< Ezekiel 22 >

1 Moreover, the worde of the Lord came vnto me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Now thou sonne of man, wilt thou iudge, wilt thou iudge this bloody citie? wilt thou shew her all her abominations?
“Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
3 Then say, Thus sayth the Lord God, The citie sheddeth blood in the middes of it, that her time may come, and maketh idols against her selfe to pollute her selfe.
ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
4 Thou hast offended in thy blood, that thou hast shed, and hast polluted thy selfe in thine idols, which thou hast made, and thou hast caused thy dayes to draw neere, and art come vnto thy terme: therefore haue I made thee a reproch to the heathen, and a mocking to all countreys.
kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
5 Those that be neere, and those that be farre from thee, shall mocke thee, which art vile in name and sore in affliction.
Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
6 Beholde, the princes of Israel euery one in thee was ready to his power, to shed blood.
“‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
7 In thee haue they despised father and mother: in the middes of thee haue they oppressed the stranger: in thee haue they vexed the fatherlesse and the widowe.
A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
8 Thou hast despised mine holy things, and hast polluted my Sabbaths.
Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
9 In thee are men that cary tales to shed blood: in thee are they that eate vpon the mountaines: in ye mids of thee they comit abomination.
A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
10 In thee haue they discouered their fathers shame: in thee haue they vexed her that was polluted in her floures.
A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
11 And euery one hath committed abomination with his neighbours wife, and euery one hath wickedly defiled his daughter in lawe, and in thee hath euery man forced his owne sister, euen his fathers daughter.
A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
12 In thee haue they taken giftes to shed blood: thou hast taken vsurie and the encrease, and thou hast defrauded thy neighbours by extortion, and hast forgotten me, saith the Lord God.
A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
13 Beholde, therefore I haue smitten mine hands vpon thy couetousnesse, that thou hast vsed, and vpon the blood, which hath bene in the middes of thee.
“‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
14 Can thine heart endure, or can thine hands be strong, in the dayes that I shall haue to doe with thee? I the Lord haue spoken it, and will doe it.
Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
15 And I wil scatter thee among the heathen, and disperse thee in the countreys, and will cause thy filthines to cease from thee.
Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
16 And thou shalt take thine inheritance in thy selfe in the sight of the heathen, and thou shalt knowe that I am the Lord.
Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
17 And the worde of the Lord came vnto me, saying,
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 Sonne of man, the house of Israel is vnto me as drosse: all they are brasse, and tinne, and yron, and leade in the mids of the fornace: they are euen the drosse of siluer.
“Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
19 Therefore, thus sayth the Lord God, Because ye are all as drosse, beholde, therefore I will gather you in the middes of Ierusalem.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
20 As they gather siluer and brasse, and yron, and leade, and tinne into the middes of the fornace, to blowe the fire vpon it to melt it, so wil I gather you in mine anger and in my wrath, and wil put you there and melt you.
Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
21 I wil gather you, I say, and blowe the fire of my wrath vpon you, and you shalbe melted in the mids thereof.
Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
22 As siluer is melted in the mids of the fornace, so shall ye be melted in the mids thereof, and ye shall knowe, that I the Lord haue powred out my wrath vpon you.
Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
23 And the worde of the Lord came vnto me, saying,
Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
24 Sonne of man, say vnto her; Thou art the land, that is vncleane, and not rained vpon in the day of wrath.
“Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
25 There is a conspiracie of her prophets in the mids thereof like a roaring lyon, rauening the praye: they haue deuoured soules: they haue taken the riches and precious things: they haue made her many widowes in the mids thereof.
Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
26 Her Priests haue broken my Lawe, and haue defiled mine holy things: they haue put no difference betweene the holy and prophane, neither discerned betweene the vncleane, and the cleane, and haue hid their eyes from my Sabbaths, and I am prophaned among them.
Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
27 Her princes in the mids thereof are like wolues, rauening the praye to shed blood, and to destroy soules for their owne couetous lucre.
Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
28 And her prophets haue dawbed them with vntempered morter, seeing vanities, and diuining lies vnto them, saying, Thus sayth the Lord God, when the Lord had not spoken.
Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
29 The people of the land haue violently oppressed by spoyling and robbing, and haue vexed the poore and the needy: yea, they haue oppressed the stranger against right.
Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
30 And I sought for a man among them, that should make vp the hedge, and stand in the gap before me for the land, that I should not destroy it, but I found none.
“Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
31 Therefore haue I powred out mine indignation vpon them, and consumed them with the fire of my wrath: their owne wayes haue I rendred vpon their heads, sayth the Lord God.
Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ezekiel 22 >