< 2 Kings 16 >

1 The seuenteenth yeere of Pekah the sonne of Remaliah, Ahaz the sonne of Iotham King of Iudah began to reigne.
A shekara ta goma sha bakwai ta mulkin Feka ɗan Remaliya, Ahaz ɗan Yotam sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Twentie yeere olde was Ahaz, when hee began to reigne, and he reigned sixteene yeere in Ierusalem, and did not vprightly in the sight of the Lord his God, like Dauid his father:
Ahaz ya zama sarki yana da shekara ashirin, ya kuma yi mulki shekara goma sha shida a Urushalima ba kamar Dawuda mahaifinsa ba. Ahaz bai yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji Allahnsa ba.
3 But walked in the way of ye kings of Israel, yea, and made his sonne to go through the fire, after the abominations of the heathen, whom the Lord had cast out before the children of Israel.
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila har ya miƙa ɗansa hadaya a wuta, yana bin hanyoyin banƙyama na al’ummai da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
4 Also he offred and burnt incense in the hie places and on the hilles, and vnder euery greene tree.
Ya miƙa hadaya, ya kuma ƙona turare a masujadan tudu, da kan tuddai, da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
5 Then Rezin king of Aram and Pekah sonne of Remaliah King of Israel came vp to Ierusalem to fight: and they besieged Ahaz, but could not ouercome him.
Sai Rezin sarkin Aram, da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su kai wa Urushalima hari, suka kuma kewaye Ahaz, amma ba su iya shan ƙarfinsa ba.
6 At the same time Rezin king of Aram restored Elath to Aram, and droue the Iewes from Elath: so the Aramites came to Elath, and dwelt there vnto this day.
A wannan lokaci, Rezin sarkin Aram ya sāke ƙwato Elat wa Aram ta wurin korar Yahuda. Sa’an nan mutanen Edom suka mamaye Elat suna kuwa zaune a can har yau.
7 Then Ahaz sent messengers to Tiglath Pileser king of Asshur, saying, I am thy seruant and thy sonne: come vp, and deliuer me out of the hand of the king of Aram, and out of the hand of the King of Israel which rise vp against me.
Ahaz ya aika a faɗa wa Tiglat-Fileser sarkin Assuriya cewa, “Ni abokin tarayyarka ne kuma mai dogara da kai. Ka haura ka cece ni daga hannun sarkin Aram da hannun sarkin Isra’ila waɗanda suke kawo mini hari.”
8 And Ahaz tooke the siluer and the golde that was found in the house of the Lord, and in the treasures of the Kings house, and sent a present vnto the King of Asshur.
Ahaz ya ɗauki azurfa da zinariyar da suke a haikalin Ubangiji da suke kuma a ma’ajin fada ya aika wa sarkin Assuriya kyauta.
9 And the King of Asshur consented vnto him: and the King of Asshur went vp against Damascus. and when he had taken it, he caryed the people away to Kir, and slew Rezin.
Sai sarkin Assuriya ya ji roƙonsa. Ya tashi ya fāɗa wa Damaskus da hari ya kuma kame ta. Ya kwashi mazaunanta zuwa Kir, ya kuma kashe Rezin.
10 And King Ahaz went vnto Damascus to meete Tiglath Pileser King of Asshur: and when King Ahaz sawe the altar that was at Damascus, he sent to Vriiah the Priest the paterne of the altar, and the facion of it, and all the workemanship thereof.
Sa’an nan sarki Ahaz ya tafi Damaskus don yă sadu da Tiglat-Fileser sarkin Assuriya. Da ya kai can sai ya ga wani bagade a Damaskus, sai ya aika wa Uriya firist, da siffar bagaden, da fasalinsa, da cikakken bayanin bagaden.
11 And Vriiah the Priest made an altar in al poyntes like to that which King Ahaz had sent from Damascus, so did Vriiah the Priest against King Ahaz came from Damascus.
Saboda haka Uriya firist ya gina bagaden bisa ga tsarin da Sarki Ahaz ya aika masa daga Damaskus, ya kuma gama shi kafin Sarki Ahaz yă dawo.
12 So when the King was come from Damascus, the King sawe the altar: and the King drewe neere to the altar and offered thereon.
Da sarki ya dawo daga Damaskus ya ga bagaden, sai ya tafi kusa da shi ya kuma miƙa hadaya a bisansa.
13 And hee burnt his burnt offering, and his meate offring, and powred his drinke offring, and sprinkled the blood of his peace offrings besides the altar,
Ya miƙa hadayarsa ta ƙonawa da ta hatsi, ya zuba hadayarsa ta sha, ya kuma yayyafa jinin hadayunsa ta zumunci a bisa bagaden.
14 And set it by the brasen altar which was before the Lord, and brought it in farther before the house betweene the altar and the house of the Lord, and set it on the North side of the altar.
Sai ya cire bagaden tagulla wanda aka keɓe ga Ubangiji, ya sa shi a gaban haikalin wato, tsakanin ƙofar shiga haikalin Ubangiji da sabon bagaden. Ya ajiye shi a gefen arewa na sabon bagaden.
15 And King Ahaz commanded Vriiah the Priest, and sayde, Vpon the great altar set on fire in the morning the burnt offring, and in the euen the meate offring, and the Kings burnt offring and his meate offering, with the burnt offring of all the people of the lande, and their meate offring, and their drinke offrings: and powre thereby all the blood of the burnt offring, and all the blood of the sacrifice, and the brasen altar shalbe for me to inquire of God.
Sarkin Ahaz ya umarci Uriya cewa, “A kan babban sabon bagade, ka miƙa hadayar ƙonawa ta safe, da hadayar hatsi ta yamma, da hadayar sarki ta ƙonawa da hadayarsa ta hatsi, da hadaya ta dukan jama’ar ƙasar, tare da hadayan hatsinsu da kuma ta sha. Ka yayyafa jinin hadayun ƙonawa a kan bagade. Amma zan yi amfani da bagaden tagulla don neman bishewa.”
16 And Vriiah the Priest did according to all that King Ahaz had commanded.
Uriya firist kuwa ya yi duk abin da Sarki Ahaz ya umarta.
17 And King Ahaz brake the borders of the bases, and tooke the caldrons from off them, and tooke downe the sea from the brasen oxen that were vnder it, and put it vpon a pauement of stones.
Sarkin Ahaz ya kawar da katakon ya kuma ɗauke tasoshin daga mazauninsu da ake iya matsarwa. Ya ɗauke ƙaton kwano mai suna Teku daga kan bijiman tagullar da ya tallafe su ya ajiye a kan mazaunin dutse.
18 And the vaile for the Sabbath (that they had made in the house) and the Kings entrie without turned he to the house of the Lord, because of the King of Asshur.
Ya kawar da rumfa Asabbacin da aka gina a haikalin, ya kuma kawar da mashigin sarki na waje da haikalin Ubangiji, duk dai don yă gamshi sarkin Assuriya.
19 Concerning the rest of the actes of Ahaz, which he did, are they not written in the booke of the Chronicles of the Kings of Iudah?
Game da sauran ayyukan mulkin Ahaz, abubuwan da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
20 And Ahaz slept with his fathers, and was buryed with his fathers in the citie of Dauid, and Hezekiah his sonne reigned in his steade.
Ahaz ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi da su a Birnin Dawuda. Hezekiya ɗansa kuma ya gāje shi.

< 2 Kings 16 >