< 1 Chronicles 16 >

1 So they brought in the Arke of God, and set it in the middes of the Tabernacle that Dauid had pitched for it, and they offred burnt offrings and peace offrings before God.
Suka fa kawo akwatin alkawarin Allah, suka sa a cikin tentin da Dawuda ya kafa dominsa, suka kuma miƙa hadayun ƙonawa da hadayu na salama a gaban Allah.
2 And when Dauid had made an ende of offering the burnt offering and the peace offerings, hee blessed the people in the Name of the Lord.
Bayan Dawuda ya gama miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji.
3 And he dealt to euery one of Israel both man and woman, to euery one a cake of breade, and a piece of flesh, and a bottel of wine.
Sa’an nan ya ba da dunƙulen burodi da wainar dabino da kuma kauɗar zabibi ga kowane mutumin Isra’ila namiji da ta mace.
4 And he appointed certaine of the Leuites to minister before the Arke of the Lord, and to rehearse and to thanke and prayse the Lord God of Israel:
Ya sa Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka, su gode, su kuma yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
5 Asaph the chiefe, and next to him Zechariah, Ieiel, and Shemiramoth, and Iehiel, and Mattithiah, and Eliab, and Benaiah, and Obed Edom, euen Ieiel with instruments, violes and harpes, and Asaph to make a sound with cymbales,
Asaf shi ne babba, sai Zakariya na biye, sa’an nan Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Mattitiya, Eliyab, Benahiya, Obed-Edom da Yehiyel. Su ne za su kaɗa molaye, da garayu, Asaf kuwa zai buga ganguna,
6 And Benaiah and Iahaziel Priestes, with trumpets continually before the Arke of the couenant of God.
Benahiya da Yahaziyel firistoci za su busa ƙahoni kullum a gaban akwatin alkawarin Allah.
7 Then at that time Dauid did appoint at the beginning to giue thankes to the Lord by the hand of Asaph and his brethren.
A wannan rana, da farko, Dawuda ya sa Asaf da’yan’uwansa su rera wannan zabura ta yabo ga Ubangiji.
8 Praise the Lord and call vpon his Name: declare his workes among the people.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
9 Sing vnto him, sing praise vnto him, and talke of all his wonderfull workes.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan ayyukan banmamakinsa.
10 Reioyce in his holy Name: let the hearts of them that seeke the Lord reioyce.
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
11 Seeke the Lord and his strength: seeke his face continually.
Ku dogara ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
12 Remember his marueilous workes that he hath done, his wonders, and the iudgements of his mouth,
Ku tuna ayyukan banmamakin da ya aikata, mu’ujizansa da kuma hukuntai da ya yanke,
13 O seede of Israel his seruant, O the children of Iaakob his chosen.
Ya ku zuriyar Isra’ila bayinsa, Ya ku’ya’yan Yaƙub maza, zaɓaɓɓunsa.
14 He is the Lord our God: his iudgements are throughout all the earth.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; hukuntansa suna a cikin dukan duniya.
15 Remember his couenant for euer, and the worde, which hee commanded to a thousand generations:
Yakan tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
16 Which he made with Abraham, and his othe to Izhak:
alkawarin da ya yi wa Ibrahim rantsuwar da ya yi ga Ishaku.
17 And hath confirmed it to Iaakob for a Law, and to Israel for an euerlasting couenant,
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub kamar ƙa’ida, ga Isra’ila kamar madawwamin alkawari.
18 Saying, To thee will I giue the land of Canaan, the lot of your inheritance.
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana kamar rabon da za ka gāda.”
19 When ye were fewe in number, yea, a very fewe, and strangers therein,
Sa’ad da suke kima, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
20 And walked about from nation to nation, and from one kingdome to another people,
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga wannan mulki zuwa wancan.
21 He suffered no man to do them wrong, but rebuked Kings for their sakes, saying,
Bai bar wani ya zalunce su ba; saboda su ya tsawata wa sarakuna.
22 Touch not mine anoynted, and doe my Prophets no harme.
“Kada ku taɓa shafaffuna; kada ku yi wa annabawana lahani.”
23 Sing vnto the Lord all the earth: declare his saluation from day to day.
Ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
24 Declare his glory among the nations, and his wonderful workes among all people.
Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, ayyukansa masu al’ajabai a cikin mutane.
25 For the Lord is great and much to be praised, and hee is to bee feared aboue all gods.
Gama Ubangiji mai girma ne ya kuma cancanci yabo; dole a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
26 For all the gods of the people are idoles, but the Lord made the heauens.
Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ya yi sammai.
27 Prayse and glory are before him: power and beautie are in his place.
Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da farin ciki suna a wurin zamansa.
28 Giue vnto the Lord, ye families of the people: giue vnto the Lord glory and power.
Ku yabi Ubangiji, ku iyalan al’ummai, ku yabi ɗaukaka da ƙarfin Ubangiji,
29 Giue vnto the Lord ye glory of his Name: bring an offring and come before him, and worship the Lord in the glorious Sanctuarie.
ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo hadaya ku kuma zo gabansa; ku yi wa Ubangiji sujada cikin darajar tsarkinsa.
30 Tremble ye before him, al the earth: surely the world shalbe stable and not moue.
Ku yi rawar jiki a gabansa, ya ku duniya duka! Duniya ta kahu sosai; ba za tă jijjigu ba.
31 Let the heauens reioyce, and let the earth be glad, and let them say among the nations, The Lord reigneth.
Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari su ce a cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki!”
32 Let the sea roare, and all that therein is: Let the field be ioyfull and all that is in it.
Bari teku da kome da yake cikinsa su yi ruri; bari gonaki da kome a cikinsu su yi farin ciki!
33 Let the trees of the wood then reioyce at the presence of the Lord: for he commeth to iudge the earth.
Sa’an nan itatuwan jeji za su rera, za su rera don farin ciki a gaban Ubangiji, gama ya zo don yă hukunta duniya.
34 Prayse the Lord, for hee is good, for his mercie endureth for euer.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne; ƙaunarsa madawwamiya ce.
35 And say ye, Saue vs, O God, our saluation, and gather vs, and deliuer vs from the heathen, that we may prayse thine holy Name, and glorie in thy praise.
Ku yi kuka, ku ce, “Cece mu, ya Allah Mai Cetonmu; tara mu ka kuma cece mu daga al’ummai, don mu yi godiya ga sunanka mai tsarki, don mu ɗaukaka a cikin yabonka.”
36 Blessed be the Lord God of Israel for euer and euer: and let all people say, So be it, and praise the Lord.
Yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Sai dukan mutane suka ce, “Amin.” Suka kuma “Yabi Ubangiji.”
37 Then he left there before the Arke of the Lordes couenant Asaph and his brethren to minister continually before the Arke, that which was to be done euery day:
Dawuda ya bar Asaf da’yan’uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji don su yi hidima a can kullum, bisa ga tsari na kowace rana.
38 And Obed Edom and his brethren, three score and eight: and Obed Edom the sonne of Ieduthun, and Hosah were porters.
Ya kuma bar Obed-Edom da’yan’uwansa sittin da takwas don su yi hidima tare. Obed-Edom ɗan Yedutun da Hosa kuma, su ne matsaran ƙofofi.
39 And Zadok the Priest and his brethren the Priestes were before the Tabernacle of ye Lord, in the hie place that was at Gibeon,
Dawuda ya bar Zadok firist da’yan’uwansa firistoci a gaban tabanakul na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon
40 To offer burnt offrings vnto the Lord, vpon the burnt offring altar continually, in the morning and in the euening, euen according vnto all that is written in the law of the Lord, which hee commanded Israel.
don su miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a kan bagaden hadaya ta ƙonawa kullum, da safe da kuma yamma, bisa ga kome da yake a rubutacce a cikin Dokar Ubangiji, da ya ba wa Isra’ila.
41 And with them were Heman, and Ieduthun, and the rest that were chosen (which were appointed by names) to praise the Lord, because his mercie endureth for euer.
Tare da su akwai Heman da Yedutun da sauran waɗannan zaɓaɓɓun da aka rubuta sunansu don yin godiya ga Ubangiji, “gama ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
42 Euen with them were Heman and Ioduthun, to make a sound with the cornets and with the cymbales, with excellent instruments of musicke: and the sonnes of Ieduthun were at the gate.
Heman da Yedutun su ne da hakkin busa ƙahoni da kaɗa kuge da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin da ake rera waƙoƙi masu tsarki.’Ya’yan Yedutun maza, su aka ba wa aikin tsaron ƙofa.
43 And all the people departed, euerie man to his house: and Dauid returned to blesse his house.
Sa’an nan dukan mutanen suka tashi, kowa ya koma gidansa, Dawuda ya koma gida yă sa wa iyalinsa albarka.

< 1 Chronicles 16 >