< Hosea 13 >

1 When Ephraim spake, there was trembling: hee exalted him selfe in Israel, but he hath sinned in Baal, and is dead.
Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
2 And nowe they sinne more and more, and haue made them molten images of their siluer, and idoles according to their owne vnderstanding: they were all the woorke of the craftesmen: they say one to another whiles they sacrifice a man, Let them kisse the calues.
Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
3 Therefore they shall bee as the morning cloude, and as the morning dewe that passeth away, as the chaffe that is driuen with a whirlewind out of the floore, and as the smoke that goeth out of the chimney.
Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
4 Yet I am the Lord thy God from the land of Egypt, and thou shalt knowe no God but me: for there is no Sauiour beside me.
“Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
5 I did knowe thee in the wildernesse, in the land of drought.
Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
6 As in their pastures, so were they filled: they were filled, and their heart was exalted: therefore haue they forgotten me.
Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
7 And I wil be vnto them as a very lyon, and as a leopard in the way of Asshur.
Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
8 I will meete them, as a beare that is robbed of her whelpes, and I will breake the kall of their heart, and there will I deuoure them like a lion: the wilde beast shall teare them.
Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
9 O Israel, one hath destroyed thee, but in me is thine helpe.
“An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
10 I am: where is thy King, that shoulde help thee in al thy cities? and thy iudges, of whom thou saidest, Giue me a King, and princes?
Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
11 I gaue thee a King in mine anger, and I tooke him away in my wrath.
Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
12 The iniquitie of Ephraim is bound vp: his sinne is hid.
An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
13 The sorowes of a trauailing woman shall come vpon him: he is an vnwise sonne, els would he not stande still at the time, euen at the breaking forth of the children.
Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
14 I wil redeeme them from the power of the graue: I will deliuer them from death: O death, I wil be thy death: O graue, I will be thy destruction: repentance is hid from mine eyes. (Sheol h7585)
“Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol h7585)
15 Though he grewe vp among his brethren, an East winde shall come, euen the winde of the Lord shall come vp from the wildernesse, and drie vp his veine, and his fountaine shalbe dryed vp: he shall spoyle the treasure of all pleasant vessels.
ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
16 Samaria shalbe desolate: for she hath rebelled against her God: they shall fall by the sworde: their infants shalbe dashed in pieces, and their women with childe shalbe ript.
Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”

< Hosea 13 >