< Isaiah 48 >

1 Hear yee this, O house of Iaakob, which are called by the name of Israel, and are come out of the waters of Iudah: which sweare by the Name of the Lord, and make mention of the God of Israel, but not in truth, nor in righteousnesse.
“Ku kasa kunne ga wannan, ya gidan Yaƙub, waɗanda ake kira da sunan Isra’ila suka kuma fito daga zuriyar Yahuda, ku da kuke yin rantsuwa da sunan Ubangiji kuna kuma kira sunan Allah na Isra’ila, amma ba da gaskiya ko adalci ba,
2 For they are called of the holy citie, and staie themselues vpon the God of Israel, whose Name is the Lord of hostes.
ku da kuke kiran kanku’yan ƙasar birni mai tsarki kuna kuma dogara ga Allah na Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa,
3 I haue declared ye former things of old, and they went out of my mouth, and I shewed them: I did them suddenly, and they came to passe.
na nanata abubuwan da suka riga suka faru tuntuni, bakina ya yi shelar su na kuma sanar da su; sai nan da nan na aikata, suka kuma faru.
4 Because I knewe, that thou art obstinate, and thy necke is an yron sinew, and thy brow brasse,
Gama na san yadda kuke da taurinkai; jijiyoyin wuyanku ƙarafa ne, goshinku tagulla ne.
5 Therefore I haue declared it to thee of old: before it came to passe, I shewed it thee, lest thou shouldest say, Mine idole hath done them, and my carued image, and my molten image hath commanded them.
Saboda haka na faɗa waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na yi shelarsu gare ku saboda kada ku ce, ‘Gumakana ne suka yi su; siffar itacena da allahn zinariyana ne ya ƙaddara su.’
6 Thou hast heard, behold all this, and wil not yee declare it? I haue shewed thee newe things, euen now, and hid things, which thou knewest not.
Kun riga kun ji waɗannan abubuwa; kuka gan su duka. Ba za ku yarda da su ba? “Daga yanzu zuwa gaba zan faɗa muku sababbin abubuwa, na ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.
7 They are created now, and not of olde, and euen before this thou heardest them not, lest thou shouldest say, Beholde, I knewe them.
Yanzu an halicce su, ba da daɗewa ba; ba ku riga kun ji game da su kafin yau ba. Saboda haka ba za ku ce, ‘I, na san da su ba.’
8 Yet thou heardest them not, neither diddest know them, neither yet was thine eare opened of olde: for I knewe that thou wouldest grieuously transgresse: therefore haue I called thee a transgressour from the wombe.
Ba ku ji ko balle ku gane ba; tun da kunnenku bai buɗu ba. Tabbatacce na san yadda kun zama masu tayarwa; an kira ku’yan tawaye daga haihuwa.
9 For my Names sake will I defer my wrath, and for my praise will I refraine it from thee, that I cut thee not off.
Saboda girman sunana na jinkirta fushina; saboda girman yabona na janye shi daga gare ku, don dai kada a yanke ku.
10 Behold, I haue fined thee, but not as siluer: I haue chosen thee in the fornace of affliction.
Duba, na tace ku, ko da yake ba kamar azurfa ba; na gwada ku cikin wutar wahala.
11 For mine owne sake, for mine owne sake wil I doe it: for how should my Name be polluted? surely I wil not giue my glory vnto another.
Saboda girmana, saboda girmana, na yi haka. Yaya zan ƙyale a ƙazantar da kaina? Ba zan raba ɗaukakata da wani ba.
12 Heare me, O Iaakob and Israel, my called, I am, I am the first, and I am the last.
“Ka kasa kunne gare ni, ya Yaƙub, Isra’ila, wanda na kira cewa, Ni ne shi; ni ne na farko ni ne kuma na ƙarshe.
13 Surely mine hand hath laid the foundation of the earth, and my right hand hath spanned the heaues: when I cal them, they stand vp together.
Hannuna ne ya kafa harsashen duniya, hannuna na dama kuma ya shimfiɗa sammai; sa’ad da na kira su, duka suka miƙe tsaye gaba ɗaya.
14 All you, assemble your selues, and heare: which among them hath declared these thinges? The Lord hath loued him: he wil doe his will in Babel, and his arme shalbe against the Chaldeans.
“Ku tattaru, dukanku ku kuma saurara, Wanne a cikin gumakan ya iya faɗa waɗannan abubuwa? Zaɓaɓɓen da Ubangiji yake ƙauna zai aikata nufinsa a kan Babilon; hannunsa zai yi gāba da Babiloniyawa.
15 I, euen I haue spoken it, and I haue called him: I haue brought him, and his way shall prosper.
Ni kaina, na faɗa; I, na kira shi. Zan kawo shi, zai kuma yi nasara a cikin aikinsa.
16 Come neere vnto me: heare ye this: I haue not spoken it in secret from the beginning: from the time that the thing was, I was there, and now the Lord God and his Spirit hath sent me.
“Ku zo kusa da ni ku kuma saurari wannan. “Daga farkon shela ban yi magana a ɓoye ba; a lokacin da ya faru, ina nan a wurin.” Yanzu kuwa Ubangiji Mai Iko Duka ya aiko ni, da Ruhunsa.
17 Thus saith the Lord thy redeemer, the Holy one of Israel, I am the Lord thy God, which teach thee to profite, and lead thee by the way, that thou shouldest goe.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya koya muku abin da ya fi muku kyau, wanda ya muku hanyar da za ku bi.
18 Oh that thou haddest hearkened to my commandements! then had thy prosperitie bene as the floude, and thy righteousnesse as the waues of the sea.
Da a ce kawai za ku mai da hankali ga umarnaina, da salamarku ta zama kamar kogi, adalcinku kamar raƙuman teku.
19 Thy seede also had beene as the sande, and the fruite of thy body like the grauell thereof: his name should not haue bene cut off nor destroied before me.
Da zuriyarku ta zama kamar yashi,’ya’yanku kamar tsabar hatsin da ba a iya ƙidayawa; da ba za a taɓa yanke sunansu balle a hallaka su daga gabana ba.”
20 Goe yee out of Babel: flee yee from the Chaldeans, with a voice of ioy: tel and declare this: shewe it foorth to the ende of the earth: say yee, The Lord hath redeemed his seruant Iaakob.
Ku bar Babilon, ku gudu daga Babiloniyawa! Ku yi shelar wannan da sowa ta farin ciki ku kuma furta shi. Ku aika shi zuwa iyakokin duniya; ku ce, “Ubangiji ya fanshi bawansa Yaƙub.”
21 And they were not thirstie: hee led them through the wildernesse: hee caused the waters to flowe out of the rocke for them: for he claue the rocke, and the water gushed out.
Ba su ji ƙishi ba sa’ad da ya bishe su a cikin hamada; ya sa ruwa ya malalo dominsu daga dutse; ya tsage dutse ruwa kuwa ya kwararo.
22 There is no peace, sayeth the Lord, vnto the wicked.
“Babu salama ga mugaye” in ji Ubangiji.

< Isaiah 48 >