< Exodus 24 >

1 Now hee had said vnto Moses, Come vp to the Lord, thou, and Aaron, Nadab, and Abihu, and seuentie of the Elders of Israel, and yee shall worship a farre off.
Ana nan sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ku hauro zuwa wurina, kai da Haruna, Nadab da Abihu, da kuma dattawa saba’in a cikin Isra’ila. Za ku yi sujada da ɗan nisa,
2 And Moses himselfe alone shall come neere to the Lord, but they shall not come neere, neither shall the people goe vp with him.
sai Musa kaɗai zai kusaci Ubangiji. Amma sauran kada su zo kusa, kada kuma jama’a su hau tare da shi.”
3 Afterwarde Moses came and told the people all the wordes of the Lord, and all the lawes: and all the people answered with one voyce, and said, All the things which the Lord hath said, will we doe.
Sa’ad da Musa ya tafi ya faɗa wa mutanen duk kalmomin Ubangiji da dokokinsa, sai suka amsa da murya ɗaya suna cewa, “Duk abin da Ubangiji ya faɗa, za mu yi.”
4 And Moses wrote all the wordes of the Lord, and rose vp early, and set vp an altar vnder the mountaine, and twelue pillars according to the twelue tribes of Israel.
Sai Musa ya rubuta duk abin da Ubangiji ya faɗa. Ya tashi kashegari da sassafe ya gina bagade kusa da dutsen, ya aza al’amudai goma sha biyu bisa ga kabilu goma sha biyu na Isra’ila.
5 And he sent young men of the children of Israel, which offered burnt offrings of bieues, and sacrificed peace offrings vnto the Lord.
Sai ya aiki samarin Isra’ilawa, suka miƙa hadaya ta ƙonawa, suka kuma miƙa ƙananan bijimai don hadaya ta salama ga Ubangiji.
6 Then Moses tooke halfe of the blood, and put it in basens, and halfe of the blood he sprinckled on the altar.
Musa ya ɗauki rabin jinin ya zuba a cikin kwanoni, rabin kuma ya yayyafa a kan bagaden.
7 After he tooke the booke of the couenant, and read it in the audience of the people: who said, All that the Lord hath said, we will do, and be obedient.
Sa’an nan ya ɗauki Littafin Alkawari ya karanta wa mutane. Suka amsa suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa; za mu yi biyayya.”
8 Then Moses tooke the blood, and sprinkled it on the people, and said, Behold, the blood of the couenant, which the Lord hath made with you concerning all these things.
Musa ya kuma ɗauki jinin, ya yayyafa a kan mutanen ya ce, “Wannan shi ne jinin alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, bisa ga dukan waɗannan kalmomi.”
9 Then went vp Moses and Aaron, Nadab, and Abihu, and seuentie of the Elders of Israel.
Musa da Haruna, Nadab da Abihu, da dattawa saba’in, Allah na Isra’ila suka haura
10 And they saw the God of Israel, and vnder his feete was as it were a worke of a Saphir stone, and as the very heauen when it is cleare.
suka kuma ga Allah na Isra’ila. A ƙarƙashin ƙafafunsa akwai wani abu wanda aka yi da saffaya, mai haske kuma kamar sararin sama kansa.
11 And vpon the nobles of the children of Israel he laide not his hande: also they sawe God, and did eate and drinke.
Amma Allah bai yi wa shugabannin Isra’ila wani abu ba; suka ga Allah, suka ci suka kuma sha.
12 And the Lord said vnto Moses, Come vp to me into the mountaine, and be there, and I will giue thee tables of stone, and the law and the commandement, which I haue written, for to teach them.
Ubangiji ya ce wa Musa, “Hauro wurina a kan dutse, ka tsaya a nan, zan ba ka allunan dutsen, da doka da umarnan da na rubuta don koyonsu.”
13 Then Moses rose vp, and his minister Ioshua, and Moses went vp into the mountaine of God,
Sa’an nan Musa ya fita tare da Yoshuwa mataimakinsa, ya kuwa hau kan dutsen Allah.
14 And said vnto the Elders, Tary vs here, vntill we come againe vnto you: and beholde, Aaron, and Hur are with you: whosoeuer hath any matters, let him come to them.
Ya ce wa dattawan, “Ku jira mu a nan, sai mun dawo wurinku. Haruna da Hur suna tare da ku, in wani yana da wata damuwa, sai yă je wurinsu.”
15 Then Moses went vp to the mount, and the cloude couered the mountaine,
Da Musa ya hau dutsen, sai girgije ya rufe dutsen,
16 And the glorie of the Lord abode vpon mount Sinai, and the cloude couered it sixe dayes: and the seuenth day he called vnto Moses out of the middes of the cloude.
sai ɗaukakar Ubangiji ta sauka a kan Dutsen Sinai, kwana shida girgije ya rufe dutsen, a rana ta bakwai, sai Ubangiji ya kira Musa daga cikin girgijen.
17 And the sight of the glorie of the Lord was like consuming fire on the top of the moutaine, in the eyes of the children of Israel.
Ga Isra’ilawa dai, ɗaukakar Ubangiji ta yi kamar wuta mai ci a kan dutse.
18 And Moses entred into the middes of the cloude, and went vp to the mountaine: and Moses was in the mount fourtie dayes and fourty nightes.
Sa’an nan Musa ya shiga girgijen ya hau kan dutsen. Ya zauna a kan dutsen yini arba’in da dare arba’in.

< Exodus 24 >