< 2 Kings 18 >

1 Now in the third yeere of Hoshea, sonne of Elah King of Israel, Hezekiah the sonne of Ahaz king of Iudah began to reigne.
A shekara ta uku ta mulkin Hosheya ɗan Ela sarkin Isra’ila, Hezekiya ɗan Ahaz sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 He was fiue and twentie yeere olde when he began to reigne, and reigned nine and twenty yeere in Ierusalem. His mothers name also was Abi the daughter of Zachariah,
Yana da shekara ashirin da biyar da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara ashirin da tara a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Abiya’yar Zakariya.
3 And he did vprightly in the sight of the Lord, according to all that Dauid his father had done.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda kakansa Dawuda ya yi.
4 He tooke away the hie places, and brake the images, and cut downe the groues, and brake in pieces the brasen serpent that Moses had made: for vnto those dayes the children of Israel did burne incense to it, and hee called it Nehushtan.
Ya kawar da masujadan kan tudu, ya farfasa keɓaɓɓun duwatsu, ya sassare ginshiƙan Ashera. Ya fashe macijin tagullan da Musa ya yi, gama har zuwa lokacin nan Isra’ilawa suna ƙona turare gare shi. (An ba shi suna Nehushtan.)
5 He trusted in the Lord God of Israel: so that after him was none like him among all the Kings of Iudah, neither were there any such before him.
Hezekiya ya dogara ga Ubangiji, Allah na Isra’ila. Ba a yi wani kamar sa ba cikin dukan sarakunan Yahuda; ko kafin shi, ko kuma bayansa.
6 For he claue to the Lord, and departed not from him, but kept his commandements, which the Lord had commanded Moses.
Ya manne wa Ubangiji, bai fasa binsa ba; ya yi biyayya da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa.
7 So the Lord was with him, and he prospered in all thinges, which he tooke in hande: also he rebelled against the King of Asshur, and serued him not.
Ubangiji kuma ya kasance tare da shi, ya yi nasara a duk abin da ya sa hannu. Ya yi tawaye ga sarkin Assuriya, ya ƙi yă bauta masa.
8 He smote the Philistims vnto Azzah, and the coastes thereof, from the watch towre vnto the defensed citie.
Daga hasumiya zuwa birni mai katanga, ya ci Filistiyawa da yaƙi, har zuwa Gaza da kewaye.
9 And in the fourth yere of King Hezekiah, (which was the seuenth yeere of Hoshea sonne of Elah King of Israel) Shalmaneser King of Asshur came vp against Samaria, and besieged it.
A shekara ta huɗu ta Hezekiya, wato, shekara ta bakwai ke nan ta mulkin Hosheya ɗan Ela sarkin Isra’ila; Shalmaneser Sarkin Assuriya ya tasam ma Samariya da yaƙi; ya kewaye ta.
10 And after three yeeres they tooke it, euen in the sixt yeere of Hezekiah: that is, the ninth yeere of Hoshea King of Israel was Samaria taken.
A ƙarshen shekara ta uku, Assuriyawa suka ci Samariya da yaƙi. An ci Samariya da yaƙi a shekara ta shida ta mulki Hezekiya, wanda ya zo daidai da shekara ta tara ta mulkin Hosheya sarkin Isra’ila.
11 Then the King of Asshur did carry away Israel vnto Asshur, and put them in Halah and in Habor, by the riuer of Gozan, and in the cities of the Medes,
Sarkin Assuriya ya kwashe Isra’ila zuwa Assuriya ya zaunar da su a Hala, da Gozan a kogin Habor da kuma garuruwan Medes.
12 Because they woulde not obey the voyce of the Lord their God, but transgressed his couenant: that is, all that Moses the seruant of the Lord had commanded, and would neyther obey nor doe them.
Wannan ya faru ne domin ba su yi biyayya ga Ubangiji Allahnsu ba, amma suka karya alkawarinsu; da dukan abin da Musa bawan Ubangiji ya umarta. Ba su saurari umarnin ba, balle su kiyaye su.
13 Moreouer, in the fourteenth yeere of King Hezekiah, Saneherib King of Asshur came vp against all the strong cities of Iudah, and tooke them.
A shekara ta goma sha huɗu ta mulkin sarkin Hezekiya, sai sarki Sennakerib sarkin Assuriya ya kai farmaki wa biranen Yahuda masu katanga ya kuma kama su.
14 Then Hezekiah King of Iudah sent vnto the King of Asshur to Lachish, saying, I haue offended: depart from me, and what thou layest vpon me, I wil beare it. And the King of Asshur appoynted vnto Hezekiah King of Iudah three hudreth talents of siluer, and thirty talets of golde.
Sai Hezekiya sarkin Yahuda ya aika saƙo ga sarkin Assuriya a Lakish cewa, “Na yi laifi, ka janye daga gare ni, zan kuma biya ka duk abin da ake bukata daga gare ni.” Sarkin Assuriya ya karɓi talenti ɗari uku na azurfa, da talenti talatin na zinariya daga hannun Hezekiya sarkin Yahuda.
15 Therefore Hezekiah gaue all the siluer that was found in the house of the Lord, and in the treasures of the Kings house.
Ya zama kuwa cewa, Hezekiya ya bayar da dukan azurfan da suke a haikalin Ubangiji da kuma a ma’ajin fadan sarki.
16 At the same season did Hezekiah pul off the plates of the doores of the Temple of the Lord, and the pillars (which the sayd Hezekiah King of Iudah had couered ouer) and gaue them to the King of Asshur.
A wannan lokaci ne Hezekiya sarkin Yahuda ya ɓaɓɓalle zinariyan da aka dalaye ƙofofi da madogaran ƙofofin haikalin Ubangiji, ya ba sarkin Assuriya.
17 And the King of Asshur sent Tartan, and Rab-saris, and Rabshakeh from Lachish to King Hezekiah with a great hoste against Ierusalem. And they went vp, and came to Ierusalem, and when they were come vp, they stood by the conduite of the vpper poole, which is by the path of the fullers fielde,
Sai sarkin Assuriya ya aika da babban shugaban sojojinsa, da shugaban dattawansa, da wakilinsa daga birnin Lakish tare da ƙungiyar sojoji masu yawa zuwa Urushalima domin su yaƙi Sarki Hezekiya. Da suka haura sai suka tsaya a wurin lambatun da yake kawo ruwa daga Tafkin Tudu, kusa da hanyar Filin Mai Wanki.
18 And called to the King. Then came out to them Eliakim the sonne of Hilkiah, which was steward of the house, and Shebnah the chanceller, and Ioah the sonne of Asaph the recorder.
Suka kira sarki, sai Eliyakim ɗan Hilkiya sarkin fada, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf marubuci suka je wurinsu.
19 And Rabshakeh sayde vnto them, Tell ye Hezekiah, I pray you, Thus saith the great King, euen the great King of Asshur, What confidence is this wherein thou trustest?
Jagoran dogarawan sarkin Assuriya ya ce musu, “Ku ce wa Hezekiya, “‘Ga abin da babban sarkin Assuriya ya ce, da wa kake taƙama?
20 Thou thinkest, Surely I haue eloquence, but counsell and strength are for the warre. On whom then doest thou trust, that thou rebellest against me?
Ka ce kana da dabara da ƙarfin soji, amma bagu kawai kake yi. Da wa ka dogara har da za ka yi mini tawaye?
21 Lo, thou trustest now in this broken staffe of reede, to wit, on Egypt, on which if a man leane, it will goe into his hand, and pearce it: so is Pharaoh king of Egypt vnto all that trust on him.
Na sani kana dogara da Masar, wadda take kamar karar masara, wadda in ka jingina a kai, za tă karye tă soki hannunka. Haka Fir’auna sarkin Masar yake ga dukan wanda ya dogara da shi.
22 But if ye say vnto me, We trust in the Lord our God, is not that he whose hie places, and whose altars Hezekiah hath taken away, and hath sayd to Iudah and Ierusalem, Ye shall worship before this altar in Ierusalem?
Sai ya ci gaba da cewa, in kuma ka ce mini “Muna dogara ga Ubangiji Allahnmu ne,” ba masujadansa da bagadansa ne Hezekiya ya ciccire, yana ce wa Urushalima da Yahuda, “Dole ku yi sujada a gaban wannan bagade a Urushalima”?
23 Now therefore giue hostages to my lord the King of Asshur, and I will giue thee two thousand horses, if thou be able to set riders vpon them.
“‘Yanzu, ka zo ku shirya da shugabana, sarkin Assuriya. Zan ba ka dawakai dubu biyu, in za ka sami mahayansu!
24 For how canst thou despise any captaine of the least of my masters seruants, and put thy trust on Egypt for charets and horsemen?
Yaya za ka yi tsayayya da mafi ƙanƙantan hafsan shugabana, ko da kana dogara da Masar don kekunan yaƙi da mahaya dawakai?
25 Am I now come vp without the Lord to this place, to destroy it? the Lord sayd to me, Goe vp against this land, and destroy it.
Ban da haka ma, kana gani cewa na zo in hallaka wannan wuri ne ba tare da na ji daga Ubangiji ba? Ubangiji da kansa ne ya ce da ni in kawo wa wannan ƙasa hari in hallaka ta.’”
26 Then Eliakim the sonne of Hilkiah, and Shebnah, and Ioah said vnto Rabshakeh, Speake I pray thee, to thy seruants in the Aramites language, for we vnderstand it, and talke not with vs in the Iewes tongue, in the audience of the people that are on the wall.
Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, da Shebna, da Yowa suka ce wa jagoran dakarun, “Muna roƙonka ka yi wa bayinka magana da harshen Arameyik da yake muna ji. Kada ka yi mana magana da Yahudanci domin kada mutanen da suke bisa katanga su ji!”
27 But Rabshakeh saide vnto them, Hath my master sent me to thy master and to thee to speake these words, and not to the men which sit on the wall, that they may eate their owne doung, and drinke their owne pisse with you?
Amma shugaban sojojin ya ce, “Ai, ba gare ku da sarkinku kaɗai ne shugabana ya aike ni ba. Amma har ga mutanen da suke zaune a kan katangar birnin, waɗanda za su ci kashinsu, su sha fitsarinsu!”
28 So Rabshakeh stoode and cryed with a loude voyce in the Iewes language, and spake, saying, Heare the wordes of the great King, of the king of Asshur.
Sai shugaban sojojin ya yi kira da Yahudanci ya ce, “Ku ji muryar babban sarki, sarkin Assuriya!
29 Thus sayth the King, Let not Hezekiah deceiue you: for he shall not be able to deliuer you out of mine hand.
Ga abin da sarki ya faɗa; kada ku bar Hezekiya yă ruɗe ku. Ba zai iya cetonku daga hannuna ba.
30 Neither let Hezekiah make you to trust in the Lord, saying, The Lord will surely deliuer vs, and this citie shall not be giuen ouer into the hand of the king of Asshur.
Kada ku yarda Hezekiya yă rinjaye ku cewa ku dogara ga Allah, sa’ad da ya ce da ku, ‘Ba shakka Ubangiji zai cece mu; yana ce da ku birnin nan ba zai faɗa a hannun sarkin Assuriya ba.’
31 Hearken not vnto Hezekiah: for thus saith the king of Asshur, Make appointment with me, and come out to me, that euery man may eate of his owne vine, and euery man of his owne figge tree, and drinke euery man of the water of his owne well,
“Kada ku saurari Hezekiya. Ga abin da sarkin Assuriya ya ce, ku shirya zaman lafiya da ni, ku fito zuwa wurina. Kowane ɗayanku kuwa zai ci’ya’yan inabinsa da’ya’yan ɓaurensa, yă kuma sha ruwa daga randarsa,
32 Till I come, and bring you to a land like your owne land, euen a land of wheate and wine, a land of bread and vineyardes, a lande of oliues oyle, and hony, that ye may liue and not die: and obey not Hezekiah, for he deceiueth you, saying, The Lord will deliuer vs.
har lokacin da zan zo in kwashe ku, in kai ku wata ƙasa mai kama da taku, ƙasa mai yalwar hatsi, da ruwan inabi, da abinci, da gonakin inabi, da itatuwan zaitun, da zuma, don ku rayu, kada ku mutu! “Kada ku saurari Hezekiya, don karya yake muku, sa’ad da ya ce, ‘Ubangiji zai cece mu.’
33 Hath any of the gods of the nations deliuered his lande out of the hand of the King of Asshur?
Akwai allahn wata al’ummar da ya taɓa ceton ƙasarsa daga hannun sarkin Assuriya?
34 Where is the god of Hamah, and of Arpad? where is the god of Sepharuaim, Hena and Iuah? how haue they deliuered Samaria out of mine hand?
Ina allolin Hamat da na Arfad? Ina allolin Sefarfayim, da na Hena, da na Iffa? Sun cece Samariya daga hannuna?
35 Who are they among all the gods of the nations, that haue deliuered their lande out of mine hand, that the Lord should deliuer Ierusalem out of mine hand?
Wanne a cikin dukan allolin ƙasashen nan ya iya ceton ƙasarsa da gare ni? Shugaban sojojin ya kuma ci gaba da cewa, ta yaya Ubangiji zai ceci Urushalima daga hannuna?”
36 But the people helde their peace, and answered not him a worde: for the Kings commandement was, saying, Answere ye him not.
Amma mutane suka yi shiru ba su amsa masa ba, domin sarki ya umarta cewa, “Kada ku amsa masa.”
37 Then Eliakim, the sonne of Hilkiah which was steward of the house, and Shebnah the chanceller, and Ioah the sonne of Asaph the recorder came to Hezekiah with their clothes rent, and tolde him the wordes of Rabshakeh.
Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, sarkin fada, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf, marubuci, suka je wurin Hezekiya da tufafinsu a kece, suka faɗa masa abin da shugaban sojojin ya faɗa.

< 2 Kings 18 >