< Ezekiel 15 >

1 And thee word of the Lord came vnto me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Sonne of man, what commeth of the vine tree aboue all other trees? and of the vine braunch, which is among the trees of ye forest?
“Ɗan mutum, da me itacen kuringa ya fi reshen waɗansu itatuwa kyau a cikin kurmi?
3 Shall wood bee taken thereof to doe any worke? or wil men take a pin of it to hang any vessel thereon?
An taɓa ɗaukan itacensa an yi wani abu mai amfani? Akan yi maratayi da ita da za a rataya wani abu a kai?
4 Behold, it is cast in the fire to be consumed: the fire consumeth both the endes of it, and the middes of it is burnt. Is it meete for any worke?
Bayan kuma a jefa ta cikin wuta, wuta kuma ta cinye kowane gefe ta kuma babbaka tsakiyarta, tana da amfani don yin wani abu kuma?
5 Behold, when it was whole, it was meete for no worke: how much lesse shall it bee meete for any worke, when the fire hath consumed it, and it is burnt?
In ba ta da amfanin wani abu sa’ad da take cikakkiya, balle bayan da wuta ta babbake ta, za a iya yin amfani da ita?
6 Therefore thus sayth the Lord God, As the vine tree, that is among the trees of the forest, which I haue giuen to the fire to be consumed, so will I giue the inhabitants of Ierusalem.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kamar yadda na ba da itacen kuringa a cikin itatuwan kurmi ya zama itacen wuta, haka zan sa mazaunan Urushalima su zama.
7 And I will set my face against them: they shall go out from one fire, and another fire shall consume them: and ye shall know, that I am the Lord, when I set my face against them,
Zan yi gāba da su. Ko da yake sun fito daga wuta, wuta za tă cinye su. Kuma sa’ad da na yi gāba da su, za ku san cewa ni ne Ubangiji.
8 And when I make the lande waste, because they haue greatly offended, saith the Lord God.
Zan mai da ƙasar kufai domin sun yi rashin aminci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ezekiel 15 >