< Genesis 27 >

1 And when Izhak was olde, and his eyes were dimme (so that he coulde not see) he called Esau his eldest sonne, and sayde vnto him, My sonne. And he answered him, I am here.
Sa’ad da Ishaku ya tsufa idanunsa suka raunana har ba ya iya gani, sai ya kira Isuwa babban ɗansa ya ce masa, “Ɗana.” Isuwa kuwa ya amsa, ya ce “Ga ni.”
2 Then he sayd, Beholde, I am nowe olde, and knowe not the day of my death:
Ishaku ya ce, “Yanzu na tsufa kuma ban san ranar mutuwata ba.
3 Wherefore nowe, I pray thee take thine instruments, thy quiuer and thy bowe, and get thee to the fielde, that thou mayest take mee some venison.
Saboda haka yanzu, ka ɗauki makamanka, kwari da bakanka, ka tafi jeji ka farauto mini nama.
4 Then make mee sauourie meate, such as I loue, and bring it me that I may eat, and that my soule may blesse thee, before I die.
Ka shirya mini irin abinci mai daɗin da nake so, ka kawo mini in ci, domin in sa maka albarka kafin in mutu.”
5 (Nowe Rebekah heard, when Izhak spake to Esau his sonne) and Esau went into the fielde to hunt for venison, and to bring it.
Ashe, Rebeka tana ji sa’ad da Ishaku ya yi wa ɗansa Isuwa magana. Da Isuwa ya tafi jeji don yă farauto nama yă kawo,
6 Then Rebekah spake vnto Iaakob her sonne, saying, Beholde, I haue heard thy father talking with Esau thy brother, saying,
sai Rebeka ta ce wa ɗanta Yaƙub, “Ka ji nan, na ji mahaifinka ya ce wa ɗan’uwanka Isuwa,
7 Bring mee vension, and make mee sauourie meate, that I may eate and blesse thee before the Lord, afore my death.
‘Kawo mini nama ka shirya mini abinci mai daɗi don in ci, in sa maka albarka a gaban Ubangiji kafin in mutu.’
8 Nowe therefore, my sonne, heare my voyce in that which I command thee.
Saboda haka ɗana, ka saurara da kyau ka kuma yi abin da na faɗa maka.
9 Get thee nowe to the flocke, and bring me thence two good kids of the goates, that I may make pleasant meate of them for thy father, such as he loueth.
Je garke ka kawo mini awaki biyu kyawawa, domin in shirya abinci mai daɗi wa mahaifinka, kamar yadda dai yake so.
10 Then shalt thou bring it to thy father, and he shall eate, to the intent that he may blesse thee before his death.
Sa’an nan ka kai wa mahaifinka yă ci, domin yă sa maka albarka kafin yă mutu.”
11 But Iaakob sayde to Rebekah his mother, Beholde, Esau my brother is rough, and I am smoothe.
Yaƙub ya ce wa mahaifiyarsa Rebeka, “Amma ɗan’uwana Isuwa mutum ne mai gashi a jiki, ni kuma jikina sumul yake.
12 My father may possibly feele me, and I shall seem to him to be a mocker: so shall I bring a curse vpon me, and not a blessing.
A ce baba ya tattaɓa ni fa? Zai zama kamar ina ruɗunsa ne, wannan fa zai jawo mini la’ana a maimakon albarka.”
13 But his mother sayd vnto him, vpon me be thy curse, my sonne: onely heare my voyce, and go and bring me them.
Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, bari la’anar tă fāɗo a kaina. Kai dai yi abin da na faɗa, jeka ka kawo mini su.”
14 So he went and set them, and brought them to his mother: and his mother made pleasant meat, such as his father loued.
Sai ya tafi ya kamo su, ya kawo wa mahaifiyarsa, ta kuwa shirya abinci mai daɗi, yadda mahaifinsa yake so.
15 And Rebekah tooke faire clothes of her elder sonne Esau, which were in her house, and clothed Iaakob her yonger sonne:
Sa’an nan Rebeka ta ɗauki riguna mafi kyau na Isuwa babban ɗanta, waɗanda take da su a gida ta sa wa ƙaramin ɗanta Yaƙub.
16 And she couered his hands and the smoothe of his necke with the skinnes of the kiddes of the goates.
Sai ta mamanne gashin awakin nan biyu a hannuwansa da bayan wuyarsa wanda ba gashi.
17 Afterward she put the pleasant meate and bread, which she had prepared, in the hand of her sonne Iaakob.
Sa’an nan ta ba wa ɗanta Yaƙub abinci mai daɗi da kuma burodin da ta yi.
18 And when he came to his father, he sayd, My father. Who answered, I am here: who art thou, my sonne?
Shi kuwa ya tafi wurin mahaifinsa ya ce, “Babana.” Shi kuma ya amsa “I, ɗana, wane ne?”
19 And Iaakob sayde to his father, I am Esau thy first borne, I haue done as thou badest me, arise, I pray thee: sit vp and eate of my venison, that thy soule may blesse me.
Yaƙub ya ce wa mahaifinsa, “Ni ne Isuwa ɗan farinka. Na yi yadda ka faɗa mini. Ina roƙonka tashi ka zauna ka ci naman, domin ka sa mini albarkarka.”
20 Then Izhak said vnto his sonne, Howe hast thou founde it so quickly my sonne? Who sayde, Because the Lord thy God brought it to mine hande.
Ishaku ya tambayi ɗansa, “Yaya aka yi ka samo shi da sauri haka, ɗana?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Ubangiji Allahnka ne ya ba ni nasara.”
21 Againe sayde Izhak vnto Iaakob, Come neere nowe, that I may feele thee, my sonne, whether thou be that my sonne Esau or not.
Sai Ishaku ya ce wa Yaƙub, “Zo kusa don in taɓa ka, ɗana, domin in sani ko tabbatacce kai ne ɗana Isuwa ko babu.”
22 Then Iaakob came neere to Izhak his father, and he felt him and sayd, The voyce is Iaakobs voyce, but the hands are the hands of Esau.
Yaƙub kuwa ya matsa kusa da mahaifinsa Ishaku, wanda ya tattaɓa shi, sa’an nan ya ce, “Muryan nan dai, muryar Yaƙub ce, amma hannuwan, hannuwan Isuwa ne.”
23 (For he knewe him not, because his hands were rough as his brother Esaus hands: wherefore he blessed him)
Bai gane shi ba, gama hannuwansa suna da gashi kamar na ɗan’uwansa Isuwa, saboda haka ya albarkace shi.
24 Againe he sayd, Art thou that my sonne Esau? Who answered, Yea.
Ya tambaya, “Tabbatacce kai ne ɗana Isuwa?” Ya amsa ya ce “Ni ne.”
25 Then said he, Bring it me hither, and I will eate of my sonnes venison, that my soule may blesse thee. And he brought it to him, and he ate: also he brought him wine, and he dranke.
Sa’an nan ya ce, “Ɗana, kawo mini naman da ka farauto in ci, domin in sa maka albarka.” Yaƙub ya kawo masa ya kuwa ci; ya kuma kawo masa ruwan inabi ya kuma sha.
26 Afterward his father Izhak sayd vnto him, Come neere nowe, and kisse me, my sonne.
Sa’an nan mahaifinsa Ishaku ya ce masa, “Zo nan, ɗana ka sumbace ni.”
27 And hee came neere and kissed him. Then he smellled the sauour of his garmentes, and blessed him, and sayde, Behold, the smelll of my sonne is as the smelll of a fielde, which the Lord hath blessed.
Saboda haka ya je gunsa ya sumbace shi. Sa’ad da Ishaku ya ji ƙanshin rigunansa, sai ya sa masa albarka ya ce, “Aha, ƙanshin ɗana yana kama da ƙanshin jejin da Ubangiji ya sa wa albarka ne.
28 God giue thee therefore of the dewe of heauen, and the fatnesse of the earth, and plentie of wheate and wine.
Allah yă ba ka daga raɓar sama da kuma yalwar ƙasa, yalwar hatsi da sabon ruwan inabi.
29 Let people bee thy seruantes, and nations bowe vnto thee: be Lord ouer thy brethren, and let thy mothers children honour thee. cursed be he that curseth thee, and blessed be he that blesseth thee.
Bari al’ummai su bauta maka mutane kuma su rusuna maka. Ka zama shugaba a kan’yan’uwanka bari kuma’ya’yan mahaifiyarka su rusuna maka. Bari waɗanda suka la’anta ka, su la’antu; waɗanda kuma suka sa maka albarka, su sami albarka.”
30 And when Izhak had made an ende of blessing Iaakob, and Iaakob was scarce gone out from the presence of Izhak his father, then came Esau his brother from his hunting,
Bayan Ishaku ya gama sa masa albarka, Yaƙub yana fita daga mahaifinsa ke nan, sai ga ɗan’uwansa Isuwa ya dawo daga farauta.
31 And hee also prepared sauourie meate and brought it to his father, and sayd vnto his father, Let my father arise, and eat of his sonnes venison, that thy soule may blesse me.
Shi ma ya shirya abinci mai daɗi ya kawo wa mahaifinsa. Sa’an nan ya ce masa, “Babana, tashi ka zauna ka ci daga abin da na farauto, domin ka sa mini albarka.”
32 But his father Izhak sayde vnto him, Who art thou? And he answered, I am thy sonne, euen thy first borne Esau.
Mahaifinsa Ishaku ya tambaye shi, “Wane ne kai?” Ya amsa, “Ni ne ɗanka, ɗan farinka, Isuwa.”
33 Then Izhak was stricken with a marueilous great feare, and sayde, Who and where is hee that hunted venison, and brought it mee, and I haue eate of all before thou camest? and I haue blessed him, therefore he shalbe blessed.
Ishaku ya yi makyarkyata ƙwarai ya ce, “To, wane ne wannan da ya farauto nama ya kawo mini kafin ka zo, har na ci na kuma sa masa albarka? Tabbatacce zai zama mai albarka!”
34 When Esau heard the wordes of his father, he cryed out with a great crye and bitter, out of measure, and sayde vnto his father, Blesse me, euen me also, my father.
Sa’ad da Isuwa ya ji kalmomin mahaifinsa, sai ya fashe da kuka mai zafi kuma da ƙarfi, ya ce wa mahaifinsa, “Ka albarkace ni, ni ma, baba!”
35 Who answered, Thy brother came with subtiltie, and hath taken away thy blessing.
Amma ya ce, “Ɗan’uwanka ya zo da makirci ya karɓi albarkarka.”
36 Then he sayde, Was hee not iustly called Iaakob? for hee hath deceiued mee these two times: he tooke my birthright, and loe, nowe hath he taken my blessing. Also he sayd, Hast thou not reserued a blessing for me?
Isuwa ya ce, “Ba saboda haka ne aka raɗa masa suna Yaƙub ba? Ya yi mini ƙwace sau biyu ke nan; ya ƙwace mini matsayina na ɗan fari, ga shi yanzu kuma ya karɓi albarkata.” Sa’an nan ya yi tambaya, “Ba sauran albarkar da ka rage mini?”
37 Then Izhak answered, and sayd vnto Esau, Beholde, I haue made him thy lorde, and all his brethre haue I made his seruants: also with wheate and wine haue I furnished him, and vnto thee now what shall I doe, my sonne?
Ishaku ya amsa wa Isuwa, “Na mai da shi shugaba a kanka, na sa dukan dangoginsa su zama bayinsa, na kuma ba shi hatsi da sabon ruwan inabi. Saboda haka me kuma zan yi maka ɗana?”
38 Then Esau sayde vnto his father, Hast thou but one blessing my father? blesse mee, euen me also, my father: and Esau lifted vp his voyce, and wept.
Isuwa ya ce wa mahaifinsa, “Iyakar albarkar da kake da ita ke nan, baba? Ka albarkace ni ni ma, baba!” Sai Isuwa ya ɗaga murya ya yi kuka.
39 Then Izhak his father answered, and sayde vnto him, Behold, the fatnesse of the earth shall be thy dwelling place, and thou shalt haue of the dewe of heauen from aboue.
Mahaifinsa Ishaku ya amsa masa ya ce, “Ga shi, ni’imar ƙasar za tă nisanci mazauninka. Raɓar samaniya can ƙwanƙoli za tă nisance ka.
40 And by thy sword shalt thou liue, and shalt be thy brothers seruant. But it shall come to passe, when thou shalt get the masterie, that thou shalt breake his yoke from thy necke.
Za ka rayu ta wurin takobi za ka kuwa bauta wa ɗan’uwanka. Amma sa’ad da ka ɓalle, za ka kakkarye karkiyarsa daga wuyanka.”
41 Therefore Esau hated Iaakob, because of the blessing, wherewith his father blessed him. And Esau thought in his minde, The dayes of mourning for my father will come shortly, then I will slay may brother Iaakob.
Isuwa ya riƙe Yaƙub a zuciya saboda albarkar da mahaifinsa ya sa masa. Ya ce wa kansa, “Kwanakin mutuwar mahaifina sun yi kusa; sa’an nan zan kashe ɗan’uwana Yaƙub.”
42 And it was told to Rebekah of the wordes of Esau her elder sonne, and shee sent and called Iaakob her yonger sonne, and sayd vnto him, Beholde, thy brother Esau is comforted against thee, meaning to kill thee:
Sa’ad da aka faɗa wa Rebeka abin da babban ɗanta Isuwa ya faɗa, sai ta kira ɗanta Yaƙub ta ce masa, “Ɗan’uwanka Isuwa yana ta’azantar da kansa da tunanin kashe ka.
43 Now therefore my sonne, heare my voyce, arise, and flee thou to Haran to my brother Laban,
To, fa, ɗana, yi abin da na ce; gudu nan take zuwa wurin ɗan’uwana Laban a Haran.
44 And tarie with him a while vntill thy brothers fiercenesse be swaged,
Zauna tare da shi na ɗan lokaci sai ɗan’uwanka ya huce.
45 And till thy brothers wrath turne away from thee, and hee forget the thinges, which thou hast done to him: then will I sende and take thee from thence: why shoulde I bee depriued of you both in one day?
Sa’ad da ɗan’uwanka ya daina fushi da kai, ya kuma manta da abin da ka yi masa, zan aika don ka dawo daga can. Don me zan rasa ku biyu a rana guda?”
46 Also Rebekah said to Izhak, I am weary of my life, for the daughters of Heth. If Iaakob take a wife of the daughters of Heth like these of the daughters of the lande, what auaileth it me to liue?
Sa’an nan Rebeka ta ce wa Ishaku, “Ni fa na gaji da matan Hittiyawan nan. In Yaƙub ya auri mata daga cikin matan ƙasan nan, wato, daga matan Hittiyawa irin waɗannan, rayuwata ba za tă daɗa mini kome ba.”

< Genesis 27 >