< Leviticus 9 >

1 On the eighth day after the ordination Moses called Aaron and his sons, and the elders of Israel, to meet with him.
A rana ta takwas, Musa ya kira Haruna da’ya’yansa maza da kuma dattawan Isra’ila.
2 He told Aaron, “You need to bring a young bull as a sin offering and a ram as a burnt offering, both without defects, and present them before the Lord.
Ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki ɗan maraƙi domin hadayarka don zunubi da kuma ɗan rago domin hadaya ta ƙonawa, dukan biyu su kasance marar lahani, ka miƙa su a gaban Ubangiji.
3 Then tell the Israelites, ‘Bring the following offerings: a male goat as a sin offering; a calf and a lamb, (both a year old and without defects), for a burnt offering;
Sa’an nan ka ce wa Isra’ilawa, ‘Ku ɗauki bunsuru na yin hadaya don zunubi, da ɗan maraƙi bana ɗaya, da ɗan rago bana ɗaya marasa lahani, don hadaya ta ƙonawa,
4 a bull and a ram as a peace offering to sacrifice before the Lord; and a grain offering mixed with olive oil. Do this because today the Lord is going to reveal himself to you today.’”
da bijimi da rago don hadayun salama, a yi hadaya da su ga Ubangiji, da hadaya ta gari da aka kwaɓa da mai, gama yau Ubangiji zai bayyana a gare ku.’”
5 Following Moses' orders they brought what he'd said to the front of the Tent of Meeting. Everyone came and stood before the Lord.
Suka ɗauki abubuwan da Musa ya umarta zuwa gaban Tentin Sujada, sai dukan jama’a suka zo kusa suka tsaya a gaban Ubangiji.
6 Moses said, “This is what the Lord ordered me to tell you to do, so that you may see his glory.”
Sa’an nan Musa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya umarce ku ku yi, domin ɗaukakar Ubangiji za tă bayyana gare ku.”
7 Then Moses told Aaron, “Go to the altar and sacrifice your sin offering and your burnt offering to make you and the people right. Then sacrifice the offerings brought by the people as a means to make them right, as the Lord ordered.”
Musa ya ce wa Haruna, “Matsa kusa da bagaden, ka miƙa hadayarka don zunubi, da hadayarka ta ƙonawa, ka yi kafara don kanka da kuma don jama’a. Ka kuma kawo hadayar jama’a, ka yi kafara dominsu kamar yadda Ubangiji ya umarta.”
8 So Aaron went to the altar and killed the calf as a sin offering for himself.
Sai Haruna ya matsa kusa da bagaden, ya yanka ɗan maraƙi na yin hadaya don zunubi saboda kansa.
9 His sons brought the blood to him. He dipped his finger in the blood and put it on the horns of the altar. He poured out the rest of the blood at the bottom of the altar.
’Ya’yan Haruna maza suka kawo masa jinin, ya kuma tsoma yatsarsa a cikin jinin ya zuba cikin ƙahonin bagade; sauran jinin kuwa ya zuba a gindin bagaden.
10 He burned the fat, the kidneys, and the best part of the liver from the sin offering on the altar, as the Lord had ordered Moses to do.
A kan bagaden, ya ƙone kitsen, ƙodojin, da abin da ya rufe hanta, daga hadaya don zunubi, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
11 However, he burned up the meat and the skin outside the camp.
Naman da fatar kuwa ya ƙone waje da sansanin.
12 Aaron killed the burnt offering. His sons brought him the blood, and he sprinkled it on the sides of the altar.
Sa’an nan ya yanka hadaya ta ƙonawa.’Ya’yan Haruna maza suka miƙa masa jinin, ya kuwa yayyafa shi a kowane gefe na bagaden.
13 They brought him the head and all the other pieces of the burnt offering, and he burned them on the altar.
Suka miƙa masa hadaya ta ƙonawa gunduwa-gunduwa, haɗe da kan, ya kuwa ƙone su a bisa bagaden.
14 He washed the insides and the legs and burned them with the rest of the burnt offering on the altar.
Sai ya wanke kayan ciki da ƙafafun, ya kuwa ƙone su tare da hadaya ta ƙonawa a kan bagade.
15 Then Aaron presented the offerings of the people. He killed the male goat as the sin offering for the people, and offered it in the same way as his own sin offering.
Sa’an nan Haruna ya kawo hadayar da take domin mutane. Ya ɗauki akuya ta hadaya don zunubin mutane, ya yanka shi, ya miƙa shi domin hadaya don zunubi kamar yadda ya yi da na farko.
16 He presented the burnt offering, doing so in accordance with the regulations.
Ya kawo hadaya ta ƙonawa ya kuma miƙa ta yadda aka tsara.
17 He presented the grain offering. He took a handful from it and burned it on the altar, in addition to the burnt offering presented earlier that morning.
Ya kuma kawo hadaya ta gari, ya ɗiba a tafi hannu ya ƙone a kan bagade tare da hadaya ta ƙonawa ta safe.
18 Aaron killed the bull and the ram as the peace offering for the people. His sons brought him the blood, and he sprinkled it on the sides of the altar.
Haruna ya yanka maraƙin da ragon a matsayin hadaya ta salama domin mutane.’Ya’yansa maza suka miƙa masa jinin, ya kuwa yayyafa shi a kowane gefe na bagade.
19 They also brought him the fat portions from the bull, and from the ram—the fat tail, the fat covering the insides, the kidneys, and the best part of the liver—
Amma sashen kitsen maraƙin da na ragon, da wutsiya mai kitse, da kitsen da yake rufe da kayan ciki, da ƙodoji da kuma kitsen da ya rufe hanta,
20 and put them on the breasts. Aaron burned the fat portions on the altar,
suka shimfiɗa waɗannan a kan ƙirjin, sa’an nan Haruna ya ƙone kitsen a kan bagade.
21 but he waved the breasts and the right thigh as a wave offering before the Lord, as Moses had ordered him to do.
Sai Haruna ya kaɗa ƙirjin da kuma cinyar dama a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa, kamar yadda Musa ya umarta.
22 Then Aaron held up his hands towards the people and blessed them. After that he came down from the altar, having completed the sin offering, the burnt offering, and the peace offering.
Sa’an nan Haruna ya ɗaga hannuwansa wajen mutane ya sa musu albarka. Da yake ya miƙa hadaya don zunubi, hadaya ta ƙonawa da kuma hadaya ta salama, sai ya sauka.
23 Moses and Aaron went into the Tent of Meeting. When they came out, they blessed the people, and the glory of the Lord was revealed to everyone.
Sai Musa da Haruna suka shiga cikin Tentin Sujada. Da suka fita, sai suka sa wa mutane albarka; sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan mutane.
24 Fire came from the presence of the Lord and burned up the burnt offering and the fat portions on the altar. When everyone saw this, they shouted for joy and fell down with their faces to the ground.
Sai wuta ta fito daga gaban Ubangiji ta cinye hadaya ta ƙonawa da sassan kitsen a kan bagaden. Sa’ad da dukan mutane suka ga haka, sai suka yi ihu suna farin ciki, suka fāɗi rubda ciki, suka yi sujada.

< Leviticus 9 >