< Nehemiah 12 >

1 This is a list of the priests and Levites who came back with Zerubbabel, son of Shealtiel, and Jeshua, the high priest: Seraiah, Jeremiah, Ezra,
Waɗannan su ne firistoci da Lawiyawa waɗanda suka komo tare da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da kuma Yeshuwa. Serahiya, Irmiya, Ezra,
2 Amariah, Malluch, Hattush,
Amariya, Malluk, Hattush
3 Shecaniah, Rehum, Meremoth,
Shekaniya, Rehum, Meremot,
4 Iddo, Ginnethon, Abijah,
Iddo, Ginneton, Abiya,
5 Miniamin, Maadiah, Bilgah,
Miyamin, Mowadiya, Bilga,
6 Shemaiah, Joiarib, Jedaiah,
Shemahiya, Yohiyarib, Yedahiya,
7 Sallu, Amok, Hilkiah, and Jedaiah. These were the leaders of the priests and their relatives in Jeshua's time.
Sallu, Amok, Hilkiya da Yedahiya. Waɗannan su ne shugabannin firistoci da’yan’uwansu a kwanakin Yeshuwa.
8 The Levites were Jeshua, Binnui, Kadmiel, Sherebiah, Judah, and Mattaniah, who with his fellow Levites was in charge of the songs of praise.
Lawiyawan su ne Yeshuwa, Binnuyi, Kadmiyel, Sherebiya, Yahuda, da kuma Mattaniya, wanda tare da’yan’uwansa yake lura da waƙoƙin godiya.
9 Two other Levites, Bakbukiah and Unni, stood opposite them in the service.
Bakbukiya da Unni,’yan’uwansu sun tsaya ɗaura da su a hidimomi.
10 Jeshua the high priest was the father of Joiakim, who was the father of Eliashib, who was the father of Joiada,
Yeshuwa ne mahaifin Yohiyakim, Yohiyakim shi ne mahaifin Eliyashib, Eliyashib shi ne mahaifin Yohiyada,
11 who was the father of Jonathan, who was the father of Jaddua.
Yohiyada shi ne mahaifin Yonatan, Yonatan kuma mahaifin Yadduwa.
12 In Joiakim's time, these were the family leaders of the priests: of the family of Seraiah, Meraiah; of Jeremiah, Hananiah;
A kwanakin Yohiyakim, waɗannan su ne shugabannin iyalan firistoci, na iyalin Serahiya, Merahiya; na iyalin Irmiya, Hananiya;
13 of Ezra, Meshullam; of Amariah, Jehohanan;
na iyalin Ezra, Meshullam; na iyalin Amariya, Yehohanan;
14 of Malluchi, Jonathan; of Shebaniah, Joseph;
na iyalin Malluk, Yonatan; na iyalin Shebaniya, Yusuf;
15 of Harim, Adna; of Meraioth, Helkai;
na iyalin Harim, Adna; na iyalin Merahiyot, Helkai;
16 of Iddo, Zechariah; of Ginnethon, Meshullam;
na iyalin Iddo, Zakariya; na iyalin Ginneton, Meshullam;
17 of Abijah, Zichri; of Miniamin and of Moadiah, Piltai;
na iyalin Abiya, Zikri; na iyalin Miniyamin da na Mowadiya, Filtai;
18 of Bilgah, Shammua; of Shemaiah, Jehonathan;
na iyalin Bilga, Shammuwa; na iyalin Shemahiya, Yehonatan;
19 of Joiarib, Mattenai; of Jedaiah, Uzzi;
na iyalin Yohiyarib, Mattenai; na iyalin Yedahiya, Uzzi;
20 of Sallai, Kallai; of Amok, Eber;
na iyalin Sallu, Kallai; na iyalin Amok, Eber;
21 of Hilkiah, Hashabiah; of Jedaiah, Nethanel.
na iyalin Hilkiya, Hashabiya; na iyalin Yedahiya, Netanel.
22 The family leaders of the Levites in the time of Eliashib, Joiada, Johanan, and Jaddua, in addition to those of the priests, were recorded during the reign of Darius the Persian.
Shugabannin iyalin Lawiyawa a kwanakin Eliyashib, Yohiyada, Yohanan da Yadduwa, da kuma na firistoci, an rubuta su a zamanin mulkin Dariyus mutumin Farisa.
23 As for the genealogy of the sons of Levi, the family leaders up to the time of Johanan, son of Eliashib, were listed in the Book of the Records.
Shugabannin iyali cikin zuriyar Lawi har zuwa lokacin Yohanan ɗan Eliyashib, an rubuta su a cikin littafin tarihi.
24 The Levite leaders were Hashabiah, Sherebiah, and Jeshua, son of Kadmiel, together with their fellow Levites, who stood opposite them, each section giving praise and thanks and responding to one another, as arranged by David, the man of God.
Shugabannin Lawiyawa kuwa su ne Hashabiya, Sherebiya, Yeshuwa ɗan Kadmiyel, da’yan’uwansu, waɗanda suka tsaya ɗaura da su don su yi yabo da kuma godiya, sashe ɗaya kan ba da amsa ga ɗaya sashen, kamar yadda Dawuda mutumin Allah ya umarta.
25 They were joined by Mattaniah, Bakbukiah, and Obadiah. Meshullam, Talmon, and Akkub were gatekeepers who guarded the storehouses at the gates.
Mattaniya, Bakbukiya, Obadiya, Meshullam, Talmon da Akkub su ne matsaran ƙofofi waɗanda suka yi tsaron ɗaukan ajiya a ƙofofi.
26 They served in the time of Joiakim, son of Jeshua, son of Jozadak, and in the time of Nehemiah the governor and Ezra the priest and scribe.
Sun yi hidima a kwanakin Yohiyakim ɗan Yeshuwa, ɗan Yozadak, kuma a kwanakin Nehemiya gwamna da kuma na Ezra firist da kuma marubuci.
27 In order to dedicate the wall of Jerusalem, the Levites were called from everywhere they were living to come to Jerusalem and celebrate with joy the dedication with songs of praise and thanks, accompanied by cymbals, harps, and lyres.
A keɓewar katangar Urushalima, an nemi Lawiyawa daga inda suke zama aka kawo su Urushalima don su yi bikin miƙawa da farin ciki da waƙoƙin godiya da kuma kiɗin kuge, garaya da molo.
28 The singers were also brought in from the area around Jerusalem and from the villages of the Netophathites,
Aka kuma tattara mawaƙa su ma daga yankin kewayen Urushalima, daga ƙauyukan Netofawa,
29 as well as from Beth-gilgal and from the area of Geba and Azmaveth, for the singers had built villages for themselves all around Jerusalem.
daga Bet-Gilgal, da kuma daga wuraren Geba da Azmawet, gama mawaƙan sun gina wa kansu ƙauyuka kewaye da Urushalima.
30 Once the priests and the Levites had purified themselves, they purified the people, the gates, and the wall.
Sa’ad da firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu da tsarki, sai suka tsarkake mutane, ƙofofi da kuma katanga.
31 I had the leaders of Judah go up on the wall, and arranged two large choirs that to give thanks. One group went to right along the wall to the Refuse Gate.
Sai na sa shugabannin Yahuda suka haura zuwa bisan katangar. Na kuma sa manyan ƙungiyoyi biyu na mawaƙa su miƙa godiya. Ɗaya ya haura zuwa bisan katangar zuwa dama, wajen Ƙofar Juji.
32 Hoshaiah and half the leaders of Judah followed them,
Hoshahiya da rabin shugabannin Yahuda kuwa suka bi su,
33 with Azariah, Ezra, Meshullam,
tare da Azariya, Ezra, Meshullam,
34 Judah, Benjamin, Shemaiah, and Jeremiah,
Yahuda, Benyamin, Shemahiya, Irmiya,
35 as well as some of the priests with trumpets, and Zechariah, son of Jonathan, son of Shemaiah, son of Mattaniah, son of Micaiah, son of Zaccur, son of Asaph,
da waɗansu firistoci kuma da ƙahoni, da kuma Zakariya ɗan Yonatan, ɗan Shemahiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mikahiya, ɗan Zakkur, ɗan Asaf,
36 and his fellow priests, Shemaiah, Azarel, Milalai, Gilalai, Maai, Nethanel, Judah, and Hanani, along with the musical instruments as required by David, the man of God. Ezra the scribe led them.
da’yan’uwansa, Shemahiya, Azarel, Milalai, Gilalai, Ma’ai, Netanel, Yahuda da Hanani, tare da kayan kiɗi da Dawuda mutumin Allah ya umarta. Ezra malamin Doka ya jagoranci jerin gwanon.
37 At the Fountain Gate they headed straight up by the stairs of the city of David, where the wall goes uphill, above the house of David, and on to the Water Gate on the east.
A Ƙofar Maɓuɓɓuga suka ci gaba kai tsaye suka haura matakalan Birnin Dawuda a kan hawa zuwa katangar suka wuce a bisa gidan Dawuda zuwa Ƙofar Ruwa wajen gabas.
38 The other choir group went in the opposite direction. I followed them, along with half the people, on the wall passing the Tower of the Ovens, on to the Broad Wall,
Ƙungiyar mawaƙa ta biyu suka yi jerin gwano a ɗaya gefen. Na bi su a bisan katangar, tare da rabin mutanen, muka wuce Hasumiya Tanderu zuwa Katanga Mai Faɗi,
39 over the Ephraim Gate, the Jeshanah Gate, the Fish Gate, the Tower of Hananel, and the Tower of the Hundred, as far as the Sheep Gate, stopping at the Guard Gate.
bisa Ƙofar Efraim, Ƙofar Yeshana, Ƙofar Kifi, Hasumiyar Hananel da kuma Hasumiya ɗari, har zuwa Ƙofar Tumaki. A Ƙofar Matsara suka tsaya.
40 Both thanksgiving choirs then took their places in God's Temple. I followed with the group of leaders that was with me,
Ƙungiyoyin mawaƙa biyu da suka yi godiya suka ɗauki wurarensu a gidan Allah, haka ma ni, tare da rabin shugabanni,
41 along with the priests blowing their trumpets: Eliakim, Maaseiah, Miniamin, Micaiah, Elioenai, Zechariah, and Hananiah.
da kuma firistoci, Eliyakim, Ma’asehiya, Miniyamin, Mikahiya, Eliyohenai, Zakariya da Hananiya tare da ƙahoninsu,
42 Then came the singers Maaseiah, Shemaiah, Eleazar, Uzzi, Jehohanan, Malchijah, Elam, and Ezer, and the choirs sang, directed by Jezrahiah.
haka ma Ma’asehiya, Shemahiya, Eleyazar, Uzzi, Yehohanan, Malkiya, Elam da Ezer. Mawaƙan suka rera waƙoƙi a ƙarƙashin kulawar Yezrahiya.
43 Many sacrifices were offered that day, celebrating that God had brought them so much happiness, tremendous happiness. The women and children also celebrated, and the sounds of joy in Jerusalem could be heard far away.
A rana ta uku kuma suka miƙa manyan hadayu, suna farin ciki domin Allah ya ba su farin ciki mai girma. Mata da yara suka yi farin ciki su ma. An ji ƙarar farin ciki da ake yi a Urushalima daga nesa.
44 On the same day men were put in charge over the storerooms that contained the offerings, the first part of the crops, and tithes. What was allocated by the Law for the priests and Levites was brought into these storerooms from the fields around the towns, because all the people of Judah were happy for the service of the priests and Levites.
A lokacin an naɗa mutane su lura da ɗakunan ajiya don sadakoki, nunan fari da kuma zakka. Daga gonakin garuruwan da suke kewaye za su kawo sassan da Dokar ta umarta zuwa ɗakunan ajiya domin firistoci da Lawiyawa, gama Yahuda ya ji daɗin aikin firistoci da Lawiyawa.
45 They were responsible for the worship of their God and for the service of purification, along with the singers and gatekeepers, following the instructions of David and his son Solomon.
Sun yi hidimar Allahnsu da kuma hidimar tsarkakewa, kamar yadda mawaƙa da matsaran ƙofofi suka yi, bisa ga umarnin Dawuda da ɗansa Solomon.
46 For long ago, back in the time of David and Asaph, directors had been appointed for the singers and for the songs of praise and thanks to God.
Gama tun dā, a kwanakin Dawuda da Asaf, akwai masu bi da mawaƙa da kuma na waƙoƙin yabo da na godiya ga Allah.
47 So in the time of Zerubbabel and of Nehemiah, everyone in Israel provided the daily food allowances for the singers and the gatekeepers. They also made sure to provide for the other Levites, and the Levites gave a share of this to the descendants of Aaron.
Saboda haka a kwanakin Zerubbabel da Nehemiya, dukan Isra’ila suka ba da sashe na kowace rana domin mawaƙa da matsaran ƙofofi. Suka kuma keɓe sashe don sauran Lawiyawa, Lawiyawan kuma suka keɓe sashe don zuriyar Haruna.

< Nehemiah 12 >