< 2 Kings 17 >

1 In the twelft yeere of Ahaz King of Iudah began Hoshea the sonne of Elah to reigne in Samaria ouer Israel, and reigned nine yeeres.
A shekara ta goma sha biyu ta mulkin Ahaz sarkin Yahuda, Hosheya ɗan Ela ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki na shekara tara.
2 And he did euill in the sight of the Lord, but not as the Kinges of Israel, that were before him.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar na sarakunan Isra’ilan da suka riga shi ba.
3 And Shalmaneser king of Asshur came vp against him, and Hoshea became his seruant, and gaue him presents.
Shalmaneser sarkin Assuriya ya kawo wa Hosheya wanda dā abokin tarayyarsa ne, hari har Hosheya ya biya shi haraji.
4 And the King of Asshur founde treason in Hoshea: for he had sent messengers to So King of Egypt, and brought no present vnto the King of Asshur, as he had done yeerely: therfore the king of Asshur shut him vp, and put him in prison.
Amma sarkin Assuriya ya gane cewa Hosheya mai cin amana ne, gama ya aika da wakilai wurin So sarkin Masar, ya kuma daina aika wa sarkin Assuriya haraji yadda ya saba yi kowace shekara. Saboda haka Shalmaneser ya kama shi ya sa a kurkuku.
5 Then the king of Asshur came vp throughout all the lande, and went against Samaria, and besieged it three yeere.
Sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar Hosheya gaba ɗaya farmaki, ya kewaye Samariya na tsawon shekara uku.
6 In the ninth yeere of Hoshea, the King of Asshur tooke Samaria, and caryed Israel away vnto Asshur, and put them in Halah, and in Habor by the riuer of Gozan, and in the cities of the Medes.
A shekara ta tara ta sarautar Hosheya, sarkin Assuriya ya ci Samariya da yaƙi ya kuma kwashe Isra’ilawa zuwa Assuriya. Ya tsugunar da su a Hala, da a Gozan a bakin Kogin Habor da kuma a garuruwan Medes.
7 For when the children of Israel sinned against the Lord their God, which had brought them out of the land of Egypt, from vnder ye hand of Pharaoh king of Egypt, and feared other gods,
Duk wannan ya faru ne saboda Isra’ilawa sun yi wa Ubangiji Allahnsu zunubi, shi wanda ya fitar da su daga Masar daga ƙarƙashin ikon Fir’auna sarkin Masar. Sun yi wa waɗansu alloli sujada
8 And walked according to the facions of the Heathen, whom the Lord had cast out before the children of Israel, and after the maners of the Kings of Israel, which they vsed,
suka kuma bi gurbin al’umman da Ubangiji ya kora a gabansu, da kuma ayyukan da sarakuna Isra’ila suka gabatar.
9 And the children of Israel had done secretly things that were not vpright before the Lord their God, and throughout all their cities had built hie places, both from the tower of the watch, to the defensed citie,
Isra’ilawa a ɓoye sun aikata abubuwan da ba daidai ba ga Ubangiji Allahnsu. Tun daga hasumiyoyi har zuwa birane masu katanga, sun gina wa kansu wuraren sujada na tudu a dukan garuruwansu.
10 And had made them images and groues vpon euery hie hill, and vnder euery greene tree,
Suka kafa keɓaɓɓun duwatsu da kuma ginshiƙan Ashera a kowane tudu mai tsayi da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
11 And there burnt incense in all the hie places, as did the heathen, whom the Lord had taken away before them, and wrought wicked things to anger the Lord,
Suka ƙona turare a kan kowane tudu, kamar dai yadda al’umman da Ubangiji ya kora daga gabansu suka yi. Suka yi muguntan da ya sa Ubangiji ya yi fushi.
12 And serued idoles: whereof the Lord had sayd vnto them, Ye shall do no such thing,
Suka bauta wa gumaka, ko da yake Ubangiji ya ce, “Ba za ku yi wannan ba.”
13 Notwithstanding the Lord testified to Israel, and to Iudah by all the Prophets, and by all the Seers, saying, Turne from your euill wayes, and keepe my commandements and my statutes, according to all the Lawe, which I commanded your fathers, and which I sent to you by my seruants the Prophets.
Ubangiji ya yi wa Isra’ila da Yahuda kashedi ta bakin dukan annabawansa da kuma masu duba, cewa, “Ku juyo daga mugayen ayyukanku. Ku yi biyayya da umarnai da farillaina, bisa ga dukan Dokar da na dokaci kakanninku su bi, waɗanda na kuma bayar ta wurin bayina, annabawa.”
14 Neuerthelesse they would not obey, but hardened their neckes, like to the neckes of their fathers, that did not beleeue in the Lord their God.
Amma ba su saurare ni ba don sun kangare kamar kakanninsu, waɗanda ba su amince da Ubangiji Allahnsu ba.
15 And they refused his statutes and his couenant, that he made with their fathers, and his testimonies (wherewith he witnessed vnto them) and they followed vanitie, and became vaine, and followed the heathen that were round about them: concerning whome the Lord had charged them, that they should not do like them.
Suka yi watsi da farillansa da yarjejjeniyar da ya ƙulla da kakanninsu, da kuma kashedin da ya yi musu. Suka bi gumaka marasa amfani, wannan ya sa su ma kansu suka zama marasa amfani. Suka kwaikwayi sauran ƙasashen da suke kewaye da su, ko da yake Ubangiji ya umarce su cewa, “Kada ku yi rayuwa irin tasu,” suka kuwa yi abin da Ubangiji ya hana su.
16 Finally they left all the commandements of the Lord their God, and made them molten images, euen two calues, and made a groue, and worshipped all the hoste of heauen, and serued Baal.
Suka wofinta dukan umarnan Ubangiji Allahnsu, suka yi wa kansu gumakan zubi na siffar’yan maruƙa biyu, da kuma ginshiƙin Ashera. Suka rusuna wa rundunan taurari, suka kuma yi wa Ba’al sujada.
17 And they made their sonnes and their daughters passe thorowe the fire, and vsed witchcraft and inchantments, yea, solde them selues to doe euill in the sight of the Lord, to anger him.
Suka miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ta wuta. Suka yi duba, suka yi sihiri suka kuma ba da kansu ga mugunta a gaban Ubangiji; suka sa ya yi fushi.
18 Therefore the Lord was exceeding wroth with Israel, and put them out of his sight, and none was left but the tribe of Iudah onely.
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi ƙwarai da Isra’ila, ya kuma kawar da su daga gabansa. Kabilar Yahuda kaɗai aka bari,
19 Yet Iudah kept not the commandements of the Lord their God, but walked according to the facion of Israel, which they vsed.
ko Yahuda ma ba su kiyaye umarnan Ubangiji Allahnsu ba. Sun bi gurbin da Isra’ila ta kawo.
20 Therefore the Lord cast off all the seede of Israel, and afflicted them, and deliuered them into the handes of spoylers, vntill he had cast them out of his sight.
Saboda haka Ubangiji ya wofinta mutanen Isra’ila; ya azabtar da su, ya kuma ba da su a hannun masu kwasar ganima, sai da ya shafe su ƙaƙaf daga gabansa.
21 For he cut off Israel from the house of Dauid, and they made Ieroboam the sonne of Nebat King: and Ieroboam drewe Israel away from following the Lord, and made them sinne a great sinne.
Sa’ad da ya ware Isra’ila daga gidan Dawuda, sai suka naɗa Yerobowam ɗan Nebat sarki a kansu. Yerobowam ya rinjayi Isra’ila daga ƙin Ubangiji, ya sa suka aikata babban zunubi.
22 For the children of Israel walked in all the sinnes of Ieroboam, which he did, and departed not therefrom,
Isra’ila suka nace cikin dukan zunuban Yerobowam, ba su kuwa rabu da su ba
23 Vntill the Lord put Israel away out of his sight, as he had said by all his seruants the Prophets, and caryed Israel away out of their land to Asshur vnto this day.
har Ubangiji ya kawar da su daga gabansa, kamar yadda ya gargaɗe su ta bakin bayinsa annabawa. Saboda haka aka kwashi mutanen Isra’ila daga ƙasarsu zuwa bauta a Assuriya, har wa yau kuwa suna can.
24 And the King of Asshur brought folke from Babel, and from Cuthah, and from Aua, and from Hamath, and from Sepharuaim, and placed them in the cities of Samaria in steade of the children of Israel: so they possessed Samaria, and dwelt in the cities thereof.
Sarkin Assuriya ya kawo mutane daga Babilon, Kuta, Afa, Hamat da Sefarfayim ya zaunar da su a garuruwan Samariya don su maya gurbin Isra’ilawa. Suka mallaki Samariya suka kuma zauna a garuruwansu.
25 And at the beginning of their dwelling there, they feared not the Lord: therefore the Lord sent lions among them, which slewe them.
Sa’ad da suka fara zama a can, ba su bauta wa Ubangiji ba; saboda haka ya aika da zakoki a tsakaninsu suka karkashe waɗansu mutane.
26 Wherefore they spake to the King of Asshur, saying, The nations which thou hast remoued, and placed in the cities of Samaria, knowe not the maner of the God of the land: therefore he hath sent lions among them, and behold, they slay them, because they knowe not the maner of the God of the land.
Sai aka faɗa wa sarkin Assuriya cewa, “Mutanen da ka kwashe ka zaunar a garuruwan Samariya fa ba su san abin da allahn ƙasar yake bukata ba. Saboda haka allahn ƙasar ya tura zakoki a cikinsu, waɗanda suke karkashe su, domin mutanen ba su san abin da yake bukata ba.”
27 Then the King of Asshur commanded, saying, Carie thither one of the Priestes whome ye brought thence, and let him goe and dwell there, and teache them the maner of the God of the countrey.
Sai sarkin Assuriya ya ba da umarni cewa, “A sami wani daga cikin firistocin da aka kwaso zuwa bauta daga Samariya, yă koma yă zauna a can, yă koya wa mutanen abin da allahn ƙasar yake bukata.”
28 So one of the Priestes, which they had caryed from Samaria, came and dwelt in Beth-el, and taught them how they shoulde feare the Lord.
Saboda haka ɗaya daga cikin firistocin da aka kawo bauta daga Samariya ya dawo ya zauna a Betel, ya koya musu yadda za su yi sujada ga Ubangiji.
29 Howbeit euery nation made their gods, and put them in the houses of the hie places, which the Samaritanes had made, euery nation in their cities, wherein they dwelt.
Duk da haka, jama’ar kowace ƙasa, suka ƙera tasu alloli a garuruwa masu yawa inda suke zaune, suka sa su a masujadan da mutanen Samariya suka gina a kan tuddai.
30 For the men of Babel made Succoth-Benoth: and the men of Cuth made Nergal, and the men of Hamath made Ashima,
Mutane daga Babilon suka ƙera Sukkot Benot, mutane daga Kut suka ƙera Nergal, mutane daga Hamat suka ƙera Ashima;
31 And the Auims made Nibhaz, and Tartak: and the Sepharuims burnt their children in the fire to Adrammelech, and Anammelech the gods of Sepharuaim.
Awwiyawa suka ƙera Nibhaz da Tartak, Sefarfayawa kuwa suka ƙone’ya’yansu a wuta a matsayi hadayu ga Adrammelek da Anammelek allolin Sefarfayim.
32 Thus they feared the Lord, and appoynted out Priestes out of them selues for the hie places, who prepared for them sacrifices in the houses of the hie places.
Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma suka zaɓi mutanensu su yi musu hidima a matsayin firistoci a masujadan da suke kan tuddai.
33 They feared the Lord, but serued their gods after the maner of the nations whome they caryed thence.
Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma sun bauta wa allolinsu bisa ga al’adun ƙasashen da suka fito.
34 Vnto this day they doe after the olde maner: they neyther feare God, neyther doe after their ordinances, nor after their customes, nor after the Lawe, nor after the commandement, which the Lord commanded the children of Iaakob, whom he named Israel,
Har yă zuwa yau, sun nace da ayyukansu na dā. Ba sa yin wa Ubangiji sujada, ba sa kuma bin dokoki da farillansa, dokoki da umarnan da Ubangiji ya ba wa zuriyar Yaƙub, wadda ya ba wa suna Isra’ila.
35 And with whom the Lord had made a couenant, and charged them, saying, Feare none other gods, nor bowe your selues to them, nor serue them, nor sacrifice to them:
Da Ubangiji ya ƙulla alkawari da Isra’ilawa, ya dokace su cewa, “Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada ko ku durƙusa a gabansu ku bauta musu, ko ku miƙa musu hadaya.
36 But feare the Lord which brought you out of the land of Egypt with great power, and a stretched out arme: him feare ye, and worshippe him, and sacrifice to him.
Amma Ubangiji wanda ya fito da ku daga Masar da iko mai girma da hannu mai ƙarfi, shi ne za ku yi masa sujada. Gare shi za ku durƙusa ku kuma miƙa masa hadayu.
37 Also keepe ye diligently the statutes and the ordinances, and the Lawe, and the commandement, which he wrote for you, that ye do them continually, and feare not other gods.
Dole kullum ku mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da farillan, dokoki da umarnan da ya rubuta muku. Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada.
38 And forget not the couenant that I haue made with you, neither feare ye other gods,
Kada ku manta da alkawarin da na ƙulla da ku, kada ku yi sujada ga waɗansu alloli.
39 But feare the Lord your God, and he will deliuer you out of the handes of all your enemies.
Maimakon haka, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada; shi ne zai cece ku daga hannun abokan gābanku.”
40 Howbeit they obeyed not, but did after their olde custome.
Amma ba su saurara ba, suka nace da ayyukansu na dā.
41 So these nations feared the Lord, and serued their images also: so did their children, and their childrens children: as did their fathers, so do they vnto this day.
Ko ma yayinda mutanen nan suke yi wa Ubangiji sujada, ba su daina bauta wa gumakansu ba. Har yă zuwa yau,’ya’yansu da jikokinsu sun ci gaba da bin gurbin kakanninsu.

< 2 Kings 17 >