< Luke 21 >

1 Looking around, Jesus watched rich people putting their gifts into the collection box.
Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
2 He also saw a very poor widow put in two small coins.
Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
3 “I tell you the truth,” he said, “this poor widow has put in more than all the rest together.
Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
4 All of them gave from their wealth what they had, but she gave from her poverty all she had to live on.”
Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
5 Some of those there were talking about the Temple, its fine stonework and the beautiful gifts that had been donated. But Jesus said,
Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
6 “Regarding these things you're looking at… The time is coming when not one stone will be left on another; everything will be destroyed!”
“Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
7 “Teacher, when will this happen?” they asked him. “What will be the sign that these things are about to happen?”
Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
8 “Make sure you're not deceived,” Jesus warned them. “Many people will come claiming to be me, saying, ‘Here I am!’ and, ‘The time has come!’ but don't follow them.
Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
9 When you hear of wars and revolutions, don't be frightened, because these things have to happen first, but the end won't come immediately.
Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
10 Nation will fight nation, and kingdom will fight kingdom,” he told them.
Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
11 “There will be severe earthquakes, famines, and epidemic diseases in many lands, and extraordinary signs in the sky that are terrifying.
Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
12 But before all this, they will seize you and persecute you. They will drag you before synagogues and throw you into prison, and put you on trial before kings and governors on account of me.
Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
13 But this will provide you an opportunity to speak on my behalf before them.
Zai zamar maku zarafin shaida.
14 So make up your mind beforehand not to worry about how to defend yourselves,
Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
15 for I will give you words of wisdom that your enemies won't be able to dispute or contradict.
gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
16 You will be betrayed even by your parents, brothers, relatives, and friends, and they will kill some of you.
Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
17 Everyone will hate you because of me.
Kowa zai ki ku saboda sunana.
18 But not a single hair of your head will be lost.
Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
19 By standing firm you will gain your lives.
A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
20 However, when you see Jerusalem surrounded by armies, then you know that its destruction is near.
Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
21 Those who are in Judea should run away to the mountains, and those who are in Jerusalem should leave, and those who are the countryside shouldn't enter the city.
Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
22 For these are days of punishment, fulfilling all that's written.
Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
23 How hard it will be for those who are pregnant or nursing babies at that time! For terrible trouble is coming on the land and punishment against this people.
Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
24 They will be killed by the sword and taken away as prisoners to all the nations. Jerusalem will be trodden down by the foreign nations until their time is fulfilled.
Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
25 There will be signs in the sun, moon, and stars, and on the earth the nations will be in distress, confused by the sea's rolling and crashing.
Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
26 People will be faint from fear, terrified about what is happening to the world, for the powers of heaven will be shaken.
Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
27 Then they'll see the Son of man coming in a cloud with power and great glory.
Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
28 But when these things happen, stand up and look up, because you will soon be saved.”
Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
29 Then he told them this story as an illustration. “Look at the fig tree, or any other kind of tree.
Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
30 When you see new leaves appear, you don't need to be told that summer is near.
Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
31 In the same way, when you see these things happening, you don't need to be told that God's kingdom is near.
Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
32 I tell you the truth, this generation won't come to an end before all this happens.
Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
33 Heaven and earth will come to an end, but my word will not.
Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
34 Watch out that you don't become distracted by partying or getting drunk or by the worries of this life, so that this day catches you by surprise.
Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
35 For this day will come upon everyone who lives on the face of the earth.
kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
36 Always keep watch and pray, so that you may be able to escape all that will happen and stand before the Son of man.”
Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
37 Every day Jesus taught in the Temple, and every evening he went and stayed on the Mount of Olives.
Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
38 All the people came early in the morning to listen to him in the Temple.
Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.

< Luke 21 >