< Hebrews 3 >

1 Therefore, holy brethren, partakers of the heauenly vocation, consider the Apostle and high Priest of our profession Christ Iesus:
Saboda haka,’yan’uwa tsarkaka, waɗanda suke da rabo a kiran nan na sama, ku kafa tunaninku a kan Yesu, manzo da kuma babban firist wanda muke shaidawa.
2 Who was faithfull to him that hath appointed him, euen as Moses was in al his house.
Ya yi aminci ga wanda ya naɗa shi, kamar yadda Musa ya yi aminci ga dukan gidan Allah.
3 For this man is counted worthy of more glory then Moses, inasmuch as he which hath builded the house, hath more honour then the house.
An ga Yesu ya cancanci girma fiye da Musa, kamar yadda mai ginin gida ya fi gidan daraja.
4 For euery house is builded of some man, and he that hath built all things, is God.
Gama kowane gida yana da wanda ya gina shi, amma maginin dukan abu Allah ne.
5 Now Moses verely was faithfull in all his house, as a seruant, for a witnesse of the thinges which should be spoken after.
Musa ya yi aminci a matsayin bawa cikin dukan gidan Allah, yana ba da shaida a kan abubuwan da za a faɗa nan gaba.
6 But Christ is as the Sonne, ouer his owne house, whose house we are, if we holde fast that confidence and that reioycing of that hope vnto the ende.
Amma Kiristi mai aminci ne kamar ɗa a gidan Allah. Mu kuwa gidansa ne, in muka tsaya gabanmu gadi da kuma begen da muke taƙama a kai.
7 Wherefore, as the holy Ghost sayth, To day if ye shall heare his voyce,
Kamar dai yadda Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Yau, in kuka ji muryarsa,
8 Harden not your hearts, as in the prouocation, according to the day of the tentation in the wildernes,
kada ku taurare zukatanku, yadda kuka yi a tawayen nan, a lokacin gwaji a hamada,
9 Where your fathers tempted me, prooued me, and sawe my workes fourtie yeeres long.
inda kakanninku suka gwada ni, suka kuma gwada ni, ko da yake a cikin shekaru arba’in sun ga abin da na yi.
10 Wherefore I was grieued with that generation, and sayde, They erre euer in their heart, neither haue they knowen my wayes.
Shi ya sa na yi fushi da wancan zamani, na kuma ce, ‘Kullum zukatansu a karkace suke, ba su kuma san hanyoyina ba.’
11 Therefore I sware in my wrath, If they shall enter into my rest.
Saboda haka na yi rantsuwa a cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
12 Take heede, brethren, least at any time there be in any of you an euill heart, and vnfaithfull, to depart away from the liuing God.
Ku lura fa,’yan’uwa, cewa kada waninku yă kasance da zuciya mai zunubi marar bangaskiya da takan juye daga bin Allah mai rai.
13 But exhort one another dayly, while it is called to day, lest any of you be hardened through the deceitfulnes of sinne.
Sai dai ku ƙarfafa juna kullum, muddin akwai lokacin da ana ce da shi Yau, don kada waninku yă zama mai taurin zuciya ta wurin ruɗun zunubi.
14 For we are made partakers of Christ, if we keepe sure vnto the ende that beginning, wherewith we are vpholden,
Mu masu tarayya ne da Kiristi idan mun riƙe bangaskiyarmu da ƙarfi daga farko har zuwa ƙarshe.
15 So long as it is sayd, To day if ye heare his voyce, harden not your hearts, as in the prouocation.
Kamar yadda aka faɗa cewa, “Yau, in kuka ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a tawayen nan.”
16 For some when they heard, prouoked him to anger: howbeit, not all that came out of Egypt by Moses.
Su wane ne suka ji suka kuma yi tawaye? Ba su ne duk waɗanda Musa ya bi da su daga Masar ba?
17 But with whome was he displeased fourtie yeeres? Was hee not displeased with them that sinned, whose carkeises fell in the wildernes?
Da su wane ne kuwa ya yi fushi har shekaru arba’in? Ba da waɗanda suka yi zunubi, waɗanda suka mutu a hamada ba?
18 And to whom sware he that they should not enter into his rest, but vnto them that obeyed not?
Kuma ga su wane ne Allah ya rantse cewa ba za su taɓa shiga hutunsa ba, in ba ga marasa biyayyan nan ba?
19 So we see that they could not enter in, because of vnbeliefe.
Saboda haka mun ga cewa ba su iya shiga ba, saboda rashin bangaskiyarsu ne.

< Hebrews 3 >