< 2 Chronicles 25 >

1 Amaziah was fiue and twentie yere old when he began to reigne, and he reigned nine and twentie yeere in Ierusalem: and his mothers name was Iehoaddan, of Ierusalem.
Amaziya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin ce; ita daga Urushalima ne.
2 And he did vprightly in the eyes of the Lord, but not with a perfite heart.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, amma ba da dukan zuciyarsa ba.
3 And when the kingdome was established vnto him, he slewe his seruants, that had slaine the King his father.
Bayan sarauta ta kahu a ƙarƙashinsa, sai ya kashe hafsoshin da suka kashe mahaifinsa sarki.
4 But he slewe not their children, but did as it is written in the Lawe, and in the booke of Moses, where the Lord commanded, saying, The fathers shall not dye for the children, neyther shall the children die for the fathers, but euery man shall dye for his owne sinne.
Duk da haka bai kashe’ya’yansu maza ba amma ya yi bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Doka, a cikin Littafin Musa, inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda’ya’yansu ba; ba kuwa za a kashe’ya’ya saboda iyayensu ba; kowa zai mutu saboda zunubansa ne.”
5 And Amaziah assembled Iudah, and made them captaines ouer thousandes, and captaines ouer hundreths, according to the houses of their fathers, thorowout all Iudah and Beniamin: and he nombred them from twentie yeere olde and aboue, and founde among them three hundreth thousand chosen men, to goe foorth to the warre, and to handle speare and shield.
Amaziya ya tattara mutanen Yahuda ya kuma ba su aiki bisa ga iyalansu, ya ba da aiki ga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, a dukan Yahuda da Benyamin. Ya kuma tattara waɗanda suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye ya sami mutane dubu ɗari uku da suke a shirye don aikin soja, da suka isa riƙe māshi da garkuwa.
6 He hyred also an hundreth thousand valiant men out of Israel for an hundreth talents of siluer.
Ya kuma ɗauko sojan haya jarumawa dubu ɗari ɗaya daga Isra’ila a kan talenti ɗari na azurfa.
7 But a man of God came to him, saying, O King, let not the armie of Israel goe with thee: for the Lord is not with Israel, neither with all the house of Ephraim.
Amma mutumin Allah ya zo wurinsa ya ce, “Ya sarki, waɗannan runduna daga Isra’ila ba za su tafi tare da kai ba, gama Ubangiji ba ya tare da Isra’ila, ba ya nan da wani cikin mutanen Efraim.
8 If not, goe thou on, doe it, make thy selfe strong to the battel, but God shall make thee fall before the enemie: for God hath power to helpe, and to cast downe.
Ko da ma ya tafi ya yi faɗa da ƙwazo a cikin yaƙi, Allah zai tumɓuke shi a gaban abokan gāba, gama Allah yana da iko yă taimaka ko yă tumɓuke.”
9 And Amaziah sayde to the man of God, What shall we doe then for the hundreth talents, which I haue giuen to the hoste of Israel? Then the man of God answered, The Lord is able to giue thee more then this.
Amaziya ya tambayi mutumin Allah ya ce, “Amma game da talenti ɗarin da na biya saboda waɗannan rundunonin Isra’ila fa?” Mutumin Allah ya amsa, “Ubangiji zai ba ka fiye da wannan.”
10 So Amaziah separated them, to wit, the armie that was come to him out of Ephraim, to returne to their place: wherefore their wrath was kindled greatly against Iudah, and they returned to their places with great anger.
Saboda haka Amaziya ya sallame rundunonin da suka zo daga Efraim, ya kuma mayar da su gida. Suka husata da Yahuda suka koma gida da fushi sosai.
11 Then Amaziah was encouraged, and led forth his people, and went to the salt valley, and smote of the children of Seir, ten thousand.
Sa’an nan Amaziya ya yi ƙarfin hali ya jagoranci mayaƙansa zuwa Kwarin Gishiri, inda ya kashe mutanen Seyir dubu goma.
12 And other ten thousand did the children of Iudah take aliue, and caryed them to the top of a rocke, and cast them downe from the top of the rocke, and they all burst to pieces.
Mayaƙan Yahuda suka kuma kama mutane dubu goma da rai, suka ɗauke su zuwa ƙwanƙolin dutsen, suka yi ta tunkuɗa su ƙasa suka yi kaca-kaca.
13 But the men of the armie, which Amaziah sent away, that they should not goe with his people to battell, fell vpon the cities of Iudah from Samaria vnto Beth-horon, and smote three thousand of them, and tooke much spoyle.
Ana cikin haka, sai rundunar da Amaziya ya mai da su gida, waɗanda ba a bari suka tafi yaƙin ba, suka kai wa garuruwan Yahuda daga Samariya zuwa Bet-Horon hari. Suka kashe mutane dubu uku suka kwashe ganima mai yawan gaske.
14 Now after that Amaziah was come from the slaughter of the Edomites, he brought the gods of the children of Seir, and set them vp to be his gods, and worshipped them, and burned incense vnto them.
Da Amaziya ya dawo daga kisan mutanen Edom, sai ya dawo da allolin mutanen Seyir. Ya kafa su a matsayin allolinsa, ya rusuna musu, ya kuma miƙa musu hadayun ƙonawa.
15 Wherefore the Lord was wroth with Amaziah, and sent vnto him a Prophet, which sayd vnto him, Why hast thou sought the gods of the people, which were not able to deliuer their owne people out of thine hand?
Fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan Amaziya, sai ya aiki wani annabi wurinsa wanda ya ce, “Me ya sa ka nemi shawarar allolin mutanen nan, waɗanda ba za su cece mutanensu daga hannunka ba?”
16 And as he talked with him, he said vnto him, Haue they made thee the Kings counseler? cease thou: why should they smite thee? And the Prophet ceased, but said, I knowe that God hath determined to destroy thee, because thou hast done this, and hast not obeyed my counsell.
Tun yana cikin magana, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Rufe mana baki! Me zai hana a kashe ka?” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”
17 Then Amaziah King of Iudah tooke counsell, and sent to Ioash the sonne of Iehoahaz, the sonne of Iehu King of Israel, saying, Come, let vs see one another in the face.
Bayan Amaziya sarkin Yahuda ya nemi shawara mashawartansa, sai ya kalubalanci Yowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, “Zo mu gamu fuska da fuska.”
18 But Ioash King of Israel sent to Amaziah King of Iudah, saying, The thistle that is in Lebanon, sent to the cedar that is in Lebanon, saying, Giue thy daughter to my sonne to wife: and the wilde beast that was in Lebanon went and trode downe the thistle.
Amma Yowash sarkin Isra’ila ya amsa wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata ƙaya ce a Lebanon, ta aika da saƙo wa itacen al’ul na Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Sai wani naman jeji na Lebanon ya zo ya tattake ƙayar.
19 Thou thinkest: lo, thou hast smitten Edom, and thine heart lifteth thee vp to bragge: abide now at home: why doest thou prouoke to thine hurt, that thou shouldest fall, and Iudah with thee?
Ka ce wa kanka cewa ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana fariya da ɗaga kai. Amma tsaya dai a gida! Me ya sa kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da ta Yahuda?”
20 But Amaziah would not heare: for it was of God, that he might deliuer them into his had, because they had sought the gods of Edom.
Amma Amaziya bai saurara ba gama Allah ya yi haka domin yă miƙa su ga Yehowash, domin sun nemi shawarar allolin Edom.
21 So Ioash the King of Israel went vp: and he, and Amaziah King of Iudah saw one another in the face at Bethshemesh, which is in Iudah.
Saboda haka Yowash sarkin Isra’ila ya kai yaƙi. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh a Yahuda.
22 And Iudah was put to the worse before Israel, and they fled euery man to his tents.
Isra’ila ta fatattaki Yahuda, sai kowane mutum ya gudu zuwa gidansa.
23 But Ioash the King of Israel tooke Amaziah King of Iudah, the sonne of Ioash, the sonne of Iehoahaz in Bethshemesh, and brought him to Ierusalem, and brake downe the wall of Ierusalem, from the gate of Ephraim vnto the corner gate, foure hundreth cubites.
Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya kawo shi Urushalima ya farfasa katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, wani sashe mai tsawon ƙafa ɗari shida.
24 And he tooke all the gold and the siluer, and all the vessels that were found in the house of God with Obed Edom, and in the treasures of the Kings house, and the children that were in hostage, and returned to Samaria.
Ya kwashe dukan zinariya da azurfa da dukan kayayyakin da aka samu a haikalin Allah waɗanda suke a ƙarƙashin kulawar Obed-Edom, da kaya masu daraja na gidan sarki, da waɗanda aka kamo cikin yaƙi, ya kawo Samariya.
25 And Amaziah the sonne of Ioash King of Iudah liued after the death of Ioash sonne of Iehoahaz King of Israel, fifteene yeere.
Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya rayu shekara goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
26 Concerning the rest of the actes of Amaziah first and last, are they not written in the booke of the Kings of Iudah and Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
27 Nowe after the time that Amaziah did turne away from ye Lord, they wrought treason against him in Ierusalem: and when he was fled to Lachish, they sent to Lachish after him, and slewe him there.
Sa’ad da Amaziya ya bar bin Ubangiji, aka shirya masa maƙarƙashiya a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma suka aiki mutane suka bi shi zuwa Lakish, a can suka kashe shi.
28 And they brought him vpon horses, and buried him with his fathers in the citie of Iudah.
Aka dawo da shi a kan doki, aka binne shi tare da kakanninsa a Birnin Yahuda.

< 2 Chronicles 25 >