< Ezekiel 4 >

1 Thou also sonne of man, take thee a bricke, and lay it before thee, and pourtray vpon it the citie, euen Ierusalem,
“Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki tubalin yumɓu, ka ajiye shi a gabanka ka kuma zāna birnin Urushalima a kansa.
2 And lay siege against it, and builde a fort against it, and cast a mount against it: set the campe also against it, and lay engins of warre against it rounde about.
Sa’an nan ka yi mata ƙawanya. Ka kafa mata katangar ƙawanya, ka gina katangar da ɗan tudu ka kewaye ta da dundurusai.
3 Moreouer, take an yron pan, and set it for a wall of yron betweene thee and the citie, and direct thy face towarde it, and it shall be besieged, and thou shalt lay siege against it: this shall be a signe vnto the house of Israel.
Sa’an nan ka ɗauki kwanon ƙarfe, ka shirya shi kamar katangar ƙarfe tsakaninka da birnin ka kuma zuba mata ido. Za tă kasance a ƙarƙashin ƙawanya, kai kuwa za ka yi mata ƙawanya. Wannan zai zama alama ga gidan Isra’ila.
4 Sleepe thou also vpon thy left side, and lay the iniquitie of the house of Israel vpon it: according to the nomber of the dayes, that thou shalt sleepe vpon it, thou shalt beare their iniquity.
“Sa’an nan ka kwanta a hagunka ka kuma sa zunubin gidan Isra’ila a kanka. Za ka ɗauki zunubinsu na waɗansu kwanakin da kake kwance a gefenka.
5 For I haue layed vpon thee the yeeres of their iniquitie, according to the nomber of the dayes, euen three hundreth and ninetie dayes: so shalt thou beare the iniquitie of the house of Israel.
Na ɗora maka kwanaki bisa ga shekarun zunubinsu. Saboda haka cikin kwana 390 za ka ɗauki zunubin gidan Isra’ila.
6 And when thou hast accomplished them, sleepe againe vpon thy right side, and thou shalt beare the iniquitie of the house of Iudah fourtie dayes: I haue appointed thee a day for a yeere, euen a day for a yeere.
“Bayan ka gama haka, ka sāke kwantawa, a wannan lokaci a gefen damarka, ka kuma ɗauki zunubin gidan Yahuda. Na ɗora maka kwanaki 40, kwana guda a madadin shekara guda.
7 Therefore thou shalt direct thy face towarde the siege of Ierusalem, and thine arme shalbe vncouered, and thou shalt prophesie against it.
Ka juya fuskarka wajen ƙawanyar Urushalima da hannunka a buɗe ka yi annabci a kanta.
8 And beholde, I will lay bands vpon thee, and thou shalt not turne thee from one side to another, till thou hast ended the dayes of thy siege.
Zan ɗaura ka da igiyoyi don kada ka juya daga wannan gefe zuwa wani gefe sai ka gama kwanakin ƙawanyarka.
9 Thou shalt take also vnto thee wheate, and barley, and beanes, and lentiles, and millet, and fitches, and put them in one vessell, and make thee bread thereof according to the nomber of the dayes, that thou shalt sleepe vpon thy side: euen three hundreth and ninetie dayes shalt thou eate thereof.
“Ka ɗauki alkama da sha’ir, wake da acca, gero da maiwa; ka sa su a tulun ajiya ka kuma yi amfani da su don yin burodi wa kanka. Za ka ci shi a kwanaki 390 da za ka kwanta a gefenka.
10 And the meate, whereof thou shalt eate, shalbe by weight, euen twenty shekels a day: and from time to time shalt thou eate thereof.
Ka auna shekel ashirin na abinci don kowace rana ka kuma ci shi a ƙayyadadden lokaci.
11 Thou shalt drinke also water by measure, euen the sixt part of an Hin: from time to time shalt thou drinke.
Haka ma ka auna kashi ɗaya bisa shida na garwan ruwa ka sha shi a ƙayyadadden lokaci.
12 And thou shalt eate it as barley cakes, and thou shalt bake it in the dongue that commeth out of man, in their sight.
Ka ci abinci yadda za ka ci ƙosai sha’ir, ka gasa shi a gaban mutane, ka yi amfani da najasar mutane kamar itacen wuta.”
13 And the Lord said, So shall the children of Israel eate their defiled bread among the Gentiles, whither I will cast them.
Ubangiji ya ce, “Ta haka mutanen Isra’ila za su ci ƙazantaccen abinci a cikin al’ummai inda zan kore su in kai.”
14 Then said I, Ah, Lord God, beholde, my soule hath not bene polluted: for from my youth vp, euen vnto this houre, I haue not eaten of a thing dead, or torne in pieces, neither came there any vncleane flesh in my mouth.
Sai na ce, “Ba haka ba ne, Ubangiji Mai Iko Duka! Ban taɓa ƙazantar da kaina ba. Daga ƙuruciyata har zuwa yanzu ban taɓa cin wani abin da aka samu ya mutu ko abin da namun jeji suka kashe ba. Ba nama marar tsabtan da ya taɓa shiga bakina.”
15 Then he said vnto me, Loe, I haue giuen thee bullockes dongue for mans dongue, and thou shalt prepare thy bread therewith.
Sai ya ce, “To da kyau, zan bari ka gasa burodin a kan kashin shanu a maimakon najasar mutane.”
16 Moreouer, he said vnto me, Sonne of man, beholde, I will breake the staffe of bread in Ierusalem, and they shall eate bread by weight, and with care, and they shall drinke water by measure, and with astonishment.
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, zan yanke tanadin abinci a Urushalima. Mutane za su auna abincin da za su ci da tsoro su kuma auna ruwan da za su sha cikin fargaba,
17 Because that bread and water shall faile, they shalbe astonied one with another, and shall consume away for their iniquitie.
domin abinci da ruwa za su kāsa. Za su damu da ganin juna za su kuma lalace saboda zunubinsu.

< Ezekiel 4 >