< Jeremiah 15 >

1 Then sayde the Lord vnto me, Though Moses and Samuel stoode before mee, yet mine affection coulde not be toward this people: cast them out of my sight, and let them depart.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Ko da Musa da Sama’ila za su tsaya a gabana, zuciyata ba za tă komo ga mutanen nan ba. Ka kore su daga gabana! Su tafi!
2 And if they say vnto thee, Whither shall we depart? then tell them, Thus saith the Lord, Such as are appointed to death, vnto death: and such as are for the sworde, to the sworde: and such as are for the famine, to the famine: and such as are for the captiuitie, to the captiuitie.
In kuma suka tambaye ka, ‘Ina za mu tafi?’ Sai ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Waɗanda aka ƙaddara ga mutuwa, ga mutuwa za su; waɗanda aka ƙaddara ga takobi, ga takobi za su; waɗanda aka ƙaddara ga yunwa, ga yunwa za su; waɗanda aka ƙaddara ga zaman bauta, ga zaman bauta za su.’
3 And I wil appoint ouer them foure kindes, sayth the Lord, the sworde to slay, and the dogs to teare in pieces, and the soules of the heauen, and the beastes of the earth to deuoure, and to destroy.
“Zan aika musu da iri masu hallakarwa guda huɗu,” in ji Ubangiji, “takobi zai kashe, karnuka za su kwashe, tsuntsaye da namun jeji kuma su cinye su kuma hallaka.
4 I will scatter them also in all kingdomes of the earth, because of Manasseh the sonne of Hezekiah King of Iudah, for that which he did in Ierusalem.
Zan sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya saboda abin da Manasse ɗan Hezekiya sarkin Yahuda ya aikata a Urushalima.
5 Who shall then haue pitie vpon thee, O Ierusalem? or who shalbe sorie for thee? or who shall go to pray for thy peace?
“Wa zai ji tausayinki, ya Urushalima? Wa zai yi makoki dominki? Wa zai dakata ya tambayi lafiyarki?
6 Thou hast forsaken me, sayth the Lord, and gone backward: therefore wil I stretch out mine hand against thee, and destroy thee: for I am weary with repenting.
Kin ƙi ni,” in ji Ubangiji. “Ki ci gaba da ja da baya. Ta haka zan ɗibiya hannuwana a kanki in hallaka ki; ba zan ƙara nuna miki jinƙai ba.
7 And I wil scatter them with the fanne in the gates of the earth I haue wasted, and destroyed my people, yet they would not returne from their wayes.
Zan sheƙe ki da abin sheƙewa a ƙofofin birnin ƙasar. Zan kawo baƙin ciki da hallaka a kan mutanena, gama ba su canja hanyoyinsu ba.
8 Their widdowes are increased by mee aboue the sande of the sea: I haue brought vpon them, and against the assembly of the yong men a destroyer at noone day: I haue caused him to fal vpon them, and the citie suddenly, and speedily.
Zan ƙara yawan gwaurayensu su fi yashin teku yawa. Da tsakar rana zan kawo mai hallakarwa a kan iyaye mata na samarinsu; farat ɗaya zan kawo musu wahala da razana.
9 Shee that hath borne seuen, hath bene made weake: her heart hath failed: the sunne hath failed her, whiles it was day: she hath bene confounded, and ashamed, and the residue of them will I deliuer vnto the sworde before their enemies, sayth the Lord.
Mahaifiya’ya’ya bakwai za tă suma ta ja numfashinta na ƙarshe. Ranarta zai fāɗi tun lokacin bai yi ba; za tă sha kunya a kuma wulaƙanta ta. Zan sa a kashe raguwa da takobi a gaban abokan gābansu,” in ji Ubangiji.
10 Wo is mee, my mother, that thou hast borne mee, a contentious man, and a man that striueth with the whole earth I haue neither lent on vsury, nor men haue lent vnto me on vsurie: yet euery one doeth curse me.
Kaitona, mahaifiyata, da kika haife ni, mutumin da dukan ƙasa take faɗa take kuma gardama da shi! Ban ba da bashi ko in ci bashi ba, duk da haka kowa yana zagina.
11 The Lord sayd, Surely thy remnant shall haue wealth: surely I will cause thine enemie to intreate thee in the time of trouble, and in the time of affliction.
Ubangiji ya ce, “Tabbatacce zan cece ka don alheri; tabbatacce zan sa abokan gābanka su yi roƙo gare ka a lokacin masifa da kuma lokacin wahala.
12 Shall the yron breake the yron, and the brasse that commeth from the North?
“Mutum zai iya karye ƙarfe ƙarfe daga arewa, ko tagulla?
13 Thy substance and thy treasures wil I giue to be spoyled without gaine, and that for all thy sinnes euen in all thy borders.
“Dukiyarku da arzikinku zan ba da su ganima, babu tara, saboda duka zunubanku ko’ina a ƙasar.
14 And I wil make thee to go with thine enemies into a land that thou knowest not: for a fire is kindled in mine anger, which shall burne you.
Zan bautar da ku ga abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, gama fushina zai yi ƙuna kamar wuta da za tă yi ƙuna a kanku.”
15 O Lord, thou knowest, remember me, and visite me, and reuenge me of my persecuters: take mee not away in the continuance of thine anger: know that for thy sake I haue suffered rebuke.
Ka gane, ya Ubangiji; ka tuna da ni ka kuma lura da ni. Ka yi mini ramuwa a kan masu tsananta mini. Cikin jimirinka, kada ka ɗauke ni; ka tuna yadda na sha zagi saboda kai.
16 Thy wordes were founde by me, and I did eate them, and thy worde was vnto me the ioy and reioycing of mine heart: for thy Name is called vpon me, O Lord God of hostes.
Sa’ad da maganganunka suka zo, na cinye su; suka zama abin farin ciki zuciyata kuma ta yi murna, gama ana kirana da sunanka, Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki.
17 I sate not in the assembly of the mockers, neither did I reioyce, but sate alone because of thy plague: for thou hast filled me with indignation.
Ban taɓa zauna a cikin’yan tawaye ba, ban taɓa yi murna da su ba; na zauna ni kaɗai domin hannunka yana a kaina ka kuma sa na cika da haushi.
18 Why is mine heauines continuall? and my plague desperate and cannot be healed? why art thou vnto me as a lyar, and as waters that faile?
Me ya sa wahalata ba ta ƙarewa mikina kuma ba ya warkuwa? Za ka zama mini kamar rafi mai yaudara ne, kamar maɓulɓulan da ta kafe ne?
19 Therefore thus saith the Lord, If thou returne, then wil I bring thee againe, and thou shalt stand before me: and if thou take away the precious from the vile, thou shalt be according to my worde: let them returne vnto thee, but returne not thou vnto them.
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “In ka tuba, zan maido da kai don ka bauta mini; in ka ambaci maganganu masu kyau, ba marasa kyau ba, za ka zama kakakina. Bari wannan mutane su juyo gare ka, amma kada ka juye gare su.
20 And I will make thee vnto this people a strong brasen wall, and they shall fight against thee, but they shall not preuaile against thee: for I am with thee to saue thee and to deliuer thee, saith ye Lord.
Zan mai da kai katanga ga wannan mutane, katanga mai ƙarfi na tagulla; za su yi yaƙi da kai amma ba za su yi nasara a kanka ba, gama ina tare da kai don in kuɓutar in kuma cece ka,” in ji Ubangiji.
21 And I will deliuer thee out of the hand of the wicked, and I will redeeme thee out of the hand of the tyrants.
“Zan cece ka daga hannuwan mugaye in ɓamɓare ka daga hannun marasa tausayi.”

< Jeremiah 15 >