< 1 Chronicles 5 >

1 The sonnes also of Reuben the eldest sonne of Israel (for he was the eldest, but had defiled his fathers bed, therefore his birthright was giuen vnto the sonnes of Ioseph the sonne of Israel, so that the genealogie is not rekoned after his birthright.
’Ya’yan Ruben maza ɗan farin Isra’ila (shi ne ɗan fari, amma sa’ad da ya ƙazantar da gadon auren mahaifinsa, sai aka ba wa’yancin ɗan farinsa wa’ya’yan Yusuf maza ɗan Isra’ila; don kada a lissafta shi a tarihin zuriya bisa ga matsayin haihuwarsa,
2 For Iudah preuailed aboue his brethren, and of him came the prince, but the birthright was Iosephs)
ko da yake Yahuda shi ne mafi ƙarfi cikin’yan’uwansa kuma mai mulki ya fito daga gare shi,’yancin zaman ɗan fari na Yusuf ne),
3 The sonnes of Reuben the eldest sonne of Israel, were Hanoch and Pallu, Hezron and Carmi.
’ya’yan Ruben ɗan farin Isra’ila maza su ne, Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.
4 The sonnes of Ioel, Shemaiah his sonne, Gog his sonne, and Shimei his sonne,
Zuriyar Yowel su ne, Shemahiya, Gog, Shimeyi,
5 Michah his sonne, Reaiah his sonne, and Baal his sonne,
Mika, Reyahiya, Ba’al,
6 Beerah his sonne: whom Tilgath Pilneeser King of Asshur caryed away: he was a prince of the Reubenites.
da Beyera, wanda Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya ɗauka zuwa zaman bauta. Beyera shi ne shugaban mutanen Ruben.
7 And when his brethren in their families rekoned the genealogie of their generations, Ieiel and Zechariah were the chiefe,
Danginsu bisa ga iyalansu da aka jera bisa ga tarihin zuriyarsu su ne, Yehiyel shi ne sarki, akwai Zakariya,
8 And Bela the sonne of Azaz, the sonne of Shema, the sonne of Ioel, which dwelt in Aroer, euen vnto Nebo and Baal meon.
da Bela ɗan Azaz. Azaz ɗan Shema daga dangin Yowel. Yowel ya yi zama a yankin Arower har zuwa Nebo da Ba’al-Meyon.
9 Also Eastwarde he inhabited vnto the entring in of the wildernes from the riuer Perath for they had much cattel in the land of Gilead.
Ta waje gabas sun zauna a ƙasar har zuwa bakin hamadan da ya nausa zuwa Kogin Yuferites, domin dabbobinsu sun ƙaru a Gileyad.
10 And in the dayes of Saul they warred with the Hagarims, which fell by their hands: and they dwelt in their tentes in all the East partes of Gilead.
A zamanin Shawulu zuriyar Ruben sun yi yaƙi da Hagirawa, suka ci su da yaƙi, suka zauna a wuraren zaman Hagirawan ko’ina a dukan yankin gabashin Gileyad.
11 And the children of Gad dwelt ouer against them in the land of Bashan, vnto Salchah.
Mutanen Gad sun zauna kusa da mutanen Ruben a Bashan, har zuwa Saleka.
12 Ioel was the chiefest, and Shapham the second, but Iaanai and Shaphat were in Bashan.
Yowel shi ne babba, sai Shafan na biyu, sa’an nan Yanai da Shafat, su ne tushen Bashan.
13 And their brethren of the house of their fathers were Michael, and Meshullam, and Sheba, and Sorai, and Iacan, and Zia and Eber, seuen.
Danginsu, bisa ga iyalai su ne, Mika’ilu, Meshullam, Sheba, Yorai, Yakan, Ziya da Eber, su bakwai ne duka.
14 These are the childre of Abihail, the sonne of Huri, the sonne of Iaroah, the sonne of Gilead, the sonne of Michael, the sonne of Ieshishai, the sonne of Iahdo, the sonne of Buz.
Waɗannan su ne’ya’yan Abihayil ɗan Huri, ɗan Yarowa, ɗan Gileyad, ɗan Mika’ilu, ɗan Yeshishai, ɗan Yado, ɗan Buz.
15 Ahi the sonne of Abdiel, the sonne of Guni was chiefe of the houshold of their fathers.
Ahi ɗan Abiyel, ɗan Guni, shi ne kan iyalinsu.
16 And they dwelt in Gilead in Bashan, and in the townes thereof, and in all the suburbes of Sharon by their borders.
Mutanen Gad sun zauna a Bashan da ƙauyukan da suke kurkusa da shi, da kuma a dukan makiyayan Sharon har zuwa iyaka inda suka kai.
17 All these were rekoned by genealogies in the dayes of Iotham King of Iudah, and in the dayes of Ieroboam King of Israel.
Dukan waɗannan sun shiga tarihin zuriya a lokacin mulkin Yotam sarkin Yahuda da Yerobowam sarkin Isra’ila.
18 The sonnes of Reuben and of Gad, and of halfe the tribe of Manasseh of those that were viliant men, able to beare shield, and sworde, and to draw a bowe, exercised in warre, were foure and fourtie thousand, seuen hundreth and three score, that went out to the warre.
Mutanen Ruben, mutanen Gad da rabin kabilar Manasse sun kasance da mutane 44,760 shiryayyu don aikin soja, jarumawan da za su iya riƙe garkuwa da takobi, waɗanda suke iya yin amfani da baka, waɗanda kuma aka horar don yaƙi.
19 And they made warre with the Hagarims, with Ietur, and Naphish, and Nodab.
Suka yi yaƙi da Hagirawa, Yetur, Nafish da Nodab.
20 And they were holpen against them, and the Hagarims were deliuered into their hande, and all that were with them: for they cryed to God in the battel, and he heard them, because they trusted in him.
Aka taimake su a yaƙin, Allah kuma ya ba da Hagirawa da dukan abokansu gare su, domin sun yi kuka gare shi a lokacin yaƙin. Ya amsa addu’o’insu, domin sun dogara gare shi.
21 And they led away their cattel, euen their camels fiftie thousand, and two hundreth, and fiftie thousand sheepe, and two thousand asses, and of persons an hundreth thousand.
Suka ƙwace dabbobin Hagirawa, raƙuma dubu hamsin, tumaki dubu ɗari biyu da hamsin da kuma jakuna dubu biyu. Suka kuma kame mutane dubu ɗari ɗaya,
22 For many fel downe wounded, because the warre was of God. And they dwelt in their steads vntill the captiuitie.
waɗansu suka mutu, domin yaƙin na Allah ne. Suka zauna a ƙasar har lokacin da aka kai su zaman bauta.
23 And the children of the halfe tribe of Manasseh dwelt in the land, from Baashan vnto Baal Hermon, and Senir, and vnto mount Hermon: for they increased.
Mutanen rabin kabilar Manasse sun yi yawa; suka zauna a ƙasar daga Bashan har zuwa Ba’al-Hermon, wato, zuwa Senir (Dutsen Hermon).
24 And these were the heads of the housholds of their fathers, euen Epher and Ishi, and Eliel and Azriel, and Ieremiah, and Hodauiah, and Iahdiel, strong men, valiant and famous, heades of the housholdes of their fathers.
Waɗannan su ne kawunan iyalansu. Efer, Ishi, Eliyel, Azriyel, Irmiya, Hodawiya da Yadiyel. Su jarumawa ne, sanannu, su ne kuma kawunan iyalansu.
25 But they transgressed against the God of their fathers, and went a whoring after the gods of the people of the lande, whome God had destroyed before them.
Amma ba su yi aminci da Allahn kakanninsu ba, suka kuma yi karuwanci ga waɗansu allolin mutanen ƙasar, waɗanda Allah ya hallaka a gabansu.
26 And the God of Israel stirred vp the spirit of Pul king of Asshur, and the spirite of Tilgath Pilneeser king of Asshur, and he caryed them away: euen the Reubenites and the Gadites, and the halfe tribe of Manasseh, and brought them vnto Halah and Habor, and Hara, and to the riuer Gozan, vnto this day.
Saboda haka Allah na Isra’ila ya zuga ruhun Ful sarkin Assuriya (wato, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya), wanda ya kwashe mutanen Ruben, mutanen Gad da rabin kabilar Manasse zuwa zaman bauta. Ya kwashe su zuwa Hala, Habor, Hara da kuma kogin Gozan, inda suke har wa yau.

< 1 Chronicles 5 >