< 2 Chronicles 18 >

1 And Iehoshaphat had riches and honour in abundance, but he was ioyned in affinitie with Ahab.
Yanzu fa Yehoshafat ya wadace ƙwarai yana kuma da girma, ya kuma haɗa kansa da Ahab ta wurin aure.
2 And after certaine yeeres he went downe to Ahab to Samaria: and Ahab slew sheepe and oxen for him in great nomber, and for the people that he had with him, and entised him to goe vp vnto Ramoth Gilead.
Bayan’yan shekaru sai ya gangara don yă ziyarci Ahab a Samariya. Ahab kuwa ya yanka tumaki da shanu masu yawa dominsa da kuma mutanen da suke tare da shi, ya kuma lallashe shi yă yaƙi Ramot Gileyad.
3 And Ahab King of Israel saide vnto Iehoshaphat King of Iudah, Wilt thou goe with mee to Ramoth Gilead? And hee answered him, I am as thou art, and my people as thy people, and wee will ioyne with thee in the warre.
Ahab sarkin Isra’ila ya tambayi Yehoshafat sarkin Yahuda ya ce, “Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Ramot Gileyad?” Yehoshafat ya amsa ya ce, “Ni kamar kai ne, kuma mutanena kamar naka ne; za mu tafi tare da kai a yaƙin.”
4 And Iehoshaphat sayde vnto the King of Israel, Aske counsel, I pray thee, at the worde of the Lord this day.
Amma Yehoshafat ya kuma ce wa sarkin Isra’ila, “Da fari mu nemi bishewar Ubangiji.”
5 Therefore the King of Israel gathered of Prophets foure hundreth men, and sayde vnto them, Shall we goe to Ramoth Gilead to battel, or shall I cease? And they sayd, Go vp: for God shall deliuer it into the Kings hand.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya tattara annabawa duka, mutane ɗari huɗu, ya kuma tambaye su, “Mu tafi yaƙi a kan Ramot Gileyad ko kada mu tafi?” Suka amsa “Tafi, gama Allah zai ba da shi cikin hannun sarki.”
6 But Iehoshaphat sayde, Is there heere neuer a Prophet more of the Lord that wee might inquire of him?
Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu tambaya?”
7 And the King of Israel sayd vnto Iehoshaphat, There is yet one man, by whome wee may aske counsell of the Lord, but I hate him: for he doeth not prophesie good vnto me, but alway euil: it is Michaiah the sonne of Imla. Then Iehoshaphat said, Let not the King say so.
Sarki Isra’ila ya amsa wa Yehoshafat, “Akwai guda har yanzu mai suna Mikahiya ɗan Imla, za mu iya nemi nufin Ubangiji daga gare shi, sai dai ba na sonsa domin bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni ba, sai kullum masifa.” Yehoshafat ya amsa ya ce, “Kada sarki yă faɗa haka.”
8 And the King of Israel called an eunuche, and said, Call quickly Michaiah the sonne of Imla.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya kira ɗaya daga cikin ma’aikatansa ya ce, “A kawo Mikahiya ɗan Imla nan da nan.”
9 And the King of Israel, and Iehoshaphat King of Iudah sate either of them on his throne clothed in their apparel: they sate euen in the threshing floore at the entring in of the gate of Samaria: and all the Prophets prophesied before them.
Saye da rigunan sarakuna, sarki Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suna zaune a kan kujerunsu na mulki a masussuka ta ƙofar shigar Samariya, tare da dukan annabawa suna ta annabci a gabansu.
10 And Zidkiah ye sonne of Chenaanah made him hornes of yron, and sayde, Thus sayth the Lord, With these shalt thou push the Aramites vntill thou hast consumed them.
To, fa, Zedekiya ɗan Kena’ana ya yi ƙahonin ƙarfe, ya kuma furta, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan za ka sassoki Arameyawa sai sun hallaka.’”
11 And all the Prophets prophesied so, saying, Go vp to Ramoth Gilead, and prosper: for the Lord shall deliuer it into the hand of the King.
Dukan sauran annabawan suka yi irin annabcin nan. Suka ce, “A haura zuwa Ramot Gileyad a yi nasara, gama Ubangiji zai ba da shi cikin hannun sarki.”
12 And the messenger that went to call Michaiah, spake to him, saying, Beholde, the wordes of the Prophets declare good to the King with one accord: let thy word therefore, I pray thee, be like one of theirs, and speake thou good.
Ɗan saƙon da ya tafi don yă kawo Mikahiya kuwa ya ce masa, “Duba, kowannen a cikin annabawa ya yi faɗin nasara wa sarki. Don haka kai ma ka yi maganar da za tă gamshi sarki kamar yadda suka yi.”
13 And Michaiah saide, As the Lord liueth, whatsoeuer my God saith, that will I speake.
Amma Mikahiya ya ce, “Na rantse da ran Ubangiji, zan faɗa masa kawai abin da Allahna ya faɗa.”
14 So he came to the King, and the King said vnto him, Michaiah, shall we go to Ramoth Gilead to battel, or shall I leaue off? And he said, Goe yee vp, and prosper, and they shalbe deliuered into your hand.
Da suka iso, sarki ya tambaye shi, “Mika, mu tafi mu yaƙi Ramot Gileyad, ko kada mu tafi?” Ya amsa, “Kai masa yaƙi za ka kuwa yi nasara, gama za a ba da su a hannunka.”
15 And the King sayd to him, Howe oft shall I charge thee, that thou tell mee nothing but the trueth in the Name of the Lord?
Sarki ya ce masa, “Sau nawa zan sa ka rantse don ka faɗa gaskiya a cikin sunan Ubangiji?”
16 Then he said, I saw al Israel scattered in the mountaines, as sheepe that haue no shepheard: and the Lord sayd, These haue no Master: let them returne euery man to his house in peace.
Sa’an nan Mikahiya ya amsa, “Na ga dukan Isra’ila sun warwatsu a kan tuddai kamar tumakin da ba su da makiyaya, kuma Ubangiji ya ce, ‘Waɗannan mutane ba su da maigida. Bari kowanne yă tafi gida cikin salama.’”
17 And the King of Israel sayde to Iehoshaphat, Did I not tell thee, that he would not prophesie good vnto me, but euill?
Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Ban faɗa maka cewa bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni, in ba masifa ba?”
18 Againe hee saide, Therefore heare ye the worde of the Lord: I sawe the Lord sit vpon his throne, and all the hoste of heauen standing at his right hand, and at his left.
Mikahiya ya ci gaba, “Saboda haka sai ka ji maganar Ubangiji. Na ga Ubangiji yana zama a kan kursiyinsa tare da dukan rundunar sama tsaye a damansa da hagunsa.
19 And the Lord sayd, Who shall perswade Ahab King of Israel, that he may go vp, and fall at Ramoth Gilead? And one spake and said thus, and another said that.
Ubangiji kuwa ya ce, ‘Wa zai ruɗe Ahab sarki Isra’ila zuwa yaƙi da Ramot Gileyad da kuma zuwa mutuwarsa a can?’ “Wani ya ba da wata shawara, wani kuma wata dabam.
20 Then there came forth a spirit and stoode before the Lord, and said, I will perswade him. And the Lord said vnto him, Wherein?
A ƙarshe, wani ruhu ya zo gaba, ya tsaya a gaban Ubangiji ya ce, ‘Zan ruɗe shi.’ “Ubangiji ya yi tambaya, ‘Ta wace hanya?’
21 And he saide, I will goe out, and bee a false spirit in the mouth of all his Prophets. And hee said, Thou shalt perswade, and shalt also preuaile: goe forth and do so.
“Ya ce, ‘Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakunan dukan annabawansa.’ “Ubangiji ya ce, ‘Za ka yi nasara a ruɗinsa. Ka tafi, ka yi haka.’
22 Now therefore behold, the Lord hath put a false spirit in the mouth of these thy Prophets, and the Lord hath determined euill against thee.
“To yanzu, Ubangiji ya sa ruhun ruɗu a bakunan waɗannan annabawanka. Ubangiji ya ƙayyade masifa dominka.”
23 Then Zidkiah the sonne of Chenaanah came neere, and smote Michaiah vpon the cheeke, and sayde, By what way went the Spirit of the Lord from me, to speake with thee?
Sai Zedekiya ɗan Kena’ana ya haura ya mari Mikahiya a fuska. Ya ce, “Ta wace hanya ce ruhun Ubangiji ya fita daga gare ni ya zo ya yi magana da kai?”
24 And Michaiah saide, Behold, thou shalt see that day when thou shalt goe from chamber to chamber to hide thee.
Mikahiya ya amsa ya ce, “Za ka gane a ranar da ka je ka ɓuya a can cikin ɗaki.”
25 And the King of Israel sayde, Take ye Michaiah, and cary him to Amon the gouernour of the citie, and to Ioash the Kings sonne,
Sa’an nan sarkin Isra’ila ya umarta, “Ɗauki Mikahiya ku aika da shi zuwa ga Amon mai mulkin birni da kuma ga Yowash ɗan sarki,
26 And say, Thus saith the King, Put this man in the prison house, and feede him with bread of affliction and with water of affliction vntil I returne in peace.
ku ce ga abin da sarki ya ce, ‘Ku jefa wannan mutum a kurkuku kada kuma ku ba shi wani abu sai dai burodi da ruwa har sai na dawo lafiya.’”
27 And Michaiah said, If thou returne in peace, the Lord hath not spoken by me. And he saide, Heare, all ye people.
Mikahiya ya furta ya ce, “Idan har ka dawo lafiya, to, Ubangiji bai yi magana ta wurina ba.” Ya kuma ƙara da cewa, “Dukanku mutane, ku lura da maganata!”
28 So the King of Israel and Iehoshaphat the King of Iudah went vp to Ramoth Gilead.
Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suka haura zuwa Ramot Gileyad.
29 And the King of Israel said vnto Iehoshaphat, I will change my selfe, and enter into the battel: but put thou on thine apparel. So the King of Israel changed himselfe, and they went into the battel.
Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Zan ɓad da kama in shiga yaƙin, amma ka sa kayanka na sarauta.” Saboda haka sarkin Isra’ila ya ɓad da kama ya shiga cikin yaƙin.
30 And the King of Aram had commanded the captaines of the charets that were with him, saying, Fight you not with small, nor great, but against the King of Israel onely.
To, fa, sarkin Aram ya umarce shugabannin keken yaƙinsa ya ce, “Kada ku yaƙi kowa, ƙarami ko babba, sai dai sarkin Isra’ila.”
31 And when the captaines of the charets saw Iehoshaphat, they sayde, It is the King of Israel: and they compassed about him to fight. But Iehoshaphat cryed, and the Lord helped him and moued them to depart from him.
Sa’ad da shugabannin kekunan yaƙi suka ga Yehoshafat, sai suka yi tsammani, “Wannan ne sarkin Isra’ila.” Saboda haka suka juya don su yaƙe shi, amma Yehoshafat ya yi ihu, Ubangiji kuma ya taimake shi. Allah ya janye su daga gare shi,
32 For when the captaines of the charets saw that hee was not the King of Israel, they turned backe from him.
gama sa’ad da shugabannin keken yaƙi suka ga cewa ba shi ne sarkin Isra’ila ba, sai suka daina binsa.
33 Then a certaine man drewe a bowe mightily, and smote the King of Israel betweene the ioyntes of his brigandine: Therefore he saide to his charetman, Turne thine hand, and carie mee out of the host: for I am hurt.
Amma wani ya harba kibiya haka kawai, sai kibiyar ta sami sarki Ahab na Isra’ila a kafaɗa tsakanin rigar yaƙinsa na ƙarfe da ƙarfen ƙirjinsa. Sai sarki ya ce wa mai tuƙan keken yaƙi, “Juya ka fitar da ni daga wurin yaƙin. An ji mini rauni.”
34 And the battel increased that day: and the King of Israel stood still in his charet against the Aramites vntil euen, and dyed at the time of the sunne going downe.
Duk yini yaƙi ya yi ta cin gaba, sarkin Isra’ila kuwa ya jingina kansa a cikin keken yaƙinsa yana duban Arameyawa har yamma. Sa’an nan a fāɗuwar rana sai ya mutu.

< 2 Chronicles 18 >