< Exodus 16 >

1 Afterward all the Congregation of the children of Israel departed from Elim, and came to the wildernes of Sin, (which is betweene Elim and Sinai) the fiftenth day of the second moneth after their departing out of ye land of Egypt.
Dukan taron Isra’ila suka tashi daga Elim suka zo hamadar Sin, wadda take tsakanin Elim da Sinai, a rana ta goma sha biyar ga wata biyu, bayan sun fito daga Masar.
2 And the whole Congregation of the children of Israel murmured against Moses and against Aaron in the wildernesse.
A hamadan, dukan taro suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna.
3 For the children of Israel sayde to them, Oh that we had dyed by the hand of the Lord in the land of Egypt, when wee sate by the flesh pots, when wee ate bread our bellies full: for yee haue brought vs out into this wildernesse, to kill this whole company with famine.
Isra’ilawa suka ce musu, “Da ma a hannun Ubangiji ne muka mutu a Masar, inda muka zauna kewaye da tukwanen nama, muna cin duk abincin da muke so, amma kun kawo mu cikin wannan hamada don ku kashe dukan wannan taro da yunwa.”
4 Then sayd the Lord vnto Moses, Behold, I wil cause bread to rayne from heauen to you, and the people shall goe out, and gather that that is sufficient for euery day, that I may proue them, whether they wil walke in my Law or no.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan zubo muku burodi kamar ruwa daga sama. Mutanen za su fita kowace rana su tattara abin da zai ishe su na ranan. Ta haka zan gwada su in ga ko za su bi umarnaina.
5 But the sixt daye they shall prepare that, which they shall bring home, and it shalbe twise as much as they gather dayly.
A rana ta shida za su shirya abin da suka kwaso, wannan kuwa zai zama ninki biyu na abin da sukan tattara na sauran ranaku.”
6 Then Moses and Aaron sayde vnto all the children of Israel, At euen ye shall know, that the Lord brought you out of the land of Egypt:
Saboda haka Musa da Haruna suka ce wa dukan Isra’ila, “Da yamma za ku sani Ubangiji ne ya fitar da ku daga Masar.
7 And in the morning ye shall see the glorie of the Lord: for he hath heard your grudgings against the Lord: and what are we that ye haue murmured against vs?
Da safe za ku ga ɗaukakar Ubangiji, saboda ya ji gunaguninku a kansa. Wane mu, da za ku yi gunaguni a kanmu?”
8 Againe Moses sayd, At euen shall the Lord giue you flesh to eate, and in the morning your fil of bread: for the Lord hath heard your murmurings, which ye murmure against him: for what are we? your murmurings are not against vs, but against the Lord.
Musa ya kuma ce, “Za ku san cewa shi ne Ubangiji, sa’ad da ya ba ku nama ku ci da yamma, da kuma duk burodin da kuke so da safe, saboda ya ji gunagunin da kuka yi a kansa. Namu a wane? Ai, gunaguninku ba a kanmu ba, amma a kan Ubangiji ne.”
9 And Moses sayd to Aaron, Say vnto all the Congregation of the children of Israel, Draw neere before the Lord: for he hath heard your murmurings.
Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka faɗa wa dukan taron Isra’ila, ‘Ku zo gaban Ubangiji, gama ya ji gunaguninku.’”
10 Now as Aaron spake vnto the whole Congregation of the children of Israel, they looked toward the wildernesse, and beholde, the glory of the Lord appeared in a cloude.
Yayinda Haruna yake magana da dukan taron Isra’ila, sai suka duba wajen hamada, sai ga ɗaukakar Ubangiji tana bayyana a girgije.
11 (For the Lord had spoken vnto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
12 I haue heard the murmurings of the children of Israel: tell them therefore, and say, At euen ye shall eate flesh, and in the morning ye shall be filled with bread, and ye shall knowe that I am the Lord your God)
“Na ji gunagunin Isra’ilawa. Ka faɗa musu, ‘A tsakanin fāɗuwar rana da almuru, za ku ci nama, da safe kuma za ku ƙoshi da burodi. Sa’an nan za ku sani ni ne Ubangiji Allahnku.’”
13 And so at euen the quailes came and couered the campe: and in the morning the dewe lay round about the hoste.
Da yamman wannan rana, sai makware suka rufe dukan sansani, da safe kuma sai ga raɓa ta kewaye sansani.
14 And when the dewe that was fallen was ascended, beholde, a small round thing was vpon the face of the wildernes, small as the hoare frost on the earth.
Lokacin da raɓar ta watse, sai ga wani abu kamar tsaki, falle-falle kuma da laushi, fari, kamar hazo, a ƙasa.
15 And when the children of Israel sawe it, they sayde one to another, It is MAN, for they wist not what it was. And Moses sayd vnto them, This is the breade which the Lord hath giuen you to eate.
Sa’ad da Isra’ilawa suka ga wannan, sai suka ce wa junansu, “Mene ne wannan?” Gama ba su san ko mene ne ba. Musa ya ce musu, “Wannan shi ne burodin da Ubangiji ya ba ku ku ci.
16 This is the thing which the Lord hath commanded: gather of it euery man according to his eating an Omer for a man according to the number of your persons: euery man shall take for them which are in his tent.
Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Kowane mutum zai tattara bisa ga bukatarsa. Ku tara rabin gallon don mutum guda da yake cikin tentinku.’”
17 And the children of Israel did so, and gathered, some more, some lesse.
Isra’ilawa suka yi kamar yadda aka faɗa musu, waɗansu suka tattara da yawa, waɗansu kuma kaɗan.
18 And when they did measure it with an Omer, hee that had gathered much, had nothing ouer, and he that had gathered litle, had no lacke: so euery man gathered according to his eating.
Da suka gwada a mudu, wanda ya tattara da yawa bai sami mafi yawa ba, wanda kuma ya tattara kaɗan bai sami ƙanƙani ba. Kowane mutum ya tattara daidai bukatarsa.
19 Moses then said vnto them, Let no man reserue thereof till morning.
Sa’an nan Musa ya ce musu, “Kada wani yă bar saura har safe.”
20 Notwithstanding they obeyed not Moses: but some of them reserued of it till morning, and it was full of wormes, and stanke: therefore Moses was angrie with them.
Duk da haka waɗansu ba su kula da umarnin Musa ba, suka bar saura har safe, kashegari kuwa ta yi tsutsotsi, ta ruɓe, sai Musa ya yi fushi da su.
21 And they gathered it euery morning, euery man according to his eating: for when the heate of the sunne came, it was melted.
Kowace safiya, kowanne mutum yakan tattara daidai bukatarsa, lokacin da rana ta yi zafi, sai ta narke.
22 And the sixt day they gathered twise so much bread, two Omers for one man: then all the rulers of the Congregation came and told Moses.
A rana ta shida, suka tattara ninki biyu, mudu biyu ga mutum guda, sai shugabannin taron suka zo suka kawo ƙara wurin Musa.
23 And he answered them, This is that, which the Lord hath sayde, To morowe is the rest of the holy Sabbath vnto the Lord: bake that to day which ye wil bake, and seethe that which ye wil seethe, and all that remaineth, lay it vp to be kept till the morning for you.
Shi kuma ya ce musu, “Wannan shi ne umarnin Ubangiji, ‘Gobe za tă zama ranar hutu, Asabbaci mai tsarki ga Ubangiji. Domin haka sai ku toya abin da kuke so ku toya, ku kuma dafa abin da kuke so ku dafa. Abin da ya rage ku ajiye har safe.’”
24 And they laied it vp till the morning, as Moses bade, and it stanke not, neyther was there any worme therein.
Sai suka bar saura har safe, kamar yadda Musa ya umarta, bai kuwa yi wari ko yă yi tsutsa ba.
25 Then Moses sayde, Eate that to day: for to day is the Sabbath vnto the Lord: to day ye shall not finde it in the fielde.
Musa ya ce, “Ku ci shi yau, saboda yau Asabbaci ne na Ubangiji. Ba za ku same shi a ƙasa a yau ba.
26 Sixe dayes shall yee gather it, but in the seuenth day is the Sabbath: in it there shalbe none.
Kwana shida za ku tattara shi, amma a rana ta bakwai, Asabbaci, ba za a same shi ba.”
27 Notwithstanding, there went out some of the people in ye seuenth day for to gather, and they found none.
Duk da haka waɗansu mutane suka fita a ranar Asabbaci don su tattara, amma ba su sami kome ba.
28 And the Lord sayde vnto Moses, Howe long refuse yee to keepe my commandements, and my lawes?
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe za ku ƙi bin dokokina da umarnaina?
29 Beholde, howe the Lord hath giuen you the Sabbath: therefore he giueth you the sixt day bread for two dayes: tary therefore euery man in his place: let no man goe out of his place the seuenth day.
Ku lura fa, ai, Ubangiji ne ya ba ku Asabbaci; shi ya sa a kan ba ku burodi na kwana biyu, a rana ta shida. Kowa ya kamata yă kasance inda yake a rana ta bakwai; kada kowa yă fita.”
30 So the people rested the seuenth day.
Sai mutanen suka huta a rana ta bakwai.
31 And the house of Israel called the name of it, MAN. and it was like to coriander seede, but white: and the taste of it was like vnto wafers made with hony.
Mutanen Isra’ila suka kira burodin Manna. Manna yana nan fari kamar farin riɗi, ɗanɗanonsa kuma yana kama da masa da aka yi da zuma.
32 And Moses said, This is that which the Lord hath commanded, Fill an Omer of it, to keepe it for your posteritie: that they may see the bread wherewith I haue fed you in wildernesse, when I brought you out of the land of Egypt.
Musa ya ce, “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Ku auna mudu guda na Manna, a adana ta dukan zamananku, domin kowane zamani yă ga irin abincin da na ba ku ku ci a hamada, yayinda na fitar da ku daga Masar.’”
33 Moses also said to Aaron, Take a pot and put an Omer full of MAN therein, and set it before the Lord to be kept for your posteritie.
Saboda haka Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki tulu, ka sa mudu guda na Manna a ciki. Sa’an nan ka sa shi a gaban Ubangiji, don a adana don tsararraki masu zuwa.”
34 As the Lord commanded Moses, so Aaron laied it vp before the Testimonie to be kept.
Sai Haruna ya ajiye Mannar a gaban Akwatin Alkawari, don a adana ta kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
35 And the children of Israel did eate MAN fourtie yeres, vntill they came vnto a land inhabited: they did eate MAN vntill they came to the borders of the land of Canaan.
Isra’ilawa suka yi shekaru arba’in suna cin Manna, har sai da suka shiga cikin ƙasar da take da mutane, suka ci Manna har zuwa kan iyakar ƙasar Kan’ana.
36 The Omer is the tenth part of the Ephah.
(Omer guda, daidai ne da kashi ɗaya bisa goma na Efa.)

< Exodus 16 >