< Exodus 12 >

1 Then the Lord spake to Moses and to Aaron in the land of Egypt, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna a Masar,
2 This moneth shalbe vnto you the beginning of moneths: it shalbe to you the first moneth of the yere.
“Wannan wata za tă zama a gare ku wata na farko, wata na fari na shekararku.
3 Speake ye vnto all the congregation of Israel, saying, In the tenth of this moneth let euery man take vnto him a lambe, according to the house of the fathers, a lambe for an house.
Ka faɗa wa dukan jama’ar Isra’ila cewa a rana ta goma ga wannan wata, kowane mutum zai ɗauki ɗan rago domin iyalinsa, ɗaya domin kowane gida.
4 And if the housholde be too litle for the lambe, he shall take his neighbour, which is next vnto his house, according to the nomber of the persons: euery one of you, according to his eating shall make your count for the lambes,
In akwai wani gidan da ba za su iya cinye rago guda ɗungum ba, saboda iyalin kima ne, to, sai su haɗa kai da maƙwabtansu, su ɗauki rago guda gwargwadon yawansu, bisa ga abin da mutum guda zai ci.
5 Your lambe shalbe without blemish, a male of a yeere olde: ye shall take it of the lambes, or of the kiddes.
Dabbobin da za ku zaɓa, dole su zama bana ɗaya, namiji marar tabo, za ku kuma kamo su daga cikin tumaki ko awaki.
6 And yee shall keepe it vntill the fourteenth day of this moneth: then al the multitude of the Congregation of Israel shall kill it at euen.
Za ku turke dabbar har rana ta goma sha huɗu ga wata, wato, sa’ad da dukan taron jama’ar Isra’ila za su yanka ragunansu da yamma.
7 After, they shall take of the blood, and strike it on the two postes, and on the vpper doore post of the houses where they shall eate it.
Sa’an nan za su ɗauki jinin, su shafa a gefen da yake saman dogaran ƙofa na gidajen da suke cin naman dabbobin.
8 And they shall eate the flesh the same night, roste with fire, and vnleauened bread: with sowre herbes they shall eate it.
A wannan dare, za su gasa naman, su ci da ganyaye masu ɗaci, da kuma burodi marar yisti.
9 Eate not thereof rawe, boyled nor sodden in water, but rost with fire, both his head, his feete, and his purtenance.
Kada ku ci nama ɗanye, ko kuma dafaffe, amma a gasa shi, da kan, da ƙafafun, da kuma kayan cikin.
10 And ye shall reserue nothing of it vnto the morning: but that, which remaineth of it vnto the morowe, shall ye burne with fire.
Kada ku bar kome yă kai gobe, abin da ya kai gobe kuwa, sai ku ƙone shi.
11 And thus shall yee eate it, Your loynes girded, your shoes on your feete, and your staues in your handes, and yee shall eate it in haste: for it is the Lords Passeouer.
Ga yadda za ku ci shi, ku yi ɗamara, takalma kuwa a ƙafafunku, kuna riƙe da sandunan tafiya a hannunku. Ku ci shi da gaggawa; Bikin Ƙetarewa ne na Ubangiji.
12 For I will passe through the lande of Egypt the same night, and will smite all the first borne in the land of Egypt, both man and beast, and I will execute iudgement vpon all the gods of Egypt. I am the Lord.
“A wannan dare, zan ratsa Masar, in bugi kowane ɗan fari, na mutum da na dabba, zan kuma hukunta dukan gumakan Masar. Ni ne Ubangiji.
13 And the blood shalbe a token for you vpon the houses where ye are: so when I see the blood, I will passe ouer you, and the plague shall not be vpon you to destruction, when I smite the lande of Egypt.
Jinin zai zama alama a gare ku, a gidajen da kuke; sa’ad da kuwa na ga jinin, zan ƙetare ku. Ba wata annoba mai hallakarwa da za tă taɓa ku yayinda na bugi Masar.
14 And this day shalbe vnto you a remembrance: and ye shall keepe it an holie feast vnto the Lord, throughout your generations: yee shall keepe it holie by an ordinance for euer.
“Wannan rana za tă zama muku abin tunawa dukan zamananku masu zuwa, za ku kiyaye ta kamar biki ga Ubangiji, dawwammamiyar farilla ce har abada.
15 Seuen daies shall ye eat vnleauened bread, and in any case ye shall put away leauen the first day out of your houses: for whosoeuer eateth leauened bread from the first daie vntill the seuenth day, that person shalbe cut off from Israel.
Kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti. A rana ta fari, za ku fid da yisti daga gidajenku gama duk wanda ya ci abu mai yisti daga rana ta fari har zuwa rana ta bakwai, za a fid da shi daga Isra’ila.
16 And in the first day shalbe an holie assemblie: also in the seuenth day shalbe an holy assemblie vnto you: no worke shalbe done in them, saue about that which euery man must eate: that onely may ye do.
A rana ta fari, za ku yi taro mai tsarki, haka kuma za ku sāke yi a rana ta bakwai. Kada ku yi aiki a waɗannan ranaku, sai dai ku shirya abinci domin kowa, abin da za ku yi ke nan kawai.
17 Ye shall keepe also the feast of vnleauened bread: for that same daye I will bring your armies out of the lande of Egypt: therefore ye shall obserue this day, throughout your posteritie, by an ordinance for euer.
“Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti domin a wannan rana ce na fitar da ku ɓangare-ɓangare daga Masar. Ku kiyaye wannan rana ta zama muku dawwammamiyar farilla wa tsara masu zuwa.
18 In the first moneth and the fourteenth day of the moneth at euen, yee shall eate vnleauened bread vnto the one and twentieth day of the moneth at euen.
A wata na fari, za ku ci burodi marar yisti daga yammancin ranar goma sha huɗu har zuwa yammancin ranar ashirin da ɗaya.
19 Seuen daies shall no leauen be founde in your houses: for whosoeuer eateth leauened bread, that person shalbe cut off from the Congregation of Israel: whether he bee a stranger, or borne in the land.
Kada a sami yisti a gidajenku har kwana bakwai. Kuma duk wanda ya ci wani abu mai yisti, za a fid da shi daga taron jama’ar Isra’ila, ko baƙo ne, ko haifaffen ɗan ƙasa.
20 Ye shall eate no leauened bread: but in all your habitations shall ye eate vnleauened bread.
Kada ku ci wani abincin da aka yi da yisti. Ko’ina kuka zauna, dole ku ci burodi marar yisti.”
21 Then Moses called all the Elders of Israel, and saide vnto them, Choose out and take you for euerie of your housholdes a lambe, and kill the Passeouer.
Sa’an nan Musa ya kira dukan dattawan Isra’ila ya ce musu, “Ku je da sauri ku zaɓi dabbobin iyalanku, ku yanka ragon Bikin Ƙetarewa.
22 And take a bunch of hyssop, and dip it in the blood that is in the basen, and strike the lintell, and the doore cheekes with the blood that is in the basen, and let none of you goe out at the doore of his house, vntill the morning.
Ku ɗauki ƙunshin itacen hizzob, ku tsoma cikin jinin da yake a kwano, ku yayyafa wa dogaran ƙofa duka biyu, da bisa kan ƙofar. Kada wani daga cikinku yă fita daga ƙofar gidansa sai da safe.
23 For the Lord will passe by to smite the Egyptians: and when he seeth the blood vpon the lintel and on the two doore cheekes, the Lord wil passe ouer the doore, and wil not suffer the destroyer to come into your houses to plague you.
Sa’ad da Ubangiji yake ratsa ƙasar don yă bugi Masarawa, zai ga jinin a bisa da kuma gefen madogaran ƙofa, zai ƙetare ƙofar, ba zai bar mai hallakawa yă shiga gidajenku, yă buge ku ba.
24 Therefore shall ye obserue this thing as an ordinance both for thee and thy sonnes for euer.
“Ku kiyaye waɗannan dokokin a matsayin dawwammamiyar farilla, da ku da’ya’yanku har abada.
25 And when ye shall come into the land, which the Lord will giue you as hee hath promised, then ye shall keepe this seruice.
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji zai ba ku yadda ya alkawarta, ku kiyaye wannan biki.
26 And when your children aske you, What seruice is this ye keepe?
Sa’ad da kuma’ya’yanku suka tambaye ku, ‘Mece ce manufar wannan biki?’
27 Then ye shall saye, It is the sacrifice of the Lordes Passeouer, which passed ouer the houses of the children of Israel in Egypt, when he smote the Egyptians, and preserued our houses. Then the people bowed them selues, and worshipped.
Sai ku faɗa musu, ‘Hadaya ce ta Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, domin ya tsallake gidajen Isra’ilawa a Masar, lokacin da ya kashe Masarawa, amma bai taɓa gidajenmu ba.’” Sai mutane suka rusuna, suka yi sujada.
28 So the children of Israel went, and did as the Lord had commanded Moses and Aaron: so did they.
Isra’ilawa suka tafi suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
29 Nowe at midnight, the Lord smote all the first borne in the lande of Egypt, from the first borne of Pharaoh that sate on his throne, vnto the first borne of the captiue that was in prison, and all the first borne of beastes.
Da tsakar dare, sai Ubangiji ya karkashe dukan’ya’yan fari a ƙasar Masar, tun daga ɗan farin Fir’auna, wato, magājinsa, har zuwa ɗan fari na ɗan sarƙa da yake kurkuku, har da’ya’yan fari na dabbobi.
30 And Pharaoh rose vp in the night, he, and all his seruants and all the Egyptians: and there was a great crye in Egypt: for there was no house where there was not one dead.
Fir’auna da dukan fadawansa da kuma dukan Masarawa, suka tashi a cikin daren da kuka mai zafi, aka kuma ji kukan a ko’ina a cikin ƙasar Masar, gama ba gidan da ba a yi mutuwa ba.
31 And hee called to Moses and to Aaron by night, and saide, Rise vp, get you out from among my people, both yee, and the children of Israel, and goe serue the Lord as ye haue sayde.
A cikin daren, Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tashi, ku da jama’arku, ku fita daga cikin jama’ata. Ku tafi, ku bauta wa Ubangiji yadda kuka ce.
32 Take also your sheepe and your cattell as yee haue sayde, and depart, and blesse me also.
Ku kwashi garkunanku na tumaki da na awaki, da na shanu, ku yi tafiyarku kamar yadda kuka ce, amma ku sa mini albarka.”
33 And the Egyptians did force the people, because they would send them out of the land in haste: for they said, We die all.
Masarawa suka matsa wa Isra’ilawa su fita daga ƙasarsu da sauri. Gama mutanen Masar sun ce, “Ai, za mu mutu duka, in ba su tafi ba!”
34 Therfore the people tooke their dough before it was leauened, euen their dough bound in clothes vpon their shoulders.
Sai mutanen suka ɗauki garin da sun kwaɓa ba yisti a ciki, tare da ƙwaryansu na aikin kwaɓan, suka nannaɗe su a mayafansu, suka rataye a kafaɗunsu.
35 And the children of Israel did according to the saying of Moses, and they asked of ye Egyptians iewels of siluer and iewels of gold, and raiment.
Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Musa ya umarce su, suka roƙi Masarawa kayan adonsu na azurfa da na zinariya, da kuma tufafi.
36 And the Lord gaue the people fauour in the sight of the Egyptians: and they graunted their request: so they spoyled the Egyptians.
Ubangiji kuwa ya sa Isra’ilawa suka yi farin jini a wurin Masarawa, Masarawa kuma suka saki hannu wa mutanen, suka ba su duk abin da suka roƙa; ta haka Isra’ilawa suka washe Masarawa.
37 Then the children of Israel tooke their iourney from Rameses to Succoth about sixe hundreth thousand men of foote, beside children.
Isra’ilawa suka kama tafiya daga Rameses zuwa Sukkot. Akwai maza dubu ɗari shida da suke tafiya da ƙafa, ban da mata da yara.
38 And a great multitude of sundrie sortes of people went out with them, and sheepe, and beeues, and cattel in great abundance.
Waɗansu mutane da yawa da ba Isra’ilawa ba, suka haura tare da su, da garkunan shanu, da na tumaki da awaki.
39 And they baked the dough which they brought out of Egypt, and made vnleauened cakes: for it was not leauened, because they were thrust out of Egypt, neither coulde they tarie, nor yet prepare themselues vitailes.
Suka toya burodi marar yisti da garin da aka kwaɓa wanda suka kawo daga Masar. Garin da aka kwaɓan ba shi da yisti, domin an kore su daga Masar, ba su kuwa sami damar shirya wa kansu abinci ba.
40 So the dwelling of the children of Israel, while they dwelled in Egypt, was foure hundreth and thirtie yeres.
Zaman da Isra’ilawa suka yi a Masar, ya kai shekara 430.
41 And when the foure hundreth and thirtie yeeres were expired, euen the selfe same day departed all the hostes of the Lord out of the land of Egypt.
A ranar da shekara 430 ɗin nan suka cika, a ran nan ne dukan ɓangare-ɓangare na mutanen Ubangiji suka bar Masar.
42 It is a night to be kept holie to the Lord, because he brought them out of the lande of Egypt: this is that night of the Lord, which all the children of Israel must keepe throughout their generations.
Gama Ubangiji ya yi tsaro a wannan dare, domin yă fitar da su daga Masar, a wannan dare, dole dukan Isra’ilawa su yi tsaro, don su girmama Ubangiji, cikin dukan tsararraki masu zuwa.
43 Also the Lord said vnto Moses and Aaron, This is the Lawe of the Passeouer: no stranger shall eate thereof.
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Waɗannan ne ƙa’idodin Bikin Ƙetarewa. “Ba baƙon da zai ci shi.
44 But euerie seruant that is bought for money, when thou hast circumcised him, then shall he eat thereof.
Duk bawan da kuka sayo, yana iya ci, in dai an yi masa kaciya,
45 A stranger or an hyred seruant shall not eat thereof.
amma wanda ba ya zama tare da ku na ɗinɗinɗin, da kuma wanda aka ɗauki hayansa, ba zai ci ba.
46 In one house shall it bee eaten: thou shalt carie none of ye flesh out of the house, neither shall ye breake a bone thereof.
“Dole a ci shi a cikin gida ɗaya; kada a kai naman waje. Kada a karya wani daga ƙasusuwansa.
47 All the Congregation of Israel shall obserue it.
Dole dukan taron jama’ar Isra’ila su yi bikin.
48 But if a stranger dwell with thee, and will obserue the Passeouer of the Lord, let him circumcise all the males, that belong vnto him, and then let him come and obserue it, and he shall be as one that is borne in the land: for none vncircumcised person shall eate thereof.
“Baƙon da yake zama tare da ku da yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi wa dukan mazan da suke cikin gidansa kaciya; sa’an nan ne zai iya yin abubuwa kamar haifaffen ɗan ƙasa.
49 One lawe shalbe to him that is borne in the land, and to the stranger that dwelleth among you.
Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta shafi ɗan ƙasa da kuma baƙon da yake zama a tsakaninku.”
50 Then all the children of Israel did as the Lord commanded Moses and Aaron: so did they.
Dukan Isra’ilawa suka yi na’am da shi, suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
51 And the selfe same day did the Lord bring the children of Israel out of the land of Egypt by their armies.
A wannan rana, Ubangiji ya fito da Isra’ilawa ɓangare-ɓangare daga Masar.

< Exodus 12 >