< Ezekiel 39 >

1 Therefore, thou sonne of man, prophecie against Gog, and say, Thus sayeth the Lord God, Behold, I come against thee, O Gog, ye chiefe prince of Meshech and Tubal.
“Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
2 And I will destroy thee and leaue but the sixt part of thee, and will cause thee to come vp from the North partes and will bring thee vpon the mountaines of Israel:
Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
3 And I will smite thy bowe out of thy left hand, and I will cause thine arrowes to fall out of thy right hand.
Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
4 Thou shalt fal vpon the mountaines of Israel, and all thy bands and the people, that is with thee: for I will giue thee vnto the birdes and to euery feathered foule and beast of the fielde to be deuoured.
A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
5 Thou shalt fall vpon the open fielde: for I haue spoken it, sayth the Lord God.
Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
6 And I will sende a fire on Magog, and among them that dwell safely in the yles, and they shall knowe that I am the Lord.
Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
7 So will I make mine holy Name knowen in the middes of my people Israel, and I will not suffer them to pollute mine holy Name any more, and the heathen shall knowe that I am the Lord, the holy one of Israel.
“‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
8 Beholde, it is come, and it is done, sayeth the Lord God: and this is the day whereof I haue spoken.
Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
9 And they that dwell in the cities of Israel, shall goe forth, and shall burne and set fire vpon the weapons, and on the shieldes, and bucklers, vpon the bowes, and vpon the arrowes, and vpon the staues in their handes, and vpon the speares, and they shall burne them with fire seuen yeeres.
“‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
10 So that they shall bring no wood out of the fielde, neither cut downe any out of the forestes: for they shall burne the weapons with fire, and they shall robbe those that robbed them, and spoyle those that spoyled them, sayeth the Lord God.
Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
11 And at the same time will I giue vnto Gog a place there for burial in Israel, euen the valley whereby men go towarde the East part of the sea: and it shall cause them that passe by, to stoppe their noses, and there shall they bury Gog with all his multitude: and they shall call it the valley of Hamon-Gog.
“‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
12 And seuen moneths long shall the house of Israel be burying of the, that they may clense the land.
“‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
13 Yea, all the people of the lande shall burie them, and they shall haue a name when I shall be glorified, saith the Lord God.
Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
14 And they shall chuse out men to goe continually through the lande with them that trauaile, to bury those that remaine vpon ye ground, and clense it: they shall search to the ende of seuen moneths.
“‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
15 And the trauailers that passe through the land, if any see a mans bone, then shall he set vp a signe by it, till the buriers haue buried it, in the valley of Hamon-Gog.
Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
16 And also the name of the citie shalbe Hamonah: thus shall they clense the land.
Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
17 And thou sonne of man, thus sayeth the Lord God, Speake vnto euery feathered foule, and to all the beastes of the fielde, Assemble your selues, and come gather your selues on euery side to my sacrifice: for I do sacrifice a great sacrifice for you vpon the mountaines of Israel, that ye may eate flesh, and drinke blood.
“Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
18 Ye shall eate the flesh of the valiant, and drink the blood of the princes of the earth, of the weathers, of the lambes, and of the goates, and of bullockes, euen of all fat beastes of Bashan.
Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
19 And ye shall eate fat till you be full, and drinke blood, till ye be drunken of my sacrifice, which I haue sacrificed for you.
A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
20 Thus you shalbe filled at my table with horses and chariots, with valiant men, and with al men of warre, sayth the Lord God.
A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
21 And I wil set my glory among the heathe, and all the heathen shall see my iudgement, that I haue executed, and mine hand, which I haue layed vpon them.
“Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
22 So the house of Israel shall knowe, that I am the Lord their God from that day and so forth.
Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
23 And the heathen shall knowe, that ye house of Israel went into captiuitie for their iniquitie, because they trespassed against me: therefore hid I my face from them, and gaue them into ye hand of their enemies: so fell they all by the sword.
Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
24 According to their vncleannes, and according to their transgressions haue I done vnto the, and hid my face from them.
Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
25 Therefore thus sayth the Lord God, Nowe will I bring againe the captiuitie of Iaakob, and haue compassion vpon the whole house of Israel, and wil be ielous for mine holy Name,
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
26 After that they haue borne their shame, and all their transgression, whereby they haue transgressed against me, whe they dwelt safely in their land, and without feare of any.
Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
27 When I haue brought them againe from the people, and gathered them out of their enemies landes, and am sanctified in them in the sight of many nations,
Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
28 Then shall they know, that I am the Lord their God, which caused them to be led into captiuitie among the heathen: but I haue gathered them vnto their owne land, and haue left none of them any more there,
Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
29 Neither wil I hide my face any more from them: for I haue powred out my Spirit vpon the house of Israel, sayth the Lord God.
Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ezekiel 39 >