< 1 Samuel 24 >

1 When Saul was turned from ye Philistims, they told him, saying, Behold, Dauid is in the wildernes of En-gedi.
Bayan da Shawulu ya komo daga fafaran Filistiyawa, sai aka gaya masa cewa, “Dawuda yana can a Jejin En Gedi.”
2 Then Saul tooke three thousande chosen men out of all Israel, and went to seeke Dauid and his men vpon the rocks among the wilde goates.
Saboda haka Shawulu ya zaɓi mutum dubu uku daga cikin dukan Isra’ila, suka fita neman Dawuda da mutanensa kusa da Duwatsun Awakin Jeji.
3 And hee came to the sheepecoates by the way where there was a caue, and Saul went in to do his easement: and Dauid and his men sate in the inward parts of the caue.
Da Shawulu ya isa inda ake ajiye garken tumaki a bakin hanya inda akwai kogo, sai ya shiga ciki kogon don yă yi bayan gari. Dawuda da mutanensa kuwa suna can zaune a ƙurewar kogon.
4 And the men of Dauid said vnto him, See, the day is come, whereof the Lord sayde vnto thee, Beholde, I will deliuer thine enemie into thine hande, and thou shalt doe to him as it shall seeme good to thee. Then Dauid arose and cut off the lap of Sauls garment priuily.
Mutanen Dawuda suka ce, wannan rana ce Ubangiji ya yi magana ya ce maka, “Zan ba da maƙiyinka a hannunka domin ka yi abin da ka ga dama da shi.” Sai Dawuda ya tashi a hankali ya je ya yanke shafin rigar Shawulu.
5 And afterward Dauid was touched in his heart, because he had cut off the lappe which was on Sauls garment.
Daga baya Dawuda ya damu domin ya yanke shafin rigar Shawulu.
6 And he said vnto his men, The Lord keepe mee from doing that thing vnto my master the Lords Anoynted, to lay mine hand vpon him: for he is the Anoynted of the Lord.
Ya ce wa mutanensa, “Ubangiji yă sawwaƙe in yi abu haka ga shugabana da Ubangiji ya shafe, ko in ɗaga hannuna in kashe shi, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.”
7 So Dauid ouercame his seruants with these words, and suffered them not to arise against Saul: so Saul rose vp out of the caue and went away.
Da wannan magana Dawuda ya kwaɓi mutanensa, bai yarda su fāɗa wa Shawulu ba. Shawulu kuwa ya bar kogon ya yi tafiyarsa.
8 Dauid also arose afterward, and went out of the caue, and cryed after Saul, saying, O my lorde the King. And when Saul looked behinde him, Dauid inclined his face to the earth, and bowed himselfe.
Daga baya Dawuda ya fita daga kogon sai ya kira Shawulu ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki!” Da Shawulu ya waiwaya, sai Dawuda ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
9 And Dauid saide to Saul, Wherefore giuest thou an eare to mens words, that say, Behold, Dauid seeketh euill against thee?
Ya ce wa Shawulu, “Me ya sa kake saurari mutanen da suke cewa, ‘Dawuda ya dāge yă cuce ka’?
10 Behold, this day thine eyes haue seene, that the Lord had deliuered thee this day into mine hand in the caue, and some bade me kill thee, but I had compassion on thee, and said, I will not lay mine hande on my master: for he is the Lordes Anoynted.
Yau ka ga da idonka yadda Ubangiji ya bashe ka a hannuna a cikin kogon nan. Waɗansu sun ce mini in kashe ka, amma na bar ka, na ce, ‘Ba zan sa hannuna a kan shugabana ba, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.’
11 Moreouer my father, behold: behold, I say, the lappe of thy garment in mine hand: for when I cut off the lappe of thy garment, I killed thee not. Vnderstad and see, that there is neither euil nor wickednesse in mee, neither haue I sinned against thee, yet thou huntest after my soule to take it.
Babana, duba, ga shafin rigarka a hannuna, na yanke shafin rigarka amma ban kashe ka ba. Yanzu ka gane ka kuma sani cewa ba ni da laifin aikata kome ko tayarwa, ban yi maka laifi ba, amma kana farautar raina.
12 The Lord be iudge betweene thee and me, and the Lord auenge me of thee, and let not mine hand be vpon thee.
Ubangiji zai shari’anta tsakanina da kai. Ubangiji zai sāka mini laifin da ka yi mini, amma ni kam ba zan taɓa ka ba.
13 According as the olde prouerbe sayeth, Wickednesse proceedeth from the wicked, but mine hand be not vpon thee.
Kamar yadda karin maganan nan na dā ya ce, ‘Daga cikin masu mugunta, mugunta ke fitowa,’ hannuna dai ba zai taɓa ka ba.
14 After whom is the King of Israel come out? after whome doest thou pursue? after a dead dog, and after a flea?
“Wane ne sarkin Isra’ila, ka fito kake bi? Wa kake kora? Kana bin mataccen kare ko kuɗin cizo?
15 The Lord therfore be iudge, and iudge betweene thee and me, and see, and pleade my cause, and deliuer me out of thine hand.
Ubangiji yă zama alƙali, yă yi shari’a tsakanina da kai, bari Ubangiji yă duba, yă tsaya mini, yă nuna ba ni da laifi.”
16 Whe Dauid had made an end of speaking these words to Saul, Saul sayd, Is this thy voyce, my sonne Dauid? and Saul lift vp his voice, and wept,
Da Dawuda ya gama wannan magana, sai Shawulu ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Sai ya fasa da kuka.
17 And sayd to Dauid, Thou art more righteous then I: for thou hast rendred me good, and I haue rendred thee euill.
Ya ce, “Ka fi ni gaskiya, ka yi mini alheri, ni kuwa na yi maka mugunta.
18 And thou hast shewed this day, that thou hast dealt well with me: forasmuch as when the Lord had closed me in thine hands, thou killedst me not.
Ga shi yanzu ka faɗa mini alherin da ka yi mini. Ubangiji ya bashe ni a hannunka amma ba ka kashe ni ba.
19 For who shall finde his enemie, and let him depart free? wherefore the Lord render thee good for that thou hast done vnto me this day.
In mutum ya sami maƙiyinsa, zai bar shi yă tafi lafiya ba tare da yin masa rauni ba? Ubangiji yă sāka maka, gama ka nuna mini alheri a yau.
20 For now behold, I know that thou shalt be King, and that the kingdome of Israel shall be stablished in thine hand.
Na sani tabbatacce za ka zama sarki. Masarautar Isra’ila za tă kahu a hannunka.
21 Sweare now therfore vnto me by the Lord, that thou wilt not destroy my seede after me, and that thou wilt not abolish my name out of my fathers house.
Yanzu ka rantse mini da Ubangiji cewa ba za ka hallaka zuriyarta ko ka share sunana daga iyalin mahaifina ba.”
22 So Dauid sware vnto Saul, and Saul went home: but Dauid and his men went vp vnto ye hold.
Sai Dawuda ya rantse wa Shawulu. Sa’an nan Shawulu ya koma gida, amma Dawuda da mutanensa suka haura zuwa wurin ɓuya.

< 1 Samuel 24 >