< Habakkuk 3 >

1 A prayer of Habakkuk the Prophet for the ignorances.
Addu’ar annabi Habakkuk. A kan shigiyont.
2 O Lord, I haue heard thy voyce, and was afraide: O Lord, reuiue thy worke in the mids of the people, in the mids of the yeeres make it knowen: in wrath remember mercy.
Ya Ubangiji, na ji irin shaharar da ka yi; na yi al’ajabi game da ayyukanka, ya Ubangiji. Ka maimaita su a kwanakinmu, ka sanar da su a lokacinmu; ka yi jinƙai ko a lokacin da kake fushi.
3 God commeth from Teman, and the holy one from mount Paran, (Selah) His glory couereth the heauens, and the earth is full of his prayse,
Allah ya zo daga Teman, Mai Tsarkin nan daga Dutsen Faran. (Sela) Ɗaukakarsa ta rufe sammai yabonsa kuma ya cika duniya.
4 And his brightnes was as the light: he had hornes comming out of his hands, and there was the hiding of his power.
Darajarsa ta yi kamar fitowar rana; ƙyalƙyali ya wulga daga hannunsa, inda ikonsa yake a ɓoye.
5 Before him went the pestilence, and burning coales went forth before his feete.
Annoba ta sha gabansa; cuta kuma tana bin bayansa.
6 He stoode and measured the earth: he behelde and dissolued the nations and the euerlasting mountaines were broken, and the ancient hilles did bowe: his wayes are euerlasting.
Ya tsaya, ya kuwa girgiza duniya; ya duba, sai ya sa al’ummai suka yi rawan jiki. Tsofaffin duwatsu sun wargaje daɗaɗɗun tuddai kuma suka rurrushe. Hanyoyinsa dawwammamu ne.
7 For his iniquitie I sawe the tentes of Cushan, and the curtaines of the land of Midian did tremble.
Na ga tentin Kushan cikin azaba; wuraren zaman Midiyan cikin damuwa.
8 Was the Lord angry against the riuers? or was thine anger against the floods? or was thy wrath against the sea, that thou diddest ride vpon thine horses? thy charets brought saluation.
Ka ji haushin koguna ne, ya Ubangiji? Ko kuwa ka hasala da rafuffuka ne? Ko ka yi fushi da teku ne sa’ad da ka hau dawakanka da kuma kekunan yaƙinka masu nasara?
9 Thy bowe was manifestly reueiled, and the othes of the tribes were a sure worde, (Selah) thou diddest cleaue the earth with riuers.
Ka ja bakanka, ka nemi a ba ka kibiyoyi masu yawa. (Sela) Ka raba duniya da koguna;
10 The mountaines sawe thee, and they trembled: the streame of the water passed by: the deepe made a noyse, and lift vp his hand on hie.
duwatsu sun gan ka sai suka ƙame. Ruwaye masu hauka sun yi ta fantsamawa; zurfafa suka yi ruri suka tā da raƙuman ruwansu sama.
11 The sunne and moone stood still in their habitation: at the light of thine arrowes they went, and at the bright shining of thy speares.
Rana da wata suka tsaya cik a sammai da ganin kibiyoyinka masu wucewa fyu, da ganin hasken māshinka mai walƙiya.
12 Thou trodest downe the land in anger, and didest thresh the heathen in displeasure.
Cikin hasala ka ratsa duniya cikin fushi kuma ka tattake ƙasashe.
13 Thou wentest foorth for the saluation of thy people, euen for saluation with thine Anointed: thou hast wounded the head of the house of the wicked, and discoueredst the foundations vnto the necke, (Selah)
Ka fito don ka fanshi mutanenka, don ceci shafaffenka. Ka ragargaza shugaban ƙasar mugaye, ka tuɓe shi daga kai har ƙafa. (Sela)
14 Thou didest strike thorowe with his owne staues the heades of his villages: they came out as a whirle winde to scatter me: their reioycing was as to deuoure the poore secretly.
Da māshinsa ka soki kansa sa’ad da jarumawansa suka fito don su tarwatse mu, suna farin ciki sai ka ce masu shirin cinye matalautan da suke a ɓoye.
15 Thou didest walke in the sea with thine horses vpon the heape of great waters.
Ka tattake teku da dawakanka, kana kaɗa manyan ruwaye.
16 When I heard, my bellie trembled: my lippes shooke at the voyce: rottennesse entred into my bones, and I trembled in my selfe, that I might rest in the day of trouble: for whe he commeth vp vnto the people, he shall destroy them.
Na ji sai zuciyata ta buga, leɓunana sun yi rawa da jin murya; ƙasusuwana suka ruɓe, ƙafafuna kuma sun yi rawa. Duk da haka zan jira da haƙuri ga ranar bala’i ta zo a kan al’umman nan mai kawo mana hari.
17 For the figtree shall not flourish, neither shall fruite be in the vines: the labour of the oliue shall faile, and the fieldes shall yeelde no meate: the sheepe shalbe cut off from the folde, and there shalbe no bullocke in the stalles.
Ko da yake itace ɓaure bai tohu ba, ba kuma’ya’ya a kuringar inabi, ko da yake zaitun bai ba da amfani ba, gonaki kuma ba su ba da abinci ba, ko da yake babu tumaki a garke, ba kuma shanu a turaku,
18 But I will reioyce in the Lord: I will ioy in the God of my saluation.
duk da haka zan yi farin ciki da Ubangiji, zan yi murna da Allah Mai Cetona.
19 The Lord God is my strength: hee will make my feete like hindes feete, and he will make me to walke vpon mine hie places. To the chiefe singer on Neginothai.
Ubangiji Mai Iko Duka shi ne ƙarfina; yakan mai da ƙafafuna kamar na barewa, yakan sa in yi tafiya a wurare masu tsayi.

< Habakkuk 3 >