< Isaiah 53 >

1 Who will beleeue our report? and to whom is the arme of the Lord reueiled?
Wa ya gaskata saƙonmu kuma ga wa hannun Ubangiji ya bayyana?
2 But hee shall growe vp before him as a branche, and as a roote out of a dry grounde: he hath neither forme nor beautie: when we shall see him, there shall be no forme that wee should desire him.
Ya yi girma kamar dashe marar ƙarfi, kamar saiwa kuma daga ƙeƙasasshiyar ƙasa. Ba shi da kyan gani ko wani makamin da zai ja hankalinmu, babu wani abin da yake da shi da zai sa mu yi sha’awarsa.
3 He is despised and reiected of men: he is a man full of sorowes and hath experience of infirmities: we hidde as it were our faces from him: he was despised and we esteemed him not.
Mutane suka rena shi suka ƙi shi, mutum ne cike da baƙin ciki, ya kuma saba da wahala. Kamar wanda mutane suna ɓuya fuskokinsu daga gare shi aka rena shi aka yi banza da shi.
4 Surely hee hath borne our infirmities, and caried our sorowes: yet wee did iudge him, as plagued, and smitten of God, and humbled.
Tabbatacce ya ɗauki cututtukanmu ya kuma daure da baƙin cikinmu duk da haka muka ɗauka Allah ya hukunta shi ne, ya buge shi ya kuma sa ya sha azaba.
5 But hee was wounded for our transgressions, hee was broken for our iniquities: the chastisement of our peace was vpon him, and with his stripes we are healed.
Amma aka yi masa rauni saboda laifofinmu, aka ƙuje shi saboda kurakuranmu; hukuncin da ya kawo mana salama ya kasance a kansa, kuma ta wurin mikinsa ya sa muka warke.
6 All we like sheepe haue gone astraye: wee haue turned euery one to his owne way, and the Lord hath layed vpon him the iniquitie of vs all.
Dukanmu, muna kama da tumakin da suka ɓata, kowannenmu ya kama hanyarsa; Ubangiji kuwa ya sa hukunci ya auko a kansa hukuncin da ya wajaba a kanmu.
7 Hee was oppressed and he was afflicted, yet did he not open his mouth: hee is brought as a sheepe to the slaughter, and as a sheepe before her shearer is dumme, so he openeth not his mouth.
Aka wulaƙanta shi aka kuma yi masa azaba, duk da haka bai buɗe bakinsa ba; aka kai shi kamar ɗan rago zuwa wurin yanka, kuma kamar tunkiya a gaban masu askinta tana shiru, haka bai buɗe bakinsa ba.
8 Hee was taken out from prison, and from iudgement: and who shall declare his age? for he was cut out of the lande of the liuing: for the transgression of my people was he plagued.
Da wulaƙanci da kuma hukunci aka ɗauke shi aka tafi. Wa kuwa zai yi maganar zuriyarsa? Gama an kawar da shi daga ƙasar masu rai; saboda laifin mutanena aka kashe shi.
9 And he made his graue with the wicked, and with the riche in his death, though hee had done no wickednesse, neither was any deceite in his mouth.
Aka yi jana’izarsa tare da mugaye, aka binne shi tare da masu arziki, ko da yake bai taɓa yin wani tashin hankali ba, ko a sami ƙarya a bakinsa.
10 Yet the Lord would breake him, and make him subiect to infirmities: when hee shall make his soule an offring for sinne, he shall see his seede and shall prolong his dayes, and the will of the Lord shall prosper in his hand.
Duk da haka nufin Ubangiji ne a ƙuje shi yă kuma sa yă sha wahala, kuma ko da yake Ubangiji ya sa ransa ya zama hadaya don zunubi, zai ga zuriyarsa zai kuma kawo masa tsawon rai, nufin Ubangiji kuma zai yi nasara a hannunsa.
11 Hee shall see of the trauaile of his soule, and shall be satisfied: by his knowledge shall my righteous seruant iustifie many: for hee shall beare their iniquities.
Bayan wahalar ransa, zai ga hasken rai, ya kuma gamsu; ta wurin saninsa bawana mai adalci zai’yantar da mutane masu yawa, zai kuma ɗauki laifofinsu.
12 Therefore will I giue him a portion with the great, and he shall deuide the spoyle with the strong, because hee hath powred out his soule vnto death: and he was counted with the transgressers, and he bare the sinne of many, and prayed for the trespassers.
Saboda haka zan ba shi rabo tare da manya, zai kuma raba ganima tare da masu ƙarfi, domin ya ba da ransa har mutuwa, aka kuma lissafta shi tare da masu laifofi. Gama ya ɗauki zunubin mutane masu yawa, ya kuma yi roƙo saboda laifofinsu.

< Isaiah 53 >