< 2 Samuel 11 >

1 And when the yeere was expired in the time when Kinges goe forth to battell, Dauid sent Ioab, and his seruantes with him, and all Israel, who destroyed the children of Ammon, and besieged Rabbah: but Dauid remayned in Ierusalem.
Da bazara, a lokacin da sarakuna sukan fita zuwa yaƙi, sai Dawuda ya aiki Yowab tare da mutanen sarki, da dukan Isra’ila. Suka je suka hallaka Ammonawa, suka kuma yi wa Rabba kwanton ɓauna. Amma Dawuda ya yi zamansa a Urushalima.
2 And when it was euening tide, Dauid arose out of his bed, and walked vpon the roofe of the Kings palace: and from the roofe he sawe a woman washing her selfe: and the woman was very beautifull to looke vpon.
Wata rana da yamma, Dawuda ya tashi daga gadonsa, ya zaga kewaye a rufin fadansa. Daga rufin ya ga wata mace tana wanka. Matar kyakkyawa ce ƙwarai.
3 And Dauid sent and inquired what woman it was: and one sayde, Is not this Bath-sheba the daughter of Eliam, wife to Vriah the Hittite?
Sai Dawuda ya aiki wani yă bincika ko wace ce ita, sai mutumin ya dawo ya ce, “Wannan ba Batsheba ba ce,’yar Eliyam matar Uriya, mutumin Hitti?”
4 Then Dauid sent messengers, and tooke her away: and she came vnto him and he lay with her: (now she was purified from her vncleannes) and she returned vnto her house.
Sa’an nan Dawuda ya aiki manzanni su kawo masa ita. Ta zo wurinsa shi kuma ya kwana da ita (A lokacin kuwa ta gama tsarkake kanta ke nan daga jinin haila.) Sa’an nan ta tafi gida.
5 And the woman conceiued: therefore shee sent and tolde Dauid, and sayd, I am with childe.
Matar ta yi ciki, ta kuwa aika wa Dawuda, tana cewa, “Ina da ciki.”
6 Then Dauid sent to Ioab, saying, Send me Vriah the Hittite. And Ioab sent Vriah to Dauid.
Saboda haka Dawuda ya aika saƙo wa Yowab ya ce, “Ka aiko mini da Uriya mutumin Hitti.” Yowab kuwa ya aika da shi wajen Dawuda.
7 And when Vriah came vnto him, Dauid demanded him how Ioab did, and howe the people fared, and how the warre prospered.
Da Uriya ya zo wurinsa, sai Dawuda ya tambaye shi lafiyar Yowab da sojojin, da kuma yaya yaƙin yake tafiya.
8 Afterward Dauid said to Vriah, Go downe to thine house, and wash thy feete. So Vriah departed out of the Kings palace, and the king sent a present after him.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa Uriya, “Gangara gidanka ka wanke ƙafafunka.” Saboda haka Uriya ya bar fadar, sarki kuma ya aika masa da kyauta.
9 But Vriah slept at the doore of the Kings palace with all the seruants of his lord, and went not downe to his house.
Amma Uriya ya kwanta a ƙofar fada tare da dukan bayin maigidansa, bai kuwa tafi gidansa ba.
10 Then they tolde Dauid, saying, Vriah went not downe to his house: and Dauid saide vnto Vriah, Commest thou not from thy iourney? why didst thou not go downe to thine house?
Da aka gaya wa Dawuda, “Uriya bai tafi gida ba,” sai Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Ba ka zo daga wuri mai nisa ba? Me ya sa ba ka je gida ba?”
11 Then Vriah answered Dauid, The Arke and Israel, and Iudah dwell in tents: and my lord Ioab and the seruants of my lord abide in the open fields: shall I then go into mine house to eate and drinke, and lie with my wife? by thy life, and by the life of thy soule, I will not do this thing.
Sai Uriya ya ce wa Dawuda, “Akwatin Alkawari, da Isra’ila, da Yahuda suna zama cikin tentuna, kuma maigidana Yowab da mutanen ranka yă daɗe suna a sansani a fili. Yaya zan je gidana in ci in sha in kuma kwana da matata? Muddin kana a raye, ba zan yi irin wannan abu ba!”
12 Then Dauid sayd vnto Vriah, Tary yet this day, and to morow I will send thee away. So Vriah abode in Ierusalem that day, and the morowe.
Sai Dawuda ya ce masa, “Ka ƙara dakata a nan kwana ɗaya, gobe kuwa in sallame ka.” Saboda haka Uriya ya dakata a Urushalima a ranar, da kuma ta biye.
13 Then Dauid called him, and hee did eate and drinke before him, and he made him drunke: and at euen he went out to lie on his couch with the seruants of his Lord, but went not downe to his house.
Dawuda ya gayyace shi, ya kuwa ci ya sha tare da shi, Dawuda ya sa ya bugu tilis. Amma da yamma Uriya ya koma ya kwanta a tabarmarsa cikin bayin maigidan sarki; bai je gida ba.
14 And on the morowe Dauid wrote a letter to Ioab, and sent it by the hand of Vriah.
Da safe Dawuda ya rubuta wa Yowab wasiƙa ya ba wa Uriya.
15 And he wrote thus in the letter, Put ye Vriah in the forefront of the strength of the battell, and recule ye backe from him, that he may be smitten, and die.
A ciki wasiƙar ya rubuta, “Tura Uriya a gaba inda yaƙi ya fi zafi. Sa’an nan ka janye daga gare shi don a buge shi yă mutu.”
16 So when Ioab besieged the citie, he assigned Vriah vnto a place, where he knewe that strong men were.
Saboda haka yayinda Yowab ya kai yaƙi kusa da birnin, sai tura Uriya a inda ya sani akwai jarumawan Ammon na gaske.
17 And the men of the citie came out, and fought with Ioab: and there fell of the people of the seruants of Dauid, and Vriah the Hittite also dyed.
Sa’ad da mutanen garin suka fito suka yaƙi Yowab, sai waɗansu mutane daga sojojin Dawuda suka mutu; Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.
18 Then Ioab sent and tolde Dauid all the things concerning the warre,
Yowab ya aika wa Dawuda cikakken labari batun yaƙin.
19 And he charged the messenger, saying, When thou hast made an ende of telling all the matters of the warre vnto the King,
Ya umarci manzon ya ce, “Da ka gama yin wa sarki wannan batun yaƙin,
20 And if the kings anger arise, so that he say vnto thee, Wherefore approched ye vnto the citie to fight? knewe ye not that they would hurle from the wall?
wataƙila sarki yă husata, yă tambaye ka, ‘Me ya sa kuka je kusa da birnin don ku yi yaƙi? Ba ku san cewa za su yi harbi daga katanga ba?
21 Who smote Abimelech sonne of Ierubesheth? did not a woman cast a piece of a milstone vpon him from the wall, and he died in Thebez? why went you nie the wall? Then say thou, Thy seruant Vriah the Hittite is also dead.
Wane ne ya kashe Abimelek ɗan Yerub-Beshet? Ba mace ce ta jefa dutsen niƙa a kansa daga katanga, ta haka ya mutu a Tebez ba? Me ya sa kuka je kurkusa da katangar?’ In ya tambaye ka wannan, sai ka ce masa, ‘Har bawanka Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.’”
22 So the messenger went, and came and shewed Dauid all that Ioab had sent him for.
Manzon ya tashi ya tafi, da ya iso kuwa sai ya gaya wa Dawuda dukan abin da Yowab ya aike shi yă faɗa.
23 And the messenger said vnto Dauid, Certainely the men preuailed against vs, and came out vnto vs into the field, but we pursued them vnto the entring of the gate.
Manzon ya ce wa Dawuda, “Mutanen sun sha kanmu suka fito suka yaƙe mu a fili, amma muka kore su har ƙofar birni.
24 But the shooters shot from ye wall against thy seruants, and some of the Kings seruants be dead: and thy seruant Vriah the Hittite is also dead.
Sa’an nan maharba suka yi ta harbi daga katanga har waɗansu mutanen sarki suka mutu. Ban da haka ma, Uriya mutumin Hitti bawan sarki ya mutu.”
25 Then Dauid said vnto the messenger, Thus shalt thou say vnto Ioab, Let not this thing trouble thee: for the sworde deuoureth one as well as another: make thy battell more strong against the citie and destroy it, and encourage thou him.
Dawuda ya ce wa manzon, “Ka gaya wa Yowab, ‘Kada ka bar wannan yă dame ka; yadda takobi ya lamushe wannan, haka zai lamushe wancan ma. Ku ƙara matsa wa garin lamba, ku hallaka shi.’ Ka faɗa haka don ka ƙarfafa Yowab.”
26 And when the wife of Vriah heard that her husband Vriah was dead, she mourned for her husband.
Da matar Uriya ta ji cewa mijinta ya mutu, sai ta yi makoki saboda shi.
27 So when the mourning was past, Dauid sent and tooke her into his house, and shee became his wife, and bare him a sonne: but ye thing that Dauid had done, displeased the Lord.
Bayan kwanakin makoki suka ƙare, Dawuda ya sa aka kawo ta gidansa, ta kuwa zama matarsa, ta kuma haifa masa ɗa. Sai dai abin da Dawuda ya yi bai gamshi Ubangiji ba.

< 2 Samuel 11 >