< Hosea 10 >

1 Israel is a emptie vine, yet hath it brought foorth fruite vnto it selfe, and according to the multitude of the fruite thereof he hath increased the altars: according to the goodnesse of their lande they haue made faire images.
Isra’ila kuringa ce mai yaɗuwa; ya fitar da’ya’ya wa kansa. Yayinda’ya’yan suka ƙaru, ya gina ƙarin bagadai; da ƙasarsa ta wadata, ya yi wa keɓaɓɓun duwatsu ado.
2 Their heart is deuided: nowe shall they be founde faultie: he shall breake downe their altars: he shall destroy their images.
Zuciyarsu masu ruɗu ne, yanzu kuwa dole su ɗauki laifinsu. Ubangiji zai rushe bagadansu yă kuma hallaka keɓaɓɓun duwatsunsu.
3 For now they shall say, We haue no King because we feared not the Lord: and what should a King doe to vs?
Sa’an nan za su ce, “Ba mu da sarki domin ba mu girmama Ubangiji ba. Amma ko da ma muna da sarki, me zai yi mana?”
4 They haue spoken woordes, swearing falsly in making a couenant: thus iudgement groweth as wormewoode in the furrowes of the fielde.
Sun yi alkawura masu yawa, suka yi rantsuwar ƙarya da kuma yarjejjeniyoyi; saboda haka ƙararraki suka taso kamar ciyayi masu dafi da aka nome a gona.
5 The inhabitants of Samaria shall feare because of the calfe of Beth-auen: for the people thereof shall mourne ouer it, and the Chemarims thereof, that reioyced on it for the glorie thereof, because it is departed from it.
Mutanen da suke zama a Samariya suna tsoro saboda gunki maraƙin Bet-Awen. Mutanensa za su yi makokinsa, haka ma firistocinsa matsafa, waɗanda suka yi farin ciki a kan darajarsa, don an ɗauke ta daga gare su aka kai ta zaman bauta.
6 It shall bee also brought to Asshur, for a present vnto King Iareb: Ephraim shall receiue shame, and Israel shall be ashamed of his owne counsell.
Za a ɗauke shi a kai Assuriya kamar gandu wa babban sarki. Efraim zai sha kunya; Isra’ila zai sha kunya saboda gumakan itacensa.
7 Of Samaria, the King thereof is destroyed as the some vpon the water.
Samariya da sarkinta za su ɓace kamar kumfa a bisa ruwaye.
8 The hie places also of Auen shall be destroied, euen the sinne of Israel: the thorne and the thistle shall growe vpon their altars, and they shall say to the mountaines, Couer vs, and to the hils, Fall vpon vs.
Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”
9 O Israel, thou hast sinned from the daies of Gibeah: there they stoode: the battell in Gibeah against the children of iniquitie did not touch them.
“Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila, a can kuwa kuka ci gaba. Yaƙi bai cimma masu aikata mugunta a Gibeya ba?
10 It is my desire that I should chastice them, and the people shall be gathered against them, when they shall gather themselues in their two furrowes.
Sa’ad da na ga dama, zan hukunta su; al’ummai za su taru su yi gāba da su don su daure su saboda zunubansu da suka riɓanya.
11 And Ephraim is as an heifer vsed to delite in threshing: but I will passe by her faire necke: I will make Ephraim to ride: Iudah shall plowe, and Iaakob shall breake his cloddes.
Efraim horarriyar karsana ce mai son sussuka; saboda haka zan sa karkiya a kyakkyawan wuyanta. Zan bi da Efraim, Dole Yahuda yă yi noma, dole kuma Yaƙub yă ja garman noma.
12 Sowe to your selues in righteousnes: reape after the measure of mercy: breake vp your fallowe grounde: for it is time to seeke the Lord, till he come and raine righteousnesse vpon you.
Ku shuka wa kanku adalci, ku girbe’ya’yan jinƙai marar ƙarewa, ku kuma nome ƙasar da ba a nome ba; gama lokaci ne na neman Ubangiji, sai ya zo ya zubo adalci a kanku.
13 But you haue plowed wickednesse: ye haue reaped iniquitie: you haue eaten the fruite of lies: because thou didest trust in thine owne waies, and in the multitude of thy strong men,
Amma kun shuka mugunta, kuka girbe mugu kuka ci’ya’yan ruɗu. Domin kun dogara da ƙarfinku da kuma a jarumawanku masu yawa,
14 Therefore shall a tumult arise among thy people, and all thy munitions shall be destroyed, as Shalman destroyed Beth-arbell in the daie of battell: the mother with the children was dashed in pieces.
hayaniyar yaƙi za tă tashi gāba da mutanenku, saboda a ragargaza kagaranku, kamar yadda Shalman ya ragargaza Bet-Arbel a ranar yaƙi, sa’ad da aka fyaɗa uwaye tare da’ya’yansu da ƙasa.
15 So shall Beth-el doe vnto you, because of your malicious wickednes: in a morning shall the King of Israel be destroied.
Haka zai faru da kai, ya Betel, domin muguntarka ta yi yawa. Sa’ad da wannan rana ta zo, za a hallaka sarkin Isra’ila ƙaƙaf.

< Hosea 10 >