< Ezra 10 >

1 Whiles Ezra prayed thus, and confessed himselfe weeping, and falling downe before the house of God, there assembled vnto him of Israel a very great Congregation of men and women and children: for the people wept with a great lamentation.
Yayinda Ezra yake addu’a, yake kuma furta laifi, yana kuka, yana a durƙushe da kansa ƙasa a gaban gidan Allah, sai babban taron jama’ar Isra’ilawa, maza, mata da yara, suka taru a wurinsa. Su ma suka yi kuka mai zafi.
2 Then Shechaniah the sonne of Iehiel one of the sonnes of Elam answered, and sayd to Ezra, We haue trespassed against our God, and haue taken strange wiues of the people of the land, yet nowe there is hope in Israel concerning this.
Sai Shekaniya ɗan Yehiyel, daga zuriyar Elam ya ce wa Ezra, “Mun yi wa Allah rashin aminci ta wurin yin auratayya da maƙwabtanmu, amma duk da haka bai yashe mutanen Isra’ila ba.
3 Now therfore let vs make a couenant with our God, to put away all the wiues (and such as are borne of them) according to the counsell of the Lord, and of those that feare the commandements of our God, and let it be done according to the Lawe.
Yanzu bari mu yi alkawari da Allahnmu, mu kori matan da yaransu bisa ga abin da ranka yă daɗe da sauran shugabannin da kuke girmama umarnin Allah kuka shawarce mu, bari mu yi haka bisa ga doka.
4 Arise: for the matter belogeth vnto thee: we also wil be with thee: be of comfort and do it.
Sai ka tashi, gama wannan hakkinka ne, za mu ba ka goyon baya. Saboda haka ka yi ƙarfin hali ka aikata shi.”
5 Then arose Ezra, and caused the chiefe Priestes, the Leuites, and all Israel, to sweare that they would doe according to this worde. So they sware.
Sai Ezra ya tashi ya sa firistoci da suke shugabanni, da Lawiyawa, da dukan mutanen Isra’ila su rantse, cewa za su yi abin da aka ce. Sai suka yi rantsuwar.
6 And Ezra rose vp from before the house of God, and went into the chamber of Iohanan the sonne of Eliashib: he went euen thither, but he did eate neither bread, nor drunke water: for he mourned, because of the transgression of them of the captiuitie.
Sa’an nan Ezra ya tashi daga gidan Allah ya tafi gidan Yehohanan ɗan Eliyashib, a can ma bai ci wani abu ba, bai sha ruwa ba domin ya ci gaba da yin baƙin cikin rashin aminci na waɗanda suka dawo daga bauta.
7 And they caused a proclamation to goe throughout Iudah and Ierusalem, vnto all them of the captiuitie, that they should assemble themselues vnto Ierusalem.
Aka yi shela a duk fāɗin Yahuda da Urushalima cewa dukan waɗanda suka dawo daga bauta su tattaru a Urushalima.
8 And whosoeuer woulde not come within three dayes according to the counsel of the Princes and Elders, all his substance should be forfait, and he should be separate from the Congregation of them of the captiuitie.
Duk wanda bai zo a cikin kwana uku ba, za a washe shi, a kuma ware shi daga jama’ar da suka dawo daga bauta. Haka shugabanni da dattawa suka zartar.
9 Then all the men of Iudah and Beniamin assembled theselues vnto Ierusalem within three dayes, which was the twentieth day of the ninth moneth, and all the people sate in the streete of the house of God, trembling for this matter, and for the raine.
A cikin kwana uku duk mutanen Yahuda da na Benyamin suka taru a Urushalima. A ranar ashirin ga watan tara, dukan mutanen suka zauna a dandali a gaban gidan Allah cike da ɓacin rai saboda abin da ya faru da kuma ruwan da aka yi.
10 And Ezra the Priest stoode vp, and said vnto them, Ye haue transgressed, and haue taken strange wiues, to increase the trespasse of Israel.
Sai Ezra firist ya miƙe tsaye ya yi musu magana ya ce, “Kun yi rashin aminci; kun aure mata baƙi, ta haka kuka ƙara kan zunubin Isra’ila.
11 Now therefore giue praise vnto the Lord God of your fathers, and do his will, and separate your selues from the people of the land, and from the strange wiues.
Yanzu sai ku furta zunubanku ga Ubangiji, Allahn kakanninku, ku kuma yi nufinsa. Ku raba kanku da mutanen da suke kewaye da ku, ku kuma rabu da baƙin mata.”
12 And all the Congregation answered, and sayd with a loude voyce, So will we do according to thy wordes vnto vs.
Mutanen kuwa suka tā da murya da ƙarfi suka ce, “Gaskiya ka faɗa, dole mu yi yadda ka ce,
13 But the people are many, and it is a raynie weather, and we are not able to stande without, neither is it the worke of one day or two: for we are many that haue offended in this thing.
Amma akwai mutane da yawa, kuma lokacin damina ne; saboda haka ba za mu iya tsayawa a waje ba. Ban da haka ma, aikin nan ba na kwana ɗaya ko biyu ba ne, domin ba ƙaramin laifi muka yi ba.
14 Let our rulers stand therefore before all the Congregation, and let all them which haue taken strange wiues in our cities, come at the time appoynted, and with them the Elders of euery citie and the Iudges thereof, til the fierce wrath of our God for this matter turne away from vs.
Bari shugabanninmu su yi wani abu a madadin mutane duka, sa’an nan sai duk wanda ya san ya auri baƙuwar mace a garuruwanmu, sai yă zo nan a lokacin da aka shirya tare da dattawa da alƙalan kowane gari, har sai Allah ya huce fushinsa mai zafi da yake kanmu.”
15 Then were appoynted Ionathan the sonne of Asah-el, and Iahaziah the sonne of Tikuah ouer this matter, and Meshullam and Shabbethai the Leuites helped them.
Yonatan ɗan Asahel, da Yazehiya ɗan Tikba su ne kaɗai ba su yarda da wannan shirin ba, sai Meshullam da Shabbetai Balawe kuma suka goyi bayansu.
16 And they of the captiuitie did so, and departed, euen Ezra the Priest, and the men that were chiefe fathers to the familie of their fathers by name, and sate downe in the first day of the tenth moneth to examine the matter.
Sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi yadda aka zartar. Ezra firist ya zaɓi mutane waɗanda su ne shugabannin iyalai, ɗaya daga kowane sashe, aka rubuta sunan kowannensu. A ranar ɗaya ga watan goma kuwa suka zauna don su yi binciken waɗannan abubuwa.
17 And vntill the first day of the first moneth they were finishing the businesse with al the men that had taken strange wiues.
A rana ta farko ga watan farko, suka gama da bincike duk waɗanda suka auri baƙin mata.
18 And of the sonnes of the Priests there were men founde, that had taken strange wiues, to wit, of the sonnes of Ieshua, the sonne of Iozadak, and of his brethren, Maaseiah, Aeliezer, and Iarib and Gedaliah.
A cikin zuriyar firistoci, ga waɗanda suka auri mata baƙi. Daga zuriyar Yeshuwa ɗan Yozadak da’yan’uwansa, akwai Ma’asehiya, da Eliyezer, da Yarib, da Gedaliya.
19 And they gaue their hads, that they would put away their wiues, and they that had trespassed, gaue a ramme for their trespasse.
(Su ne suka miƙa hannuwansu suka nuna sun yarda su kori matansu baƙi, kowannensu kuma ya ba da rago daga cikin garkensa don a miƙa hadaya don zunubi.)
20 And of the sonnes of Immer, Honani, and Zebadiah.
Daga zuriyar Immer, akwai Hanani da Zebadiya.
21 And of the sonnes of Harim, Maaseiah, and Eliiah, and Shemaiah, and Iehiel, and Vzziah.
Daga zuriyar Harim, akwai Ma’asehiya, Iliya, Shemahiya, Yehiyel da Uzziya.
22 And of ye sonnes of Pashur, Elioenai, Maaseiah, Ishmael, Nethaneel, Iozabad, and Elasah.
Daga zuriyar Fashhur, akwai Eliyohenai, Ma’asehiya, Ishmayel, Netanel, Yozabad da Eleyasa.
23 And of the Leuites, Iozabad and Shimei, and Kelaiah, (which is Kelitah) Pethahiah, Iudah and Eliezer.
Cikin Lawiyawa, akwai Yozabad, Shimeyi, Kelaya (wato, Kelita), Fetahahiya, Yahuda, Eliyezer.
24 And of the singers, Eliashib. And of the porters, Shallum, and Telem, and Vri.
Daga mawaƙa, akwai Eliyashib. Daga masu tsaron ƙofofin haikali, akwai Shallum, Telem da Uri.
25 And of Israel: of the sonnes of Parosh, Ramiah, and Iesiah, and Malchiah, and Miamin, and Eleazar, and Malchiiah, and Benaiah.
Ga sunayen sauran mutanen Isra’ilan da suke da wannan laifi. Daga zuriyar Farosh, akwai Ramiya, da Izziya, Malkiya, Miyamin, Eleyazar, Malkiya da Benahiya.
26 And of the sonnes of Elam, Mattaniah, Zechariah, and Iehiel, and Abdi, and Ieremoth, and Eliah.
Daga zuriyar Elam, akwai Mattaniya, Zakariya, Yehiyel, Abdi, Yeremot, da Iliya.
27 And of the sonnes of Zattu, Elioenai, Eliashib, Mattaniah, and Ierimoth, and Zabad, and Aziza.
Daga iyalin Zattu, akwai Eliyohenai, Eliyashib, Mattaniya Yeremot da Zabad da Aziza.
28 And of the sonnes of Bebai, Iehohanan, Hananiah, Zabbai, Athlai.
Daga zuriyar Bebai, akwai Yehohanan, Hananiya, Zabbai, da Atlai.
29 And of the sonnes of Bani, Meshullam, Malluch, and Adaiah, Iashub, and Sheal, Ieramoth.
Daga zuriyar Bani, akwai Meshullam, Malluk, Adahiya, Yashub, Sheyal, da Ramot.
30 And of the sonnes of Pahath Moab, Adna, and Chelal, Benaiah, Maaseiah, Mattaniah, Bezaleel, and Binnui, and Manasseh.
Daga zuriyar Fahat-Mowab, akwai Adna, Kelal, Benahiya, Ma’asehiya, Mattaniya, Bezalel, Binnuyi, da Manasse.
31 And of the sonnes of Harim, Eliezer, Ishiiah, Malchiah, Shemaiah, Shimeon,
Daga zuriyar Harim, akwai Eliyezer, Isshiya, Malkiya, Shemahiya, Simeyon,
32 Beniamin, Malluch, Shamariah.
Benyamin, Malluk da Shemariya.
33 Of the sonnes of Hashum, Mattenai, Mattattah, Zabad, Eliphelet, Ieremai, Manasseh, Shimei.
Daga zuriyar Hashum, akwai Mattenai, da Mattatta, Zabad, Elifelet, Irmai, Manasse, da Shimeyi.
34 Of the sonnes of Bani, Maadai, Amram, and Vel,
Daga zuriyar Bani, akwai Ma’adai, Amram, Yuwel,
35 Banaiah, Bediah, Chelluh,
Benahiya, Bedeya, Keluhi,
36 Vaniah, Meremoth, Eliashib,
Baniya, Meremot, Eliyashib,
37 Mattaniah, Mattenai, and Iaasau,
Mattaniya, Mattenai da Ya’asu.
38 And Banni, and Bennui, Shimei,
Daga zuriyar Binnuyi, akwai Shimeyi,
39 And Shelemiah, and Nathan, and Adaiah,
Shelemiya, Natan, Adahiya,
40 Machnadebai, Shashai, Sharai,
Maknadebai, Shashai, Sharai,
41 Azareel, and Shelemiah, Shemariah,
Azarel, Shelemiya, da Shemariya,
42 Shallum, Amariah, Ioseph.
Shallum da Amariya da Yusuf.
43 Of the sonnes of Nebo, Ieiel, Mattithiah, Zabad, Zebina, Iadau, and Ioel, Benaiah.
Daga zuriyar Nebo, akwai Yehiyel, Mattitiya, Zabad, Zebina, Yaddai, Yowel da Benahiya.
44 All these had taken strange wiues: and among them were women that had children.
Dukan waɗannan sun auri baƙin mata, waɗansunsu suna da’ya’ya.

< Ezra 10 >