< Job 25 >

1 Then Bildad the Shuhite spoke up and said,
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 “Dominion and awe belong to God. He brings peace to his heavens.
“Mulki na Allah ne, dole a ji tsoronsa; yana tafiyar da kome yadda ya kamata a cikin sama.
3 Who can count his armies? Is there anywhere his light doesn't shine?
Za a iya ƙirga rundunarsa? A kan wane ne ba ya haska haskensa?
4 How can a human being be right before God? Can anyone born of woman be pure?
Ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah? Ta yaya mutumin da mace ta haifa zai zama mai tsarki?
5 If in God's eyes even the moon does not shine brightly, and the stars are not pure,
In har wata da taurari ba su da tsarki a idanunsa,
6 how much less a human being—who by comparison is like a maggot or a worm!”
mutum fa? Ai, wannan tsutsa ne, ɗan ƙwaro kawai. Me mutum ya daɗa a gaban Allah!”

< Job 25 >