< Luke 24 >

1 Very early on the first day of the week, the women went to the tomb, taking the spices they'd prepared.
Da sassafe a ranar farko ta mako, matan suka je kabarin, da kayan ƙanshin da suka shirya.
2 They found that the stone had been rolled away from the entrance to the tomb,
Suka iske an riga an gungurar da dutsen daga bakin kabarin.
3 but when they went in they didn't find the body of the Lord Jesus.
Amma da suka shiga ciki, ba su iske jikin Ubangiji Yesu ba.
4 While they were wondering what was going on, two men suddenly appeared dressed in clothes that shone brilliantly.
Yayinda suna cikin tunani a kan wannan, nan take, ga waɗansu mutum biyu tsaye kusa da su, sanye da kaya masu ƙyalli, kamar walƙiya.
5 The women were terrified and bowed down, their faces on the ground. They said to the women, “Why are you looking for someone who is alive among the dead?
A cikin tsoro, matan suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa, amma mutanen suka ce musu, “Me ya sa kuke neman mai rai a cikin matattu?
6 He's not here; he's risen from the dead! Remember what he told you while you were still in Galilee:
Ba ya nan, ya tashi! Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana tare da ku a Galili cewa,
7 ‘The Son of man must be betrayed into the hands of evil men, be crucified, and on the third day rise again.’”
‘Dole a ba da Ɗan Mutum ga hannun masu zunubi, a kuma gicciye shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.’”
8 Then they remembered what he'd said.
Sai suka tuna da maganarsa.
9 When they returned from the tomb they reported all that had happened to the eleven disciples and to all the others.
Da suka dawo daga kabarin, sai suka faɗa wa Sha Ɗayan nan da sauransu, dukan waɗannan abubuwa.
10 Those who told the apostles what had happened were Mary Magdalene, Joanna, Mary the mother of James, and other women with them.
Matan da suka gaya wa manzannin waɗannan abubuwa su ne, Maryamu Magdalin, da Yowanna, da Maryamu uwar Yaƙub, da waɗansu da suke tare da su.
11 But it seemed like nonsense to them, so they didn't believe the women.
Amma ba su gaskata matan ba, domin sun ɗauki kalmominsu wani zancen banza ne.
12 However, Peter got up and ran to the tomb. Bending down, he looked in and saw only the linen grave-clothes. So he went back home, wondering what had happened.
Duk da haka, Bitrus ya tashi a guje zuwa kabarin. Da ya sunkuya, sai ya ga ƙyallayen lilin kaɗai a kwance. Sai ya koma yana tunani a ransa, a kan abin da ya faru.
13 The same day two disciples were on their way to a village called Emmaus, about seven miles from Jerusalem.
A wannan rana kuma, biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani ƙauye, da ake kira Emmawus, da suke kusan mil bakwai daga Urushalima.
14 They were talking about all that had happened.
Suna magana da juna a kan dukan abubuwan da suka faru.
15 As they discussed and debated, Jesus came up and fell into step with them.
Da suna magana, kuma suna tattauna waɗannan abubuwa da junansu, sai Yesu da kansa ya zo yana tafiya tare da su.
16 But they were kept from recognizing him.
Amma ba a ba su ikon gane shi ba.
17 “What are you discussing as you walk along?” he asked them. They stopped, their faces sad.
Sai ya tambaye, su ya ce, “Mene ne kuke tattaunawa da juna a cikin tafiyarku?” Suka tsaya shiru, da damuwa a fuskarsu.
18 One of them, called Cleopas, replied, “Are you just visiting Jerusalem? You must be the only person who doesn't know the things that have happened in the past few days.”
Ɗaya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya tambaye shi ya ce, “Ashe, kai baƙo ne a Urushalima, da ba ka san abubuwan da suka faru a can, a cikin kwanakin nan ba?”
19 “What things?” Jesus asked. “About Jesus of Nazareth,” they replied. “He was a prophet who spoke powerfully and performed great miracles before God and all the people.
Sai ya yi tambaya, “Waɗanne abubuwa?” Suka amsa suka ce, “Game da Yesu Banazare. Shi annabi ne, mai iko ne kuma cikin ayyukansa da maganarsa, a gaban Allah da kuma dukan mutane.
20 But our high priests and leaders handed him over to be condemned to death, and they crucified him.
Manyan firistoci da masu mulkinmu sun ba da shi a yi masa hukuncin mutuwa, suka kuwa gicciye shi.
21 We had hoped he was the one who was going to rescue Israel. It's been three days now since all this happened.
Amma da, muna sa zuciya cewa, shi ne wanda zai fanshi Isra’ila. Bugu da ƙari kuma yau kwana uku ke nan tun da wannan abin ya faru.
22 But then some of the women in our group surprised us.
Har wa yau, waɗansu daga cikin matanmu sun ba mu mamaki. Sun je kabarin da sassafen nan,
23 At dawn they went to the tomb and they didn't find his body. They came back saying that they'd seen a vision of angels who told them he's alive.
amma ba su sami jikinsa ba. Sun dawo sun faɗa mana cewa, sun ga wahayi na mala’iku, da suka ce yana da rai.
24 Some of us went to the tomb, and found it just as the women said—but they didn't see him.”
Sa’an nan, waɗansu abokanmu suka je kabarin, suka kuma tarar da kome kamar yadda matan suka faɗa, amma shi, ba su gan shi ba.”
25 Jesus told them, “You're so dull! How slow you are to trust in all that the prophets said!
Sai ya ce musu, “Ashe, ku marasa azanci ne, masu nauyin zuciyar gaskata, da dukan abin da annabawa suka faɗa!
26 Didn't the Messiah have to suffer before he could enter into his glory?”
Ai, dole Kiristi yă sha waɗannan wahalolin, kafin yă shiga ɗaukakarsa.
27 Then, starting with Moses and all the prophets, he explained to them everything that was said in Scripture about himself.
Sai ya fara bayyana musu daga Musa da dukan Annabawa, abin da dukan Nassi ya faɗa a kansa.”
28 As they approached the village they were going to, Jesus made it seem as if he was going farther.
Da suka yi kusa da ƙauyen da za su, sai Yesu ya yi kamar zai ci gaba.
29 But they urged him, saying, “Please come and stay with us. It's getting late—the day is almost over.” So he went to stay with them.
Amma suka matsa masa suka ce, “Sauka wurinmu, don dare ya kusa, rana ta kusa fāɗuwa.” Sai ya sauka wurinsu.
30 When he sat down to eat with them, he took the bread and gave thanks, broke it, and gave it to them.
Da ya zauna a tebur tare da su, sai ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya ya fara ba su.
31 Their eyes were opened, and they recognized him. Then he disappeared from view.
Sa’an nan idanunsu suka buɗe, suka gane shi. Sai ya ɓace musu.
32 The two disciples said to each other, “Weren't our thoughts on fire when he spoke to us, as he explained the Scriptures to us?”
Suka tambayi juna, “Ashe, shi ya sa zukatanmu suka kuna a cikinmu, sa’ad da yake magana da mu a hanya, yana bayyana mana Nassi.”
33 They got up right away and returned to Jerusalem. There they found the eleven disciples and those who were with them meeting together,
Suka tashi nan da nan suka koma Urushalima. A can suka sami Sha Ɗayan nan da waɗanda suke tare da su a wuri ɗaya,
34 who said, “The Lord has really risen again! He has appeared to Simon.”
suna cewa, “Gaskiya ne! Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman”
35 Then those who had just arrived explained to the other disciples what had happened to them on the road, and how they had recognized Jesus when he broke bread.
Sai su biyun nan suka ba da labarin abin da ya faru a hanya, da kuma yadda suka gane Yesu yayinda ya kakkarya burodin.
36 While they were talking, Jesus himself stood among them, and said, “Peace to you!”
Suna cikin wannan zance, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu. Sai ya ce musu, “Salama a gare ku!”
37 They were startled and afraid, thinking they were seeing a ghost.
Suka firgita, suka tsorota, suna tsammani fatalwa ce suka gani.
38 “Why are you frightened? Why are you doubting?” he asked them.
Sai ya ce musu, “Don me kuke damuwa, kuke kuma shakka a zuciyarku?
39 “Look at my hands and my feet—you can see it's me. Touch me and you'll be certain, for a spirit doesn't have flesh and bones, as you see I have.”
Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
40 Having said this, he showed them his hands and feet.
Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
41 But they still couldn't believe it because they were so elated and amazed. He asked them, “Do you have anything to eat?”
Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”
42 They gave him a piece of cooked fish,
Suka ba shi ɗan gasasshen kifi,
43 and he took it and ate it in front of them.
ya karɓa ya ci a gabansu.
44 Then Jesus said to them, “This is what I explained to you while I was still with you. Everything written about me in the law of Moses, the prophets, and the psalms, had to be fulfilled.”
Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da na gaya muku tun ina tare da ku cewa, dole a cika kome da aka rubuta game da ni, a cikin Dokar Musa, da Annabawa, da kuma Zabura.”
45 Then he opened their minds so they were able to understand the Scriptures.
Sai ya wayar da tunaninsu don su fahimci Nassi.
46 He told them, “It was written like this: the Messiah would suffer and rise from the dead on the third day, and in his name
Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da aka rubuta, cewa dole Kiristi yă sha wahala, a rana ta uku kuma yă tashi daga matattu.
47 repentance for the forgiveness of sins would be preached to all nations, beginning in Jerusalem.
Kuma a cikin sunansa za a yi wa’azin tuba da gafarar zunubai, ga dukan ƙasashe. Za a kuwa fara daga Urushalima.
48 You are witnesses of all this.
Ku ne shaidun waɗannan abubuwa.
49 Now I'm going to send you what my Father promised—but wait in the city until you receive power from heaven.”
Zan aika muku da abin da Ubana ya yi alkawari. Amma ku dakata a birnin tukuna, sai an rufe ku da iko daga sama.”
50 Then he led them out until they were near Bethany, and lifting up his hands, he blessed them.
Bayan ya kai su waje kusa da Betani, sai ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.
51 While he was blessing them, he left them, and was taken up to heaven.
Yana cikin sa musu albarka, sai ya rabu da su. Aka ɗauke shi zuwa cikin sama.
52 They worshiped him, and then they returned to Jerusalem full of joy.
Sai suka yi masa sujada, suka koma Urushalima cike da murna sosai.
53 They spent all their time in the Temple praising God.
Sai suka ci gaba da zama a cikin haikalin, suna yabon Allah.

< Luke 24 >