< Exodus 10 >

1 Againe the Lord saide vnto Moses, Goe to Pharaoh: for I haue hardened his heart, and the heart of his seruants, that I might worke these my miracles in the middes of his realme,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je wurin Fir’auna, gama na riga na taurare zuciyarsa da kuma zukatan fadawansa domin in aikata waɗannan mu’ujizai nawa a tsakiyarsu,
2 And that thou maist declare in the eares of thy sonne, and of thy sonnes sonne, what things I haue done in Egypt, and my miracles, which I haue done among them: that ye may knowe that I am the Lord.
don kuma ku gaya wa’ya’yanku da jikokinku yadda na tsananta wa Masarawa, da kuma yadda na aikata mu’ujizai a cikinsu, don ku sani ni ne Ubangiji.”
3 Then came Moses and Aaron vnto Pharaoh, and they said vnto him, Thus saith the Lord God of the Ebrewes, Howe long wilt thou refuse to humble thy selfe before me? Let my people goe, that they may serue me.
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce masa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, ‘Har yaushe za ka ƙi ƙasƙantar da kanka a gabana? Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
4 But if thou refuse to let my people go, beholde, to morowe will I bring grashoppers into thy coastes.
In ka ƙi ka bari su tafi, gobe zan aiko da fāra a ƙasarka.
5 And they shall couer the face of the earth, that a man can not see the earth: and they shall eate the residue which remaineth vnto you, and hath escaped from the haile: and they shall eate all your trees that bud in the fielde.
Za su rufe fuskar ƙasar, har da ba za a iya ganin ƙasa ba. Za su cinye ɗan sauran abin da ya rage muku daga ɓarnar ƙanƙara, za su cinye dukan itatuwan da suke girma a gonakinku.
6 And they shall fil thine houses, and all thy seruants houses, and the houses of all the Egyptians, as neither thy fathers, nor thy fathers fathers haue seene, since the time they were vpon the earth vnto this day. So he returned, and went out from Pharaoh.
Za su cika gidajenka, da na fadawanka, da na dukan Masarawa, abin da iyayenka da kakanninka ba su taɓa gani ba, tun daga ranar da suka sami kansu a duniya, har yă zuwa yau.’” Sa’an nan Musa ya juya, ya rabu da Fir’auna.
7 Then Pharaohs seruants saide vnto him, How long shall he be an offence vnto vs? let the men go, that they may serue the Lord their God: wilt thou first knowe that Egypt is destroyed?
Fadawan Fir’auna suka ce masa, “Har yaushe mutumin nan zai zama mana tarko? Ka bar mutanen su tafi domin su yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. Har yanzu ba ka san cewa Masar ta lalace ba?”
8 So Moses and Aaron were brought againe vnto Pharaoh, and he saide vnto them, Goe, serue the Lord your God, but who are they that shall goe?
Sa’an nan aka dawo da Musa da Haruna wurin Fir’auna. Sai ya ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada. Amma wa da wa za su tafi?”
9 And Moses answered, We will go with our yong and with our olde, with our sonnes and with our daughters, with our sheepe and with our cattell will we goe: for we must celebrate a feast vnto the Lord.
Musa ya amsa, “Za mu tafi tare da ƙanananmu, da tsofaffinmu, da’ya’yanmu maza da mata, da kuma garkunanmu na shanu da tumaki, gama dole ne mu yi bikin ga Ubangiji.”
10 And he said vnto them, Let the Lord so be with you, as I will let you goe and your children: beholde, for euill is before your face.
Fir’auna ya ce, “Ubangiji ya taimaka bisa ga niyyarku, amma matanku da ƙanananku ba za su tafi ba! A fili yake kuna da niyyar mugunta.
11 It shall not be so: nowe goe ye that are men, and serue the Lord: for that was your desire. Then they were thrust out from Pharaohs presence.
Sam! Wannan ba zai taɓa yiwu ba, sai ko maza kaɗai su tafi su yi wa Ubangiji sujada, gama abin da kuke so ke nan.” Sa’an nan aka kori Musa da Haruna daga gaban Fir’auna.
12 After, the Lord said vnto Moses, Stretch out thine hande vpon the lande of Egypt for the grashoppers, that they may come vpon the lande of Egypt, and eate all the herbes of the land, euen all that the haile hath left.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka a bisa Masar domin fāra su sauko bisa ƙasar, su ci duk abin da yake girma a gonaki, duk abin da ƙanƙara ta rage.”
13 Then Moses stretched foorth his rod vpon the lande of Egypt: and the Lord brought an East winde vpon the land all that day, and al that night: and in the morning the East wind brought the grashoppers.
Saboda haka Musa ya miƙa sandansa bisa Masar, Ubangiji kuwa ya sa iskar gabas ta hura a kan ƙasar dukan dare da kuma dukan yini. Da safe kuwa iskar ta kawo fāra;
14 So the grashoppers went vp vpon all the land of Egypt, and remained in all quarters of Egypt: so grieuous Grashoppers, like to these were neuer before, neither after them shalbe such.
suka mamaye ƙasar duka, suka sauka a ko’ina a ƙasar. Ba a taɓa ganin annobar fāra haka ba, ba kuwa za a ƙara ganin fāra kamar haka ba.
15 For they couered all the face of the earth, so that the lande was darke: and they did eate all the herbes of the lande, and all the fruites of the trees, which the haile had left, so that there was no greene thing left vpon the trees, nor among the herbes of the fielde throughout all the lande of Egypt.
Suka rufe ƙasar har ta zama baƙi. Suka cinye abin da ƙanƙara ta rage, kowane tsiron da yake girma a gonaki, da dukan’ya’yan itatuwa. Babu ɗanyen abin da ya ragu a kan itatuwa ko tsire-tsire a dukan ƙasar Masar.
16 Therefore Pharaoh called for Moses and Aaron in haste, and sayde, I haue sinned against the Lord your God, and against you.
Fir’auna ya kira Musa da Haruna da gaggawa ya ce, “Na yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, na kuma yi muku.
17 And nowe forgiue mee my sinne onely this once, and pray vnto the Lord your God, that hee may take away from me this death onely.
Yanzu ku gafarta mini zunubina a wannan karo, ku kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yă ɗauke wannan muguwar annoba daga gare ni.”
18 Moses then went out from Pharaoh, and prayed vnto the Lord.
Sai Musa ya bar Fir’auna ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
19 And the Lord turned a mightie strong West winde, and tooke away the grashoppers, and violently cast them into the red Sea, so that there remained not one grashopper in all the coast of Egypt.
Sai Ubangiji ya canja iska zuwa iska mai ƙarfi ta yamma wadda ta ɗibi fārar zuwa Jan Teku. Babu fāran da suka rage a wani wuri a Masar.
20 But the Lord hardened Pharaohs heart, and hee did not let the children of Israel goe.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba.
21 Againe ye Lord said vnto Moses, Stretch out thine hand toward heauen, that there may be vpon the lande of Egypt darkenesse, euen darkenesse that may be felt.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama domin a yi duhu a bisa Masar, duhun da za a iya taɓawa.”
22 Then Moses stretched forth his hande towarde heauen, and there was a blacke darkenesse in all the land of Egypt three daies.
Sai Musa ya miƙa hannunsa sama, aka kuma yi duhu baƙi ƙirin bisa dukan ƙasar Masar na kwana uku.
23 No man saw an other, neither rose vp from ye place where he was for three dayes: but all the children of Israel had light where they dwelt.
Ba wanda ya iya gani wani ko yă bar wurinsa na kwana uku. Amma dukan Isra’ilawa sun kasance da haske a inda suke zama.
24 The Pharaoh called for Moses and said, Go, serue the Lord: onely your sheepe and your cattel shall abide, and your children shall go with you.
Sai Fir’auna ya aika aka kira Musa, ya kuma ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji sujada. Matanku da yaranku ma za su iya tafiya tare da ku; sai dai ku bar garkunanku na shanu da tumaki.”
25 And Moses sayd, Thou must giue vs also sacrifices, and burnt offrings that wee may doe sacrifice vnto the Lord our God.
Amma Musa ya ce, “Dole ka bari mu kasance da hadayu, da kuma hadayu na ƙonawa waɗanda za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu.
26 Therefore our cattell also shall go with vs: there shall not an hoofe bee left, for thereof must we take to serue the Lord our God: neither doe wee knowe howe we shall serue the Lord, vntill we come thither.
Dole dabbobinmu ma su tafi tare da mu; ko kofato ma, ba za a bari a baya ba. A cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu yi wa Ubangiji Allahnmu sujada. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.”
27 (But the Lord hardened Pharaohs heart, and he would not let them goe)
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, har bai yarda yă sake su ba.
28 And Pharaoh sayde vnto him, Get thee from mee: looke thou see my face no more: for whensoeuer thou commest in my sight, thou shalt dye.
Fir’auna ya ce wa Musa, “Fita, ka ba ni wuri! Ka mai da hankali, kada ka ƙara bayyana a gabana, gama ran da ka sāke ganin fuskata, a ran nan za ka mutu.”
29 Then Moses said, Thou hast said well: from henceforth will I see thy face no more.
Musa ya amsa, “Madalla, kamar yadda ka faɗa, ba zan ƙara bayyana a gabanka ba.”

< Exodus 10 >