba su amfani wannan mutane ba ko kaɗan,” in ji Ubangiji.
33 And when this people, or the prophet, or a Priest shall aske thee, saying, What is the burden of the Lord? thou shalt then say vnto them, What burden? I will euen forsake you, saith the Lord.
“Sa’ad da waɗannan mutane, ko annabi ko firist, ya tambaye ka, ‘Mece ce maganarUbangiji?’ Ka ce musu, ‘Wace magana? Zan yashe ku, in ji Ubangiji.’
34 And the prophet, or the Priest, or the people that shall say, The burden of the Lord, I will euen visite euerie such one, and his house.
In annabi ko firist ko da wani dabam ya ce, ‘Wannan ne abin da Ubangiji yake cewa,’ zan hukunta wannan mutum da kuma gidansa.
35 Thus shall yee say euery one to his neighbour, and euerie one to his brother, What hath the Lord answered? and what hath the Lord spoken?
Ga abin da kowannenku yana cin gaba da ce wa abokinsa ko danginsa, ‘Mece ce amsar Ubangiji?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
36 And the burden of the Lord shall yee mention no more: for euery mans worde shall bee his burden: for ye haue peruerted the words of the liuing God, the Lord of hostes our God.
Amma kada ku ƙara ambatar ‘maganar Ubangiji’ domin kowace maganar mutum kan zama maganarsa. Ta haka kukan lalace maganar Allah mai rai, Ubangiji Maɗaukaki, Allahnmu.
37 Thus shalt thou say to the Prophet, What hath the Lord answered thee? and what hath the Lord spoken?
Ga abin da za ku ci gaba da faɗa wa annabi, ‘Mece ce amsar Ubangiji gare ka?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
38 And if you say, The burden of the Lord, Then thus saith the Lord, Because yee say this word, The burden of the Lord, and I haue sent vnto you, saying, Ye shall not say, The burden of the Lord,
Ko da yake kuna cewa, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ga abin da Ubangiji yana cewa kuna amfani da kalmomi, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ko da yake na ce muku kada ku ce, ‘Wannan ce maganar Ubangiji.’
39 Therefore beholde, I, euen I will vtterly forget you, and I will forsake you, and the citie that I gaue you and your fathers, and cast you out of my presence,
Saboda haka, tabbatacce zan manta da ku in kuma jefar da ku daga gabana tare da birnin da na ba ku da kuma kakanninku.
40 And will bring an euerlasting reproche vpon you, and a perpetual shame which shall neuer be forgotten.
Zan kawo muku madawwamiyar kunya, kunya ta har abada wadda ba za a taɓa manta ba.”

< Jeremiah 23 >