< Deuteronomy 30 >

1 Nowe when all these things shall come vpon thee, either the blessing or the curse which I haue set before thee, and thou shalt turne into thine heart, among all the nations whither the Lord thy God hath driuen thee,
Sa’ad da dukan albarku da la’anonin nan da na sa a gabanku suka zo muku, kuka kuma sa su a zuciya, a duk inda Ubangiji Allahnku ya watsar da ku a cikin al’ummai,
2 And shalt returne vnto the Lord thy God, and obey his voyce in all that I commaund thee this day: thou, and thy children with all thine heart and with all thy soule,
sa’ad da kuma ku da’ya’yanku kuka komo ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi biyayya da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, bisa ga kome da na umarce ku a yau,
3 Then the Lord thy God wil cause thy captiues to returne, and haue compassion vpon thee, and wil returne, to gather thee out of all the people, where the Lord thy God had scattered thee.
a sa’an nan ne Ubangiji Allahnku zai yi muku jinƙai, yă ji tausayinku, yă kuma sāke tattara ku daga dukan al’ummai inda ya warwatsa ku.
4 Though thou werest cast vnto the vtmost part of heauen, from thence will the Lord thy God gather thee, and from thence wil he take thee,
Ko da ma an kore ku zuwa ƙasa mafi nisa a ƙarƙashin sammai, daga can Ubangiji Allahnku zai tattara ku, yă dawo da ku.
5 And the Lord thy God will bring thee into the land which thy fathers possessed, and thou shalt possesse it, and he will shewe thee fauour, and will multiplie thee aboue thy fathers.
Zai dawo da ku zuwa ƙasar da take ta kakanninku, za ku kuwa mallake ta. Zai sa ku yi arziki, ku kuma yi yawa fiye da kakanninku.
6 And the Lord thy God will circumcise thine heart, and the heart of thy seede, that thou mayest loue the Lord thy God with all thine heart, and with al thy soule, that thou maiest liue.
Ubangiji Allahnku zai yi wa zukatanku kaciya da kuma zukatan zuriyarku, saboda ku ƙaunace shi da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, ku kuma rayu.
7 And the Lord thy God will lay all these curses vpon thine enemies, and on them, that hate thee, and that persecute thee.
Ubangiji Allahnku zai sa dukan waɗannan la’anoni a kan abokan gābanku waɗanda suke ƙinku, suke kuma tsananta muku.
8 Returne thou therefore, and obey the voyce of the Lord, and do all his commandements, which I commaund thee this day.
Za ku sāke yi wa Ubangiji biyayya, ku kuma bi dukan umarnan da nake ba ku a yau.
9 And the Lord thy God will make thee plenteous in euery worke of thine hande, in the fruite of thy bodie, and in the fruite of thy cattel, and in the fruite of the lande for thy wealth: for the Lord will turne againe, and reioyce ouer thee to do thee good, as he reioyced ouer thy fathers,
Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai mayar da ku masu arziki ƙwarai a cikin dukan aiki hannuwanku, da kuma cikin’ya’yanku, da’ya’yan shanunku, da kuma hatsin gonarku. Ubangiji zai sāke jin daɗinku yă sa ku yi arziki, kamar dai yadda ya ji daɗin kakanninku.
10 Because thou shalt obey the voyce of the Lord thy God, in keeping his comandements, and his ordinances, which are written in the booke of this Law, when thou shalt returne vnto the Lord thy God with all thine heart and with al thy soule.
In dai kuka yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma kiyaye umarnansa da ƙa’idodin da aka rubuta a wannan Littafin Doka, kuka juyo ga Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
11 For this commandement which I commande thee this day, is not hid from thee, neither is it farre off.
To, abin da nake umartanku a yau, ba mai wuya ba ne gare ku, ba kuma abin da ya fi ƙarfinku ba ne.
12 It is not in heauen, that thou shouldest say, Who shall go vp for vs to heauen, and bring it vs, and cause vs to heare it, that we may doe it?
Ba ya can sama, balle ku ce, “Wa zai hau sama yă kawo mana, yă kuma furta mana, don mu yi biyayya?”
13 Neither is it beyonde the sea, that thou shouldest say, Who shall go ouer the sea for vs, and bring it vs, and cause vs to heare it, that we may do it?
Ba kuwa yana gaba da teku ba, da za ku ce, “Wa zai haye tekun don yă kawo mana, yă kuma furta mana, don mu yi biyayya?”
14 But the word is very neere vnto thee: euen in thy mouth and in thine heart, for to do it.
A’a, kalmar tana nan dab da ku, tana cikin bakinku da cikin zuciyarku, don ku yi biyayya.
15 Beholde, I haue set before thee this day life and good, death and euill,
Ku duba, na sa a gabanku a yau, rai da wadata, mutuwa da kuma hallaka.
16 In that I commaund thee this day, to loue the Lord thy God, to walke in his wayes, and to keepe his commandements, and his ordinances, and his lawes, that thou mayest liue, and be multiplied, and that the Lord thy God may blesse thee in the land, whither thou goest to possesse it.
Gama na umarce ku a yau, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, don ku yi tafiya a hanyoyinsa, ku kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa da kuma dokokinsa, sa’an nan za ku rayu, ku kuma ƙaru, Ubangiji Allahnku kuwa zai albarkace ku a ƙasar da kuke shiga don ci gādonta.
17 But if thine heart turne away, so that thou wilt not obey, but shalt be seduced and worship other gods, and serue them,
Amma in zukatanku suka kangare, ba su kuwa yi biyayya ba, in kuma aka rinjaye ku don ku rusuna ga waɗansu alloli ku yi musu bauta,
18 I pronounce vnto you this day, that ye shall surely perish, ye shall not prolong your dayes in the lande, whither thou passest ouer Iorden to possesse it.
na furta muku yau cewa tabbatacce za a hallaka ku. Ba za ku zauna a ƙasar da kuke hayewa Urdun don ku shiga ku ci gādonta ba.
19 I call heauen and earth to recorde this day against you, that I haue set before you life and death, blessing and cursing. therefore chuse life, that both thou and thy seede may liue,
A wannan rana na kira bisa sama da ƙasa a matsayin shaidu a kanku, cewa na sa a gabanku rai da mutuwa, albarku da la’anoni. Yanzu sai ku zaɓi rai, saboda ku da’ya’yanku ku rayu
20 By louing the Lord thy God, by obeying his voyce, and by cleauing vnto him: for he is thy life, and the length of thy dayes: that thou mayest dwell in the lande which the Lord sware vnto thy fathers, Abraham, Izhak, and Iaakob, to giue them.
don kuma ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku saurari muryarsa, ku kuma manne masa. Gama Ubangiji shi ranku, zai kuwa ba ku shekaru masu yawa a ƙasar da ya rantse zai ba wa kakanninku, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.

< Deuteronomy 30 >