< Jeremiah 32 >

1 This is the Lord's message that came to Jeremiah in the tenth year of Zedekiah king of Judah's reign, which was the eighteenth year of Nebuchadnezzar's reign.
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji a shekara ta goma ta Zedekiya sarkin Yahuda, wanda ya kasance shekara ta goma sha takwas ta Nebukadnezzar.
2 This was when the army of the king of Babylon was besieging Jerusalem. Jeremiah the prophet was imprisoned in the guard's courtyard, part of the king of Judah's palace.
Sojojin sarkin Babilon a lokacin suna ƙawanya wa Urushalima annabi Irmiya kuwa yana a tsare a sansanin matsara a fadar Yahuda.
3 Zedekiah king of Judah had put him in prison, telling him: “Why do you have to prophesy like this? You say the Lord is saying, ‘Look, I'm going to hand over this city to the king of Babylon, and he will capture it.
Zedekiya sarkin Yahuda fa ya sa shi a kurkuku yana cewa, “Don me kake yin annabci? Ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa cinye ta.
4 Zedekiah king of Judah won't escape from the Babylonians. He will be captured and taken to the king of Babylon to speak with him personally and see him face to face.
Zedekiya sarkin Yahuda ba zai kuɓuta daga hannuwan Babiloniyawa ba amma tabbatacce za a ba da shi ga sarkin Babilon, zai kuwa yi masa magana fuska da fuska ya kuma gan shi da idanunsa.
5 He will take Zedekiah to Babylon, where he'll remain until I deal with him, declares the Lord. You won't be successful if you fight against the Babylonians.’”
Zai kai Zedekiya Babilon, inda zai zauna har sai ya magance shi, in ji Ubangiji. In ka yi yaƙi da Babiloniyawa, ba za ka yi nasara ba.’”
6 Jeremiah answered, “The Lord gave me a message, saying:
Irmiya ya ce, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
7 Your cousin Hanamel, son of Shallum, is coming to tell you, ‘Why don't you buy my field in Anathoth because you have the right to redeem it and buy it?’
Hananel ɗan Shallum ɗan’uwan mahaifinka zai zo wurinka ya ce, ‘Saya filina a Anatot, domin a matsayinka na dangi na kurkusa hakkinka ne kuma kai ya wajaba ka saye shi.’
8 Just as the Lord had said, my cousin Hanamel arrived to see me in the guard's courtyard and asked me, ‘Please buy my field in Anathoth in the land of Benjamin because you have the right of family ownership to redeem it. You should buy it for yourself.’” This convinced me that this was a message from the Lord.
“Sa’an nan, kamar dai yadda Ubangiji ya faɗa, sai ga Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina ya zo wurina a sansanin matsara ya ce, ‘Saya filina a Anatot a yankin Benyamin. Da yake hakkinka ne ka fanshe shi ka kuma mallake shi, ka sayo shi wa kanka.’ “Sai na gane cewa wannan maganar Ubangiji ce;
9 So I bought the field in Anathoth from my cousin Hanamel. I weighed out seventeen shekels of silver to pay him.
saboda haka sai na saye filin a Anatot daga hannun Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina na kuma auna masa shekel goma sha bakwai na azurfa.
10 I signed the deed and sealed it, had it witnessed, and weighed out the silver using the scales.
Na sa hannu a takarda, na buga hatimi na liƙe, na sami shaidu na kuwa auna shekel a ma’auni.
11 Then I took the deed of sale, both the sealed original containing the terms and conditions, and the unsealed copy,
Na ɗauki takardar ciniki, takardar da aka rubuta sharuɗan a ciki, da kuma takardar da ba a liƙe ba,
12 and handed them to Baruch son of Neriah, son of Mahseiah. I did this in the presence of my cousin Hanamel, the witnesses who had signed the deed of sale, and all the people of Judah who were sitting there in the guard's courtyard.
na kuma ba wa Baruk ɗan Neriya, ɗan Masehiya, wannan takarda a gaban Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina da kuma a gaban shaidun da suka sa hannu a takardan ciniki da kuma a gaban dukan Yahudawan da suke zaune a sansanin matsaran.
13 I gave Baruch these instructions in front of them,
“A gabansu na yi wa Baruk waɗannan umarnai cewa,
14 “This is what the Lord Almighty, the God of Israel, says: Put these deeds of sale, the sealed original and the open copy, in a clay jar so they can be kept safe for a long time.
‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka ɗauki waɗannan takardun ciniki, wanda aka liƙe da wanda ba a liƙe ba, ka sa su a cikin tulun yumɓu don kada su lalace.
15 For this is what the Lord Almighty, the God of Israel, says: The time will come when once again houses, fields, and vineyards will be bought in this country.”
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa za a sāke saye gidaje, filaye da gonakin inabi a wannan ƙasa.’
16 After I had given the deed of sale to Baruch son of Neriah, I prayed to the Lord:
“Bayan na ba da takardun ciniki ga Baruk ɗan Neriya, sai na yi addu’a ga Ubangiji na ce,
17 “Ah, Lord God! You created the heavens and the earth by your great strength and power. Nothing is too hard for you!
“A, Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi sammai da duniya ta wurin ikonka mai girma da kuma hannunka mai iko. Ba abin da ya gagare ka.
18 You give your trustworthy love to thousands, but you punish the sins of the fathers the consequences affect their children too., Great and powerful God whose name is the Lord Almighty,
Kakan nuna ƙauna ga dubbai amma kakan hukunta’ya’ya saboda laifin ubanninsu a bayansu. Ya mai girma da kuma Allah mai iko, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki,
19 you are the one who is supremely wise and who does incredible things. You watch what everyone does, and you reward them according to the way they live and what their actions deserve.
manufofinka da girma suke, ayyukanka kuma masu girma ne. Idanunka suna a buɗe ga dukan hanyoyin mutane; kakan sāka wa kowa gwargwadon halinsa yadda ya dace.
20 You carried out signs and miracles in Egypt, and you still do so today, both here in Israel and among all people everywhere. As a result you gained a great reputation, and this is still true today.
Ka aikata ayyukan banmamaki da kuma al’ajabai a Masar ka kuma ci gaba da su har yă zuwa yau, a Isra’ila da kuma a cikin dukan’yan adam, ka kuma sami sunan da har yanzu yake naka.
21 You led your people Israel out of Egypt with signs and miracles, with your great power and strength that terrified people.
Ka fitar da mutanenka Isra’ila daga Masar da alamu da abubuwa banmamaki, ta wurin hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi tare da banrazana mai girma.
22 You gave them this land that you had promised to give their forefathers, a land flowing with milk and honey.
Ka ba su wannan ƙasa da ka rantse za ka ba wa kakanni kakanninsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
23 They came and took it over, but they didn't do what you said or follow your laws. They didn't do everything you ordered them to do, which is why you've brought all this disaster down on them.
Suka shiga suka mallake ta, amma ba su yi maka biyayya ba, ba su kuma bi dokarka ba; ba su yi abin da ka umarce su ba. Saboda haka ka kawo masifa a kansu.
24 Look at the siege ramps piled up against the city to capture it! Through war and famine and disease, the city will be taken by the Babylonians who are attacking it. You can see that everything you said would happen has happened.
“Duba yadda aka gina mahaurai don a kame birni. Saboda takobi, yunwa da annoba, za a ba da birnin ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye shi da yaƙi. Abin da ka faɗa ya faru, yadda kake gani yanzu.
25 Yet, Lord God, you have told me, ‘Buy yourself the field with silver in front of witnesses, even though the city has been handed over to the Babylonians!’”
Ko da yake za a ba da birnin ga Babiloniyawa, kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka ce mini, ‘Saye fili da azurfa ka kuma sa a shaida cinikin.’”
26 Then Lord gave Jeremiah this message:
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
27 Look! I am the Lord, the God of everyone. Is anything too hard for me to do?
“Ni ne Ubangiji Allah na dukan’yan adam. Akwai wani abin da ya gagare ni?
28 So this is what the Lord says: Listen! I'm going to hand over this city to the king of Babylon and the Babylonians, and they will capture it.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga Babiloniyawa da kuma ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, wanda zai yaƙe ta.
29 The Babylonians who are attacking the city are going to come and set fire to it. They will burn it down, including the houses belonging to the people who made me angry by burning incense to Baal on their rooftops, and by pouring out drink offerings in worship of other gods.
Babiloniyawan da suke yaƙi da wannan birni za su zo ciki su cinna masa wuta; tare da gidaje inda mutane suka tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙona turare a rufin ɗakuna wa Ba’al suka zub da hadayun sha wa waɗansu alloli.
30 From their earliest days all the people of Israel and of Judah have ever done has been evil in my sight. In fact all they've even done is to make me angry through their actions, declares the Lord.
“Mutanen Isra’ila da na Yahuda ba abin da suka yi sai mugunta a gabana daga ƙuruciyarsu; tabbatacce, mutanen Isra’ila ba su yi kome ba sai dai tsokane ni da abin da hannuwansu suka yi, in ji Ubangiji.
31 This city has been such a source of anger and frustration from the time it was built right up till now. So I'm going to get rid of it,
Daga ranar da aka gina ta har zuwa yanzu, wannan birni ta tā da fushina da hasalata da dole a kawar da ita daga gabana.
32 because of all the evil things the people of Israel and Judah did that made me angry—their kings, and officials, their priests and prophets, all of those living in Judah and Jerusalem, everyone
Mutanen Isra’ila da na Yahuda sun tsokane ni ta wurin dukan muguntar da suka aikata su, sarakunansu da fadawansu, firistocinsu da annabawa, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima.
33 They have turned their backs on me. They wouldn't even look at me. Even though I kept on trying to teach them, they refused to listen or accept instruction.
Sun juya mini bayansu ba fuskokinsu ba; ko da yake na koyar da su sau da sau, ba su saurara ko bi horo na ba.
34 They have put their disgusting idols in my Temple, making it unclean.
Sun kafa gumakansu na banƙyama a cikin haikalina wanda ake kira da sunana, sun kuwa ƙazantar da shi.
35 They have built pagan shrines to Baal in the Valley of Hinnom so they could sacrifice their sons and daughters by burning them in the fire. This is something I never commanded. I never even thought of such a thing—doing something so awful and making the people of Judah guilty of sin.
Sun gina masujadai kan tudu wa Ba’al a Kwarin Ben Hinnom don su miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ga Molek, ko da yake ban taɓa umarce su ba, bai kuma zo mini cewa su yi abin banƙyama irin wannan ba ta haka suka sa Yahuda ya yi zunubi.
36 Now about this city. You are correctly saying, “It's going be handed over to the king of Babylon through war and famine and disease.” However, this is what the Lord, the God of Israel, says:
“Kana cewa game da wannan birni, ‘Ta wurin takobi, yunwa da annoba za a ba da shi ga sarkin Babilon’; amma ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa
37 I promise to gather my people from all the lands where I exiled them because they made me so very angry. I will bring them back here and they will live in safety.
tabbatacce zan tattara su daga dukan ƙasashen da na kore su zuwa cikin fushina da hasalata mai girma; zan komo da su wurin nan in sa su zauna lafiya.
38 They will be my people, and I will be their God.
Za su zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnsu.
39 I will make sure they think the same way and act in harmony, so that they will always honor me so all will be good for them and their descendants.
Zan ba su zuciya ɗaya da aiki ɗaya, don kullum su ji tsorona domin amfaninsu da kuma amfanin’ya’yansu a bayansu.
40 I will make an everlasting agreement with them: I'm never going to stop doing them good and I will help them to respect me so that they won't ever abandon me.
Zan yi madawwamin alkawari da su. Ba zan taɓa barin aikata musu alheri ba, zan kuma iza su su ji tsorona, don kada su ƙara juya daga gare ni.
41 I will be delighted to treat them well, and I will commit myself with the whole of my being to helping them to grow as a nation in this land.
Zan yi farin ciki a yin musu alheri, tabbatacce zan su dasa a wannan ƙasa da dukan zuciyata da dukan raina.
42 This is what the Lord says: Just as certainly as I have brought this whole disaster down on my people, so I'm going to give to them all the good things I have promised.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, yadda na kawo dukan wannan masifa a kan wannan mutane, haka zan ba su wadatar da na yi musu alkawari.
43 Fields will once again be bought in this country that you're describing, saying, “It's been completely destroyed—no people or animals are left. It's been handed over to the Babylonians.”
Za a sāke sayi filaye a wannan ƙasa da kuka ce, ‘Kango ce, ba mutane ko dabbobi, gama an ba da ita ga Babiloniyawa.’
44 People will buy fields with silver again, deeds will be signed, sealed, and witnessed. This will happen here in the land of Benjamin, in the areas surrounding Jerusalem, and in all the towns of Judah—including the towns of the hill country, the foothills, and the Negev—because I will bring the people back from exile, declares the Lord.
Za a sayi filaye da azurfa, a kuma sa hannu a takardan ciniki, a liƙe a kuma shaida a yankin Benyamin, a ƙauyukan kewayen Urushalima, a garuruwan Yahuda da kuma a garuruwan ƙasar tudu, na yammancin gindin dutse da na Negeb, domin zan maido da wadatarsu, in ji Ubangiji.”

< Jeremiah 32 >