< Isaiah 40 >

1 “Comfort, yes comfort my people!” says your God.
Ta’aziyya, ku ta’azantu mutanena, in ji Allahnku.
2 “Speak lovingly to the people of Jerusalem, telling them that their hard times are over, that their sins have been forgiven, and that the Lord has paid them twice over for their sins.”
Yi magana mai kwantar da rai ga Urushalima, ku kuma furta mata cewa aiki mai zafinta ya isa, cewa an fanshi zunubinta, cewa ta karɓi daga hannun Ubangiji ninki biyu saboda dukan zunubanta.
3 A voice is heard calling, “Prepare the way for the Lord in the wilderness, make a straight highway for our God through the desert.
Muryar wani tana kira cewa, “A cikin hamada ku shirya hanya saboda Ubangiji; ku miƙe manyan hanyoyi domin Allahnmu a cikin jeji.
4 Fill in all the valleys; level all the mountains and hills; smooth out the uneven ground; make the rough places flat.
Za a cike kowane kwari, a baje kowane dutse da kowane tudu; za a mayar da karkatattun wurare su zama sumul, munanan wurare kuma su zama da kyau.
5 The Lord's glory will be revealed, and everyone will see it together. This is what the Lord has declared.”
Za a kuma bayyana ɗaukakar Ubangiji, dukan mutane kuwa za su gan ta. Gama Ubangiji da kansa ne ya yi magana.”
6 A voice is heard saying, “Shout it out.” I asked, “What shall I shout?” “All human beings are like grass, and all their trustworthiness is like the flowers of the field.
Muryar tana cewa, “Ka yi shela.” Na kuwa ce, “Me zan yi shelar?” “Dukan mutane kamar ciyawa suke, kuma dukan ɗaukakarsu kamar furannin jeji ne.
7 The grass wilts and the flower fades when the Lord's breathes on them. Yes, the people are grass!
Ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, domin Ubangiji ya hura iska a kansu. Tabbatacce mutane ciyawa ne.
8 However, even though the grass wilts and the flower fades, the word of our God will endure forever.”
Hakika ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, amma maganar Allahnmu tana nan daram har abada.”
9 Zion, bringer of good news, go up a high mountain. Jerusalem, bringer of good news, raise your voice and shout out loud. Don't be afraid to shout really loud! Tell the towns of Judah, “Here is your God!”
Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Sihiyona, ka haura a bisa dutse. Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Urushalima, ka tā da muryarka ka yi ihu, ka ɗaga ta, kada ka ji tsoro; faɗa wa garuruwan Yahuda, “Ga Allahnku!”
10 Look! The Lord God is coming with power! He will rule with a firm hand. Look! He's bringing his reward with him, coming to give his gift.
Duba, Ubangiji Mai Iko Duka yana zuwa da iko, hannunsa kuma yana yin mulki dominsa. Duba, ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa kuma na rakiyarsa.
11 He looks after his flock like a shepherd. He picks up the lambs in his arms and holds them close to his chest. He leads those that are nursing young.
Yakan lura da garkensa kamar makiyayi. Yakan tattara tumaki wuri ɗaya yă riƙe su kurkusa da ƙirjinsa; a hankali kuma yakan bi da masu ba da mama.
12 Who has measured the waters he holds in the palm of his hand? Who has marked off the heavens with the span of his hand? Who has worked out the amount of dust of the earth? Who has weighed the mountains on a scale and the hills with a balance?
Wane ne ya auna ruwaye a tafin hannunsa, ko kuwa ya gwada tsawon sammai da fāɗin tafin hannunsa? Wane ne ya riƙe ƙurar ƙasa a kwando, ko kuwa ya auna nauyin duwatsu a magwaji, tuddai kuma a ma’auni?
13 Who has measured the Spirit of the Lord, or taught him what to do as his counselor?
Wane ne ya fahimci zuciyarUbangiji, ko kuwa ya koya masa a matsayin mashawarcinsa?
14 Who did the Lord go to for advice to help him understand? Who taught him right from wrong? Who gave him knowledge and showed him the way of wisdom?
Wane ne Ubangiji ya nemi shawararsa don yă ganar da shi, wane ne kuma ya koya masa hanyar da ta dace? Wane ne ya koya masa sani ko ya nuna masa hanyar fahimta?
15 It's obvious that the nations are just a drop in a bucket. They're like dust on a set of scales. He can pick up islands as if they weigh next to nothing.
Tabbatacce al’ummai suna kama da ɗigon ruwa a cikin bokiti an ɗauke su a matsayin ƙura a kan magwaji; yakan auna tsibirai sai ka ce ƙura mai laushi.
16 All the wood in Lebanon for a fire and all its animals as a sacrifice wouldn't be enough a burnt offering.
Itatuwan Lebanon ba su isa a yi wutar bagade da su ba, balle dabbobinsa su isa yin hadayun ƙonawa.
17 To him all the nations are like nothing. He counts them as less than nothing—like they don't exist.
A gabansa dukan al’ummai ba kome ba ne; ya ɗauke su ba a bakin kome ba kuma banza ne kurum.
18 Who do you think is like God? What image do you think he looks like?
To, ga wane ne za ka kwatanta Allah? Wace siffa za ka kwatanta shi da ita?
19 Is he a metal idol that a craftsman casts in a mold, and then a goldsmith overlays it with gold and makes silver chains for it?
Gunki dai, maƙeri kan yi zubinsa, maƙerin zinariya kuma yă ƙera shi da zinariya yă kuma sarrafa masa sarƙoƙin azurfa.
20 Those who are too poor to pay for that choose wood that won't rot, then they look for a skilled wood-carver to make an idol that won't fall over.
Mutumin da talauci ya sha kansa da ba zai iya miƙa irin hadayar nan ba kan zaɓi itacen da ba zai ruɓe ba. Yakan nemi gwanin sassaƙa don yă sassaƙa masa gunkin da ba zai fāɗi ba.
21 Don't you know? Haven't you heard? Hasn't it been explained to you from the very beginning? Haven't you understood from the time the world was created?
Ba ku sani ba? Ba ku taɓa ji ba? Ba a faɗa muku daga farko ba? Ba ku fahimta ba tun kafawar duniya?
22 God sits on his throne above the horizon of the earth; the people that live there are like grasshoppers. He stretches out the heavens like a curtain, spreading them out like a tent to live in.
Yana zaune a kursiyi a bisa iyakar duniya, kuma mutanenta suna kama da fāra. Ya miƙa sammai kamar rumfa, ya kuma shimfiɗa su kamar tentin da za a zauna a ciki.
23 He brings leaders down; he makes the rulers of the world like nothing.
Yakan mai da sarakuna ba kome ba yă mai da masu mulkin wannan duniya wofi.
24 In fact they are hardly even planted, hardly even sown, hardly even taken root, when he blows on them and they wither, and the wind carries them away like straw.
Ba da jimawa ba bayan an shuka su, ba da jimawa ba bayan an dasa su, ba da jimawa ba bayan sun yi saiwa a ƙasa, sai yă hura musu iska su yanƙwane, guguwa kuma ta kwashe su kamar yayi.
25 “Who are you going to compare me with? Who is equal to me?” asks the Holy One.
“Ga wa za ku kwatanta ni? Ko kuwa wa yake daidai da ni?” In ji Mai Tsarkin nan.
26 Look at the heavens. Who created all this? He leads the stars like an army, and calls each one by name. Because he has great power and incredible strength, not a single one of them is missing.
Ku ɗaga idanunku ku duba sammai. Wane ne ya halicce dukan waɗannan? Wane ne ya fitar da rundunar taurari ɗaya-ɗaya, yana kiransu, kowanne da sunansa. Saboda ikonsa mai girma da kuma ƙarfinsa mai girma, babu ko ɗayansu da ya ɓace.
27 Why do you speak like this, Jacob, and why do you say, Israel, “The Lord doesn't see what's happening to me, and he's ignoring my rights!”
Ya Yaƙub, ya Isra’ila, me ya sa kake ce kana kuma gunaguni cewa, “Hanyata tana a ɓoye daga Ubangiji; Allah bai kula da abin da yake damuna ba”?
28 Don't you know? Haven't you heard? The Lord is the eternal God, the Creator of the whole earth. He's never weak or tired; you can't find out all he knows.
Ba ku sani ba? Ba ku ji ba? Ubangiji madawwamin Allah ne, Mahaliccin iyakokin duniya. Ba zai taɓa gaji ko yă kasala ba, kuma fahimtarsa ya wuce gaban ganewar mutum.
29 He gives strength to the weary and power the powerless.
Yakan ba da ƙarfi ga waɗanda suka gaji yă kuma ƙara ƙarfi ga marasa ƙarfi.
30 Even young people grow weak and tired—they fall down when they're exhausted.
Ko matasa ma kan gaji su kuma kasala, samari kuma kan yi tuntuɓe su fāɗi;
31 But those who trust in the Lord will have their strength renewed. They will fly high with wings like eagles. They will run and not be tired. They will walk and not be worn out.
amma waɗanda suka dogara ga Ubangiji za su sabunta ƙarfinsu. Za su yi firiya da fikafikai kamar gaggafa; za su kuma yi gudu ba kuwa za su gaji ba, za su yi tafiya ba kuwa za su kasala ba.

< Isaiah 40 >