< Isaiah 50 >

1 Thus sayeth the Lord, Where is that bill of your mothers diuorcement, whome I haue cast off? or who is the creditour to whome I solde you? Beholde, for your iniquities are yee solde, and because of your transgressions is your mother forsaken.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ina takardar shaida na saki mahaifiyarka daga aure wadda na kora? Ko kuwa ga wanda mutumin da nake bin bashi ne na sayar da kai? Saboda zunubanka aka sayar da kai; saboda laifofinka ne ya sa aka kori mahaifiyarka.
2 Wherefore came I, and there was no man? I called, and none answered: is mine hand so shortened, that it cannot helpe? or haue I no power to deliuer? Beholde, at my rebuke I drie vp the Sea: I make the floods desert: their fish rotteth for want of water, and dieth for thirst.
Sa’ad da na zo, me ya sa babu kowa? Sa’ad da na yi kira, me ya sa babu wani da ya amsa? Hannuna ya kāsa ne sosai don fansarka? Na rasa ƙarfin kuɓutar da kai ne? Ta wurin tsawatawa kawai na busar da teku, na mai da koguna hamada; kifayensu duk sun ruɓe saboda rashin ruwa suka kuma mutu saboda ƙishi.
3 I clothe the heauens with darkenesse, and make a sacke their couering.
Na suturar da sararin sama da duhu na kuma mai da tsummoki abin rufuwarsa.”
4 The Lord God hath giuen me a tongue of the learned, that I shoulde knowe to minister a woord in time to him that is weary: he will raise me vp in the morning: in the morning hee will waken mine eare to heare, as the learned.
Ubangiji Mai Iko Duka ya ba ni harshen umarni, don in san maganar da za tă ƙarfafa gajiyayye. Ya farkar da ni da safe, ya farkar da kunnena don in saurara kamar wanda ake koya masa.
5 The Lord God hath opened mine eare and I was not rebellious, neither turned I backe.
Ubangiji Mai Iko Duka ya buɗe kunnuwana, kuma ban yi tayarwa ba; ban ja da baya ba.
6 I gaue my backe vnto the smiters, and my cheekes to the nippers: I hidde not my face from shame and spitting.
Na ba da bayana ga masu dūkana, kumatuna ga masu jan gemuna; ban ɓoye fuskata daga masu ba’a da masu tofa mini miyau ba.
7 For the Lord God will helpe me, therefore shall I not bee confounded: therefore haue I set my face like a flint, and I knowe that I shall not be ashamed.
Gama Ubangiji Mai Iko Duka zai taimake ni, ba zan sha kunya ba. Saboda haka na kafa fuskata kamar dutsen ƙanƙara, na kuma sani ba zan sha kunya ba.
8 Hee is neere that iustifieth mee: who will contend with me? Let vs stande together: who is mine aduersarie? let him come neere to me.
Gama shi da zai tabbatar da ni, marar laifi ne yana kusa. Wane ne zai kawo ƙararraki game da ni? Bari mu je ɗakin shari’a tare! Wane ne mai zargina? Bari yă kalubalance ni!
9 Beholde, the Lord God will helpe me: who is he that can condemne me? loe, they shall waxe olde as a garment: the mothe shall eate them vp.
Ubangiji Mai Iko Duka ne zai taimake ni. Wane ne zai iya tabbatar da ni mai laifi? Duk za su koɗe kamar riga; asu za su cinye su.
10 Who is among you that feareth the Lord? let him heare the voyce of his seruant: hee that walketh in darkenesse, and hath no light, let him trust in the Name of the Lord, and staye vpon his God.
Wane ne a cikinku yake tsoron Ubangiji yana kuma yin biyayya ga maganar bawansa? Bari wanda yake tafiya cikin duhu, wanda ba shi da haske, ya dogara a sunan Ubangiji ya kuma dogara ga Allahnsa.
11 Beholde, all you kindle a fire, and are compassed about with sparkes: walke in the light of your fire, and in the sparkes that ye haue kindled. This shall ye haue of mine hand: ye shall lye downe in sorowe.
Amma yanzu fa, dukanku waɗanda kuke ƙuna wuta kuna kuma tanada wa kanku fitilu masu ci, ku je ku yi tafiya a cikin hasken wutarku da na fitilun da kuka ƙuna. Abin da za ku karɓa ke nan daga hannuna. Za ku kwanta a cikin azaba.

< Isaiah 50 >