< Exodus 8 >

1 Afterward the Lord sayde vnto Moses, Goe vnto Pharaoh, and tell him, Thus saith the Lord, Let my people goe, that they may serue me:
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
2 And if thou wilt not let them goe, beholde, I will smite all thy countrey with frogges:
In ka ƙi barinsu, zan hore ka da annoban kwaɗi a dukan ƙasarka.
3 And the riuer shall scral ful of frogges, which shall goe vp and come into thine house, and into thy chamber, where thou sleepest, and vpon thy bed, and into the house of thy seruants, and vpon thy people, and into thine ouens, and into thy kneading troughes.
Nilu zai cika da kwaɗi. Za su haura zuwa cikin fadanka da kan gadonka, cikin gidajen bayinka da kan mutanenka, cikin kwanonin toye-toyenka da na cin abincinka.
4 Yea, the frogges shall climbe vp vpon thee, and on thy people, and vpon all thy seruants.
Kwaɗin nan za su yi ta tsalle a kanka, da kan mutanenka, da kuma kan dukan bayinka.’”
5 Also the Lord said vnto Moses, Say thou vnto Aaron, Stretch out thine hande with thy rod vpon the streames, vpon the riuers, and vpon the ponds, and cause frogs to come vp vpon the land of Egypt.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka miƙa hannunka da sandanka bisa koguna da rafuffuka da kuma kududdufai, ka sa kwaɗi su fito su mamaye ƙasar Masar.’”
6 Then Aaron stretched out his hand vpon the waters of Egypt, and the frogges came vp, and couered the land of Egypt.
Sai Haruna ya miƙa hannunsa bisa ruwan Masar, kwaɗi kuwa suka fito, suka mamaye ƙasar Masar.
7 And the sorcerers did likewise with their sorceries, and brought frogges vp vpon the land of Egypt.
Amma bokaye ma suka yi abubuwan nan ta wurin sihirinsu; suka sa kwaɗi suka fito suka mamaye ƙasar Masar.
8 Then Pharaoh called for Moses and Aaron, and said, Pray ye vnto the Lord, that hee may take away the frogges from mee, and from my people, and I will let the people goe, that they may doe sacrifice vnto the Lord.
Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Yi addu’a ga Ubangiji yă ɗauke kwaɗi daga gare ni da mutanena, zan kuwa bar mutanenku su tafi su yi hadaya ga Ubangiji.”
9 And Moses said vnto Pharaoh, Concerning me, euen command when I shall pray for thee, and for thy seruants, and for thy people, to destroy the frogges from thee and from thine houses, that they may remaine in the riuer only.
Musa ya ce wa Fir’auna, “Na ba ka dama ka ba da lokacin da zan yi addu’a dominka da kuma bayinka da mutanenka, gidajenku kuwa za su rabu da kwaɗi, amma ban da waɗanda suke cikin Nilu.”
10 Then he said, To morowe. And he answered, Be it as thou hast said, that thou maiest know, that there is none like vnto the Lord our God.
Fir’auna ya ce, “Gobe.” Musa ya amsa, “Za a yi kamar yadda ka faɗa, domin ka sani babu wani kamar Ubangiji, Allahnmu.
11 So the frogges shall depart from thee, and from thine houses, and from thy seruantes, and from thy people: onely they shall remaine in the riuer.
Kwaɗin za su bar ka da gidajenka, bayinka da mutanenka; za su kasance a Nilu ne kaɗai.”
12 Then Moses and Aaron went out from Pharaoh: and Moses cryed vnto the Lord concerning the frogges, which hee had sent vnto Pharaoh.
Bayan Musa da Haruna sun bar Fir’auna, Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji saboda kwaɗin da ya kawo a bisa Fir’auna.
13 And the Lord did according to the saying of Moses: so the frogges died in the houses, in the townes, and in the fieldes.
Sai Ubangiji ya yi abin da Musa ya nema. Kwaɗin suka mutu a gidaje, da filaye, da kuma gonaki.
14 And they gathered the together by heaps, and the land stanke of them.
Aka jibga su tsibi-tsibi, ƙasar ta yi ɗoyi saboda su.
15 But when Pharaoh sawe that hee had rest giuen him, he hardened his heart, and hearkened not vnto them, as the Lord had said.
Amma da Fir’auna ya ga an sami sauƙi, sai ya taurare, ya ƙi yă saurari Musa da Haruna kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
16 Againe the Lord sayd vnto Moses, Say vnto Aaron, Stretche out the rod, and smite the dust of the earth, that it may bee turned to lyce throughout all the land of Egypt.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Miƙa hannunka ka bugi ƙurar ƙasa,’ dukan ƙurar ƙasar Masar kuwa za tă zama ƙwari masu cizo.”
17 And they did so: for Aaron stretched out his hand with his rod, and smote the dust of the earth: and lyce came vpon man and vpon beast: all the dust of the earth was lyce throughout all the land of Egypt.
Suka yi haka, da Haruna ya miƙa hannunsa da sandan, ya bugi ƙurar ƙasa, sai ƙwari masu cizo suka fito a kan mutane da dabbobi. Dukan ƙurar, ko’ina a ƙasar Masar ta zama cinnaku.
18 Nowe the enchanters assaied likewise with their enchantments to bring forth lyce, but they could not. So the lyce were vpon man and vpon beast.
Sa’ad da bokayen Fir’auna suka yi ƙoƙari yin sihiri iri na rufe ido domin su fito da kwari, sai suka kāsa. Ƙwari masu cizo kuwa suka rufe mutane da dabbobi.
19 Then saide the enchanters vnto Pharaoh, This is the finger of God. But Pharaohs heart remained obstinate, and hee hearkened not vnto them, as the Lord had said.
Sai bokaye suka ce wa Fir’auna, “Wannan fa da hannun Allah a ciki.” Amma zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurara ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
20 Moreouer the Lord sayd to Moses, Rise vp earely in the morning, and stand before Pharaoh (lo, hee will come forth vnto the water) and say vnto him, Thus saith the Lord, Let my people go, that they may serue me.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tashi da sassafe ka sadu da Fir’auna a lokacin da za shi kogi, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, bari mutanena su tafi, don su yi mini sujada.
21 Els, if thou wilt not let my people goe, behold, I will send swarmes of flies both vpon thee, and vpon thy seruants, and vpon thy people, and into thine houses: and the houses of the Egyptians shalbe full of swarmes of flies, and the ground also whereon they are.
In ba ka bar mutanena suka tafi ba, zan turo da tarin ƙuda a kanka da bayinka, a kan mutanenka da cikin gidajenka. Gidajen Masarawa za su cika da ƙudaje, har ma da ƙasa inda za su taka.
22 But ye land of Goshe, where my people are, wil I cause to be wonderfull in that day, so that no swarmes of flies shalbe there, that thou maiest know that I am the Lord in the middes of the earth.
“‘Amma zan keɓe yankin Goshen, inda mutanena suke don kada ƙudaje su taɓa wurin, domin ka sani cewa Ni, Ubangiji, ina cikin wannan ƙasa.
23 And I will make a deliuerance of my people from thy people: to morowe shall this miracle be.
Zan sa iyaka tsakanin jama’ata da jama’arka. Gobe ne wannan mu’ujiza za tă auku.’”
24 And the Lord did so: for there came great swarmes of flies into the house of Pharaoh, and into his seruants houses, so that through all the lande of Egypt, the earth was corrupt by the swarmes of flies.
Ubangiji kuwa ya yi haka. Tarin ƙuda suka zubo a fadar Fir’auna da cikin gidajen bayinsa, da ko’ina a Masar, ƙasar kuwa ta lalace saboda ƙudaje.
25 Then Pharaoh called for Moses and Aaron, and saide, Goe, doe sacrifice vnto your God in this lande.
Sai Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tafi, ku miƙa hadaya ga Allahnku, a nan a cikin ƙasar.”
26 But Moses answered, It is not meete to do so: for then we shoulde offer vnto the Lord our God that, which is an abomination vnto the Egyptians. Loe, can we sacrifice the abomination of the Egyptians before their eyes, and they not stone vs?
Amma Musa ya ce, “Wannan ba zai yiwu ba. Hadayun da mukan miƙa wa Ubangiji, Allahnmu haram ne ga Masarawa. In kuwa muka miƙa hadayun da suke haram a idanunsu, ba za su jajjefe mu ba?
27 Let vs go three dayes iourney in the desert, and sacrifice vnto the Lord our God, as he hath commanded vs.
Dole mu yi tafiya kwana uku cikin hamada domin miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnmu, yadda ya umarce mu.”
28 And Pharaoh said, I will let you go, that ye may sacrifice vnto the Lord your God in the wildernesse: but goe not farre away, pray for me.
Fir’auna ya ce, “Zan bar ku ku tafi, don ku miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnku, a cikin hamada, amma ba za ku tafi da nisa ba. Yanzu ku yi mini addu’a.”
29 And Moses said, Behold, I will go out from thee, and pray vnto the Lord, that the swarmes of flies may depart from Pharaoh, from his seruants, and from his people to morowe: but let Pharaoh from hencefoorth deceiue no more, in not suffering the people to sacrifice vnto the Lord.
Musa ya amsa, “Da zarar na bar ka, zan yi addu’a ga Ubangiji, gobe kuwa ƙudaje za su bar Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa. Sai dai a tabbata Fir’auna bai sāke yin ruɗi ta wurin ƙin barin mutane su tafi su miƙa hadayu ga Ubangiji ba.”
30 So Moses went out from Pharaoh and prayed vnto the Lord.
Sa’an nan Musa ya rabu da Fir’auna, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
31 And the Lord did according to the saying of Moses, and the swarmes of flies departed from Pharaoh, from his seruants, and from his people, and there remained not one.
Ubangiji kuwa ya yi abin da Musa ya roƙa. Ƙudaje suka rabu da Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa; ba ƙudan da ya rage.
32 Yet Pharaoh hardened his heart at this time also, and did not let the people goe.
Amma a wannan lokaci ma, Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai kuma bar mutanen suka tafi ba.

< Exodus 8 >