< Micah 2 >

1 How disastrous it will be for those who devise evil plans as they lie awake at night. They get up in the morning to carry them out, because they have the power to do just that.
Taku ta ƙare, ku da kuke shirya makirci, ku da kuke ƙulle-ƙullen mugunta a kan gadonku! Da gari ya waye sai ku fita ku aikata mugunta domin ikon aikatawa yana hannunku.
2 They seize any fields they want. They take any houses they want. They cheat people of their houses, and steal their inheritance.
Kukan yi ƙyashin gonaki ku kuma ƙwace su, ku yi ƙyashin gidaje ku kuma ƙwace. Kukan zalunci mutum, ku ƙwace masa gidansa, har ku ƙwace masa gādonsa.
3 So this is what the Lord says. Watch out! I am planning to bring disaster on such families. They won't be able to escape. You will no longer walk around arrogantly, for this will be a time of disaster.
Saboda haka, Ubangiji ya ce, “Ina shirya wa waɗannan mutane bala’i, yadda ba za ku iya ceton kanku ba. Ba za ku ƙara tafiya kuna taƙama ba, gama zai zama lokacin bala’i ne.
4 On that day they will make up a saying to taunt you. With a mocking lament they will say, “We are totally ruined! Our possessions are being sold off. They've taken everything away, and given our fields to your conquerors.”
A wannan rana mutane za su yi muku ba’a za su yi muku gwalo da wannan waƙar makoki, ‘An lalatar da mu sarai; an rarraba mallakar mutanena. Ya ɗauke shi daga gare ni! Ya miƙa filayenmu ga maciyan amanarmu.’”
5 Consequently at that time there will be none of you in the assembly of the Lord responsible for the division of the land.
Saboda haka ba za ku kasance da wani a taron jama’ar Ubangiji da zai raba ƙasar ta wurin jefa ƙuri’a ba.
6 But you preach at me, saying, “Don't preach such things. Don't prophesy like this. Such a humiliation won't happen to us!”
“Kada ku yi annabci” in ji annabawansu. “Kada ku yi annabci game da waɗannan abubuwa; abin kunya ba zai same mu ba.”
7 Should you talk like that, descendants of Jacob? You ask, “Can the Lord run out of patience? Is this what he does?” Are not my words good to those who do what is right? asks the Lord.
Daidai ne a ce, ya gidan Yaƙub, “Ruhun Ubangiji yana fushi ne? Yana yin irin waɗannan abubuwa?” “Ashe, maganata ba tă amfane wanda ayyukansa suke daidai ba?
8 Lately my people have risen up against me like an enemy. You steal the coats off the backs of those passing by, men returning from war who expect to be safe in their homeland.
Ba da daɗewa ba mutanena sun tashi kamar magabci. Kun tuɓe riga mai tsada daga waɗanda suke wucewa ba tare da kun damu ba, sai ka ce mutanen da suke komowa daga yaƙi.
9 You drive the women of my people from their comfortable homes; you have robbed their children of my blessings forever.
Kun kori matan mutanena daga gidajensu masu daɗi. Kuka kawar da albarkata har abada daga wurin’ya’yansu.
10 Get up! Leave! For this is not a place for you to stay. It is defiled and totally ruined.
Ku tafi, ku ba ni wuri! Gama wannan ba wurin hutunku ba ne, gama ya ƙazantu, ya zama kangon da ya wuce gyara.
11 If a false prophet should come to you and lie, saying, “I'll preach to you about the virtues of wine and alcohol,” he would be the perfect prophet for your kind of people.
In maƙaryaci da mazambaci ya zo ya ce, ‘Zan yi muku annabci ku sami wadataccen ruwan inabi da barasa,’ zai dai zama annabin da ya dace da wannan mutane ne!
12 I will certainly gather all of you, descendants of Jacob, I will certainly bring back together those who are left, Israel. I will place them like sheep in the fold, like a flock in its pasture. The land will be filled with people celebrating.
“Tabbatacce zan tattara ku duka, ya gidan Yaƙub; zan tattara ku raguwar Isra’ila. Zan kawo su wuri ɗaya kamar tumaki a cikin garke, kamar garke a wajen kiwonsa; wurin zai cika da mutane.
13 The One who opens the way for them will lead them, breaking through the gate and going out. Their King will lead them; the Lord himself will be at their head.
Wanda ya fasa ƙofa ya buɗe, shi zai haura yă yi musu jagora, za su fashe bangon su fita. Sarkinsu zai wuce gabansu, Ubangiji kuma zai kasance a gaba.”

< Micah 2 >