< Genesis 49 >

1 Then Iaakob called his sonnes, and sayde, Gather your selues together, that I may tell you what shall come to you in the last dayes.
Sai Yaƙub ya kira’ya’yansa maza ya ce, “Ku tattaru don in faɗa muku abin da zai faru gare ku, a kwanaki masu zuwa.
2 Gather your selues together, and heare, ye sonnes of Iaakob, and hearken vnto Israel your father.
“Ku tattaru, ku saurara,’ya’yan Yaƙub maza; ku saurari mahaifinku, Isra’ila.
3 Reuben mine eldest sonne, thou art my might, and the beginning of my strength, the excellencie of dignitie, and the excellencie of power:
“Ruben, kai ne ɗan farina, ƙarfina, alamar farko ta ƙarfina, mafi matsayi, kuma mafi iko.
4 Thou wast light as water: thou shalt not be excellent, because thou wentest vp to thy fathers bed: then diddest thou defile my bed, thy dignitie is gone.
Mai tumbatsa kamar ruwa, amma ba za ka ƙara zama mai daraja ba, gama ka hau gadon mahaifinka ka hau kujerata, ka kuma ƙazantar da shi.
5 Simeon and Leui, brethren in euill, the instruments of crueltie are in their habitations.
“Simeyon da Lawi’yan’uwa ne, takubansu makamai ne na tā da hankali.
6 Into their secret let not my soule come: my glory, be not thou ioyned with their assembly: for in their wrath they slew a man, and in their selfe will they digged downe a wall.
Ba zan shiga shawararsu ba, ba zan shiga taronsu ba, gama sun kashe maza cikin fushinsu cikin ganin dama suka kashe bijimai.
7 Cursed be their wrath, for it was fierce, and their rage, for it was cruell: I will deuide them in Iaakob, and scatter them in Israel.
La’ananne ne fushinsu, mai tsanani ne ƙwarai, hasalarsu kuwa, muguwa ce ƙwarai! Zan warwatsa su cikin Yaƙub in kuma daidaita su cikin Isra’ila.
8 Thou Iudah, thy brethre shall praise thee: thine hande shalbe in the necke of thine enemies: thy fathers sonnes shall bowe downe vnto thee.
“Yahuda,’yan’uwanka za su yabe ka; hannuwanka za su kasance a wuyan abokan gābanka,’ya’yan mahaifinka maza za su rusuna maka.
9 Iudah, as a Lions whelpe shalt thou come vp from the spoyle, my sonne. He shall lye downe and couche as a Lion, and as a Lionesse: Who shall stirre him vp?
Kai ɗan zaki ne, ya Yahuda, ka dawo daga farauta, ɗana. Kamar zaki, yakan kwanta a miƙe, kamar zakanya, wa yake da ƙarfin halin tashe shi?
10 The scepter shall not depart from Iudah, nor a Lawegiuer from betweene his feete, vntill Shiloh come, and the people shall be gathered vnto him.
Kursiyi ba zai tashi daga Yahuda ba, ba kuwa sandan mulki daga tsakani ƙafafunsa ba, sai ya zo ga wanda yake mai shi. Biyayyar al’umma kuwa tasa ce.
11 He shall binde his Asse foale vnto ye vine, and his Asses colte vnto the best vine. hee shall wash his garment in wine, and his cloke in the blood of grapes.
Zai daure jakinsa a kuringa, aholakinsa a rassa mafi kyau; zai wanke tufafinsa cikin ruwan inabi rigunansa cikin inabi ja wur kamar jini.
12 His eyes shalbe red with wine, and his teeth white with milke.
Idanunsa za su duhunce fiye da ruwan inabi, haƙorarsa farare kamar madara.
13 Zebulun shall dwell by the sea side, and he shalbe an hauen for shippes: and his border shalbe vnto Zidon.
“Zebulun zai zauna a bakin teku, yă zama tasar jiragen ruwa; iyakarsa za tă nausa zuwa Sidon.
14 Issachar shalbe a strong asse, couching downe betweene two burdens:
“Issakar doki mai ƙarfi, kwance tsakanin buhunan sirdi.
15 And he shall see that rest is good, and that the land is pleasant, and he shall bow his shoulder to beare, and shalbe subiect vnto tribute.
Sa’ad da ya ga yadda wurin hutunsa yana da kyau da kuma daɗin da ƙasarsa take, zan tanƙware kafaɗarsa ga nauyi yă miƙa kai ga aikin dole.
16 Dan shall iudge his people as one of the tribes of Israel.
“Dan zai tanada adalci wa mutanensa kamar ɗaya cikin kabilan Isra’ila.
17 Dan shall be a serpent by the way, an adder by the path, byting the horse heeles, so that his rider shall fall backward.
Dan zai zama maciji a gefen hanya, kububuwa a bakin hanya, da take saran ɗiɗɗigen doki domin mahayinsa yă fāɗi da baya.
18 O Lord, I haue waited for thy saluation.
“Ina zuba ido ga cetonka, ya Ubangiji.
19 Gad, an hoste of men shall ouercome him, but he shall ouercome at the last.
“Masu fashi za su fāɗa wa Gad, amma zai runtume su.
20 Concerning Asher, his bread shalbe fat, and he shall giue pleasures for a king.
“Abincin Asher zai zama a wadace, zai yi tanadin abinci iri-iri da suka dace don sarki.
21 Naphtali shalbe a hinde let goe, giuing goodly wordes.
“Naftali sakakkiyar barewa ce da take haihuwar kyawawan’ya’ya.
22 Ioseph shalbe a fruitefull bough, euen a fruitful bough by the well side: the small boughs shall runne vpon the wall.
“Yusuf kuringa ce mai ba da amfani. Kuringa mai ba da amfani kusa da rafi wadda rassanta na hawan bango.
23 And the archers grieued him, and shotte against him and hated him.
Da ɗaci rai mahara suka fāɗa masa; suka harbe shi babu tausayi.
24 But his bowe abode strong, and the hands of his armes were strengthened, by the handes of the mighty God of Iaakob, of whom was the feeder appointed, by the stone of Israel,
Amma bakansa yana nan daram hannuwansa masu ƙarfi ba sa jijjiguwa saboda hannun Maɗaukaki na Yaƙub, saboda Makiyayi, Dutsen Isra’ila,
25 Euen by the God of thy father, who shall helpe thee, and by the almightie, who shall blesse thee with heauenly blessinges from aboue, with blessings of the deepe, that lyeth beneath, with blessings of the brestes, and of the wombe.
saboda Allah na mahaifinka, wanda ya taimake ka, saboda Maɗaukaki, wanda yake albarkace ka da albarkar sama da take bisa albarkun zurfafa da suke ƙarƙashin ƙasa albarkun mama da kuma mahaifa.
26 The blessings of thy father shalbe stronger then the blessings of mine elders: vnto the ende of the hilles of the worlde they shall be on the head of Ioseph, and on the top of the head of him that was separate from his brethren.
Albarkun mahaifi suna da girma fiye da albarkun daɗaɗɗun duwatsu fiye da yalwar madawwaman tuddai. Bari dukan waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin ɗan sarki a cikin’yan’uwansa.
27 Beniamin shall rauine as a wolfe: in the morning he shall deuoure the pray, and at night he shall deuide the spoyle.
“Benyamin kyarkeci ne mai kisa; da safe yakan cinye abin da ya farauto da yamma yakan raba ganima.”
28 All these are the twelue tribes of Israel, and thus their father spake vnto them, and blessed them: euery one of them blessed hee with a seuerall blessing.
Dukan waɗannan su ne kabilu goma sha biyu na Isra’ila, kuma abin da mahaifinsu ya faɗa musu ke nan sa’ad da ya albarkace su, yana ba kowane albarkar da ta dace da shi.
29 And he charged them and sayd vnto them, I am ready to be gathered vnto my people: burie mee with my fathers in the caue, that is in the fielde of Ephron the Hittite,
Sa’an nan ya ba su waɗannan umarnai ya ce, “Ina gab da a tara ni ga mutanena. Ku binne ni tare da kakannina a kogon da yake cikin filin Efron mutumin Hitti,
30 In the caue that is in the field of Machpelah besides Mamre in the land of Canaan: which caue Abraham bought with the fielde of Ephron the Hittite for a possession to burie in.
kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre a Kan’ana, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, yă zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
31 There they buried Abraham and Sarah his wife: there they buryed Izhak and Rebekah his wife: and there I buried Leah.
A can aka binne Ibrahim da matarsa Saratu, a can aka binne Ishaku da matarsa Rebeka, a can kuma na binne Liyatu.
32 The purchase of the fielde and the caue that is therein, was bought of the children of Heth.
Filin tare da kogon da yake ciki, an saya daga Hittiyawa.”
33 Thus Iaakob made an end of giuing charge to his sonnes, and plucked vp his feete into the bed and gaue vp the ghost, and was gathered to his people.
Sa’ad da Yaƙub ya gama ba da umarnan ga’ya’yansa maza, sai ya ɗaga ƙafafunsa zuwa gado, ya ja numfashinsa na ƙarshe, aka kuwa tara shi ga mutanensa.

< Genesis 49 >