< Hosea 1 >

1 The worde of the Lord that came vnto Hosea the sonne of Beeri, in the daies of Vzziah, Iotham, Ahaz, and Hezekiah Kings of Iudah, and in the daies of Ieroboam the sonne of Ioash king of Israel.
Maganar Ubangiji da ta zo wa Hosiya ɗan Beyeri a zamanin mulkin Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, sarakunan Yahuda, da zamanin mulkin Yerobowam ɗan Yowash sarkin Isra’ila.
2 At the beginning the Lord spake by Hosea, and the Lord said vnto Hosea, Goe, take vnto thee a wife of fornications, and children of fornications: for the lande hath committed great whoredome, departing from the Lord.
Sa’ad da Ubangiji ya fara magana ta wurin Hosiya, Ubangiji ya ce masa, “Ka tafi, ka auro wa kanka mazinaciya da’ya’yan da aka haifa ta hanyar rashin aminci, domin ƙasar tana da laifin mummunan zina ta wurin rabuwa da Ubangiji.”
3 So he went, and tooke Gomer, ye daughter of Diblaim, which conceiued and bare him a sonne.
Saboda haka sai ya auri Gomer’yar Dibilayim, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa namiji.
4 And the Lord said vnto him, Cal his name Izreel: for yet a litle, and I will visite the blood of Izreel vpon the house of Iehu, and will cause to cease the kingdome of the house of Israel.
Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba shi suna Yezireyel, domin ba da daɗewa ba zan hukunta gidan Yehu saboda kisan da aka yi a Yezireyel, zan kuma kawo ƙarshen mulkin Isra’ila.
5 And at that day will I also breake the bowe of Israel in the valley of Izreel.
A wannan rana zan karye ƙarfin Isra’ila a Kwarin Yezireyel.”
6 She conceiued yet againe, and bare a daughter, and God saide vnto him, Call her name Lo-ruhamah: for I will no more haue pitie vpon the house of Israel: but I wil vtterly take them away.
Gomer ta sāke ɗauki ciki ta kuma haifi’ya mace. Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba ta suna, Lo-Ruhama, gama ba zan ƙara nuna wa gidan Isra’ila ƙauna ba, har da zan gafarta musu.
7 Yet I will haue mercie vpon the house of Iudah, and wil saue them by the Lord their God, and wil not saue them by bow, nor by sword nor by battell, by horses, nor by horsemen.
Duk da haka zan nuna ƙauna ga gidan Yahuda; zan kuma cece su, ba da baka, takobi ko yaƙi ba, ko ta wurin dawakai, ko masu hawan dawakai ba, sai ko ta wurin Ubangiji Allahnsu.”
8 Nowe when she had wained Lo-ruhamah, shee conceiued, and bare a sonne.
Bayan ta yaye Lo-Ruhama, sai Gomer ta sāke haifi wani ɗa namiji.
9 Then saide God, Call his name Lo-ammi: for yee are not my people: therefore will I not be yours.
Sai Ubangiji ya ce, “Ka ba shi suna Lo-Ammi, gama ku ba mutanena ba ne, ni kuma ba Allahnku ba ne.
10 Yet the nomber of the children of Israel shall be as the sande of the sea, which can not be measured nor tolde: and in the place where it was saide vnto them, Yee are not my people, it shall be saide vnto them, Yee are the sonnes of the liuing God.
“Duk da haka Isra’ilawa za su zama kamar yashi a bakin teku, da ba za a iya aunawa ko a ƙirga ba. A inda aka ce musu, ‘Ku ba mutanena ba ne,’ za a kira su ‘’ya’yan Allah mai rai.’
11 Then shall the children of Iudah, and the children of Israel be gathered together, and appoint them selues one head, and they shall come vp out of the land: for great is the day of Izreel.
Mutanen Yahuda da mutanen Isra’ila za su sāke haɗu su zama ɗaya, za su kuma naɗa shugaba guda su kuma fita daga ƙasar, gama ranar za tă zama mai girma wa Yezireyel.

< Hosea 1 >