< Genesis 33 >

1 And as Iaakob lift vp his eyes, and looked, behold, Esau came, and with him foure hundreth men: and he deuided the children to Leah, and to Rahel, and to the two maides.
Yaƙub ya ɗaga ido ke nan, sai ga Isuwa yana zuwa tare da mutanensa ɗari huɗu; saboda haka sai ya rarraba’ya’yan wa Liyatu, Rahila da kuma matan nan biyu masu hidima.
2 And he put the maides, and their children formost, and Leah, and her children after, and Rahel, and Ioseph hindermost.
Ya sa matan nan biyu masu hidima da’ya’yansu a gaba, Liyatu da’ya’yanta biye, sa’an nan Rahila da Yusuf a baya.
3 So he went before them and bowed him selfe to the ground seuen times, vntill he came neere to his brother.
Shi kansa ya sha gabansu, ya rusuna har ƙasa sau bakwai, kafin ya kai kusa da inda ɗan’uwansa Isuwa yake.
4 Then Esau ranne to meete him, and embraced him, and fell on his necke, and kissed him, and they wept.
Amma Isuwa ya ruga a guje ya sadu da Yaƙub ya rungume shi; ya faɗa a wuyansa ya sumbace shi. Suka kuma yi kuka.
5 And he lift vp his eyes, and sawe the women, and the children, and saide, Who are these with thee? And he answered, They are ye childre whome God of his grace hath giuen thy seruant.
Sa’an nan Isuwa ya ɗaga ido ya ga mata da’ya’ya. Ya yi tambaya, “Su wane ne waɗannan tare da kai?” Yaƙub ya amsa, “Su ne’ya’yan da Allah cikin alheri ya ba bawanka.”
6 Then came the maides neere, they, and their children, and bowed themselues.
Sai matan nan biyu masu hidima da’ya’yansu suka matso kusa suka durƙusa.
7 Leah also with her children came neere and made obeysance: and after Ioseph and Rahel drew neere, and did reuerence.
Biye da su, Liyatu da’ya’yanta suka zo suka rusuna. A ƙarshe duka, sai Yusuf da Rahila suka zo, su ma suka rusuna.
8 Then he said, What meanest thou by all this droue, which I met? Who answered, I haue sent it, that I may finde fauour in the sight of my lorde:
Isuwa ya yi tambaya, “Me kake nufi da dukan abubuwan nan da na sadu da su ana korarsu?” Sai Yaƙub ya ce, “Don in sami tagomashi a idanunka ne, ranka yă daɗe.”
9 And Esau said, I haue ynough, my brother: keepe that thou hast to thy selfe.
Amma Isuwa ya ce, “Na riga na sami abin da ya ishe ni, ɗan’uwana. Riƙe abin da kake da shi don kanka.”
10 But Iaakob answered, Nay, I pray thee: if I haue found grace nowe in thy sight, then receiue my present at mine hande: for I haue seene thy face, as though I had seene the face of God, because thou hast accepted me.
Sai Yaƙub ya ce, “A’a, ina roƙonka, in na sami tagomashi a idanunka, sai ka karɓi wannan kyautai daga gare ni. Gama ganin fuskarka kamar ganin fuskar Allah ne, yanzu da ka karɓe ni da farin ciki.
11 I pray thee take my blessing, that is brought thee: for God hath had mercie on me, and therefore I haue all things: so he compelled him, and he tooke it.
Ina roƙonka ka karɓi kyautar da aka kawo maka, gama Allah ya yi mini alheri kuma ina da kome da nake bukata.” Ganin yadda Yaƙub ya nace, sai Isuwa ya karɓa.
12 And he saide, Let vs take our iourney and go, and I will goe before thee.
Sa’an nan Isuwa ya ce, “Bari mu tafi, zan yi maka rakiya.”
13 Then he answered him, My lord knoweth, that the children are tender, and the ewes and kine with yong vnder mine hande: and if they should ouerdriue them one day, all the flocke would die.
Amma Yaƙub ya ce masa, “Ranka yă daɗe, ka san cewa’ya’yan ƙanana ne, dole in lura da tumaki da shanun da suke shayar da jariransu. In aka kore su da gaggawa a rana guda kaɗai, dukan dabbobin za su mutu.
14 Let now my lord go before his seruant, and I will driue softly, according to ye pase of ye cattel, which is before me, and as the children be able to endure, vntill I come to my lord vnto Seir.
Saboda haka bari ranka yă daɗe yă sha gaban bawansa, ni kuma in tafi a hankali bisa ga saurin abin da ake kora a gabana da kuma saurin’ya’yan, sai na iso wurinka ranka yă daɗe, a Seyir.”
15 Then Esau said, I will leaue then some of my folke with thee. And he answered, what needeth this? let me finde grace in the sight of my lorde.
Sai Isuwa ya ce, “To, bari in bar waɗansu mutanena tare da kai.” Yaƙub ya ce, “Amma me ya sa za ka yi haka? Bari dai in sami tagomashi a idanunka ranka yă daɗe.”
16 So Esau returned, and went his way that same day vnto Seir.
Saboda haka a wannan rana Isuwa ya kama hanyar komawa zuwa Seyir.
17 And Iaakob went forwarde towarde Succoth, and built him an house, and made boothes for his cattell: therefore he called the name of the place Succoth.
Yaƙub kuwa, ya tafi Sukkot, inda ya gina wuri domin kansa, ya kuma yi bukkoki domin dabbobinsa. Shi ya sa aka kira wurin Sukkot.
18 Afterward, Iaakob came safe to Sheche a citie, which is in the lande of Canaan, when he came from Padan Aram, and pitched before the citie.
Bayan Yaƙub ya zo daga Faddan Aram, ya iso lafiya a birnin Shekem a Kan’ana, ya kuma kafa sansani a ƙofar birni.
19 And there he bought a parcell of ground, where hee pitched his tent, at the hande of the sonnes of Hamor Shechems father, for an hundreth pieces of money.
Ya sayi fili daga’ya’yan Hamor maza, mahaifin Shekem inda ya kafa tentinsa, a bakin azurfa ɗari.
20 And he set vp there an altar, and called it, The mightie God of Israel.
A can ya kafa bagade ya kuma kira shi El Elohe Isra’ila.

< Genesis 33 >